An daƙile yunƙurin juyin mulki a Burkina Faso
Published: 23rd, April 2025 GMT
Gwamnatin mulkin soji a Burkina Faso ta ce hukumomi leƙen asiri sun daƙile wani yunƙurin kifar da gwamnatin a cikin watan Afrilu.
Ta ce an aka kitsa juyin mulkin ne domin haifar da ruɗani a kasar ta yammacin Afirka.
Gwamnatin ta ce an gano waɗanda suka shirya juyin mulkin daga makwabciyarta Ivory Coast.
Shugaban gwamnatin rikon kwarya Ibrahim Traore Kaptin ɗin soja wanda shi kansa ya hau shugabanci ne ta hanyar juyin mulki a 2022 ya sha zargin ƙasar Ivory Coast da bai wa masu adawa da shi mafaka.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ivory Coast
এছাড়াও পড়ুন:
Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Aike Da Sako Ga Al’ummar Iran Bayan Harin Da Iran Ta Fuskanta
Jagoran juyin juya halin Musulunci ya aike da sako ga al’ummar Iran bayan harin da yahudawan sahayoniyya suka kai kan kasar
A yammacin jiya ne Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya gabatar da sakon ta gidan talabijin ga al’ummar Iran bayan harin ta’addanci na baya-bayan nan da yahudawan sahayoniyya suka kaddamar kan kasar Iran.
Jagoran juyin juya halin Musuluncin ya bayyana a cikin wani sakon da ya aike ta gidan talabijin ga al’ummar Iran cewa: Sojojin Iran za su yi aiki da dukkanin karfinsu, kuma za su mayar da martani kan wannan mugunyar aniya ta ‘yan sahayoniyya kaskantattu marasa tunani da basira.
Jagoran ya jaddada cewa: Yahudawan sahayoniyya ba za su fita cikin wannan aika-aika ba, kuma wajibi ne al’ummar Iran su tabbatar da cewa ba za a yi sassauci ko sakaci kan hakan ba.