Leadership News Hausa:
2025-08-14@12:35:42 GMT

Gwamna Sule Ya Ziyarci Gidan Yarin Keffi Bayan Tserewar Fursunoni 16

Published: 14th, August 2025 GMT

Gwamna Sule Ya Ziyarci Gidan Yarin Keffi Bayan Tserewar Fursunoni 16

Gwamnan ya yi alƙawarin cewa gwamnatin jihar za ta yi aiki tare da hukumomi masu ruwa da tsaki domin hanzarta shari’o’i da kuma rage cunkoson gidan yarin.

A lokacin ziyarar, ya lura da cewa yawancin fursunonin na zaune a ƙasa babu katifa.

Don inganta rayuwarsu, ya umarci a samar musu da katifu 500.

Gwamna Sule ya yaba wa jami’an gidan yari da sauran jami’an tsaro saboda sake kama wasu daga cikin waɗanda suka tsere.

Ya kuma roƙi jama’a da su kasance cikin shiri su kuma sanar da hukumomin tsaro idan sun ga wani mai kama da wanda ake nema.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Gwamna Sule Nasarawa

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda sun kama matashi kan zargin aikata fashi a Gombe

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, ta kama wani matashi mai shekara 18 bisa zargin aikata fashi da makami a jihar.

An kama shi ne a garin Kwadon bayan samun sahihin bayani daga jama’a.

NDLEA ta lalata gonar tabar wiwi a Gombe ’Yan ci-rani 26 sun nitse a teku suna ƙoƙarin tsallakawa Turai

Kakakin ’yan sandan jihar, DSP Buhari Abdullahi, ya ce an kama matashin ne ranar 9 ga watan Agusta, 2025 da misalin ƙarfe 2:30 na rana.

Hakazalika, ya ce an samu ƙunshi ganyen da ake zargin tabar wiwi ne.

Bincike ya nuna cewa matashin na cikin mutanen da ’yan sanda ke nema game da aikata fashi da makami, waɗanda ake shari’arsu a babbar kotun jihar.

A cewar DSP Abdullahi, matashin ya amsa cewa yana daga cikin waɗanda suka kai hare-haren.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, CP Bello Yahaya, ya umsrci a miƙa shi zuwa sashen binciken manyan laifuka domin zurfafa bincike kafin gurfanar da shi a kotu.

Rundunar ta yi kira ga jama’a da su ci gaba da ba ta bayanai da za su taimaka wajen yaƙar laifuka a jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kama Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Karkatar Da Dukiyar Gwamnati
  • ’Yan sanda sun kama matashi kan zargin aikata fashi a Gombe
  • Iraki Tace: Ita Yentacciyar Kasashe Ce Bayan da Amurka Ta Yi Korafi Kan Yarjeniyar tsaro da Iran
  • Gwamna Bago Ya Yabawa Tinubu Kan Kama Shugaban Kungiyar Ta’addanci A Neja
  • Fursunoni 16 sun tsere daga gidan yarin Keffi
  • Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo
  • An kama ɗan shekara 18 kan zargin fashi da makami a Gombe
  • Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro
  • An kama mutumin da ake zargi da kashe jami’in sibil difens a Jigawa