Aminiya:
2025-08-14@22:17:04 GMT

Mun shirya wa zaben ciki gurbi a Kano —INEC

Published: 15th, August 2025 GMT

Hukumar Zabe ta Kasa INEC ta sanar da kammala duk shirye-shiryen zaben ciki gurbi a kananan hukumomin Bagwai, Shanono da kuma Ghari (Kunchi) da ke Kano wanda za a gudanar a ranar Asabar.

Kwamishinan INEC a Kano, Zango Abdu, wanda ya tabbatar da hakan a yayin taron manema labarai, ya ce an riga an raba kayan zabe masu muhimmanci da wadanda ba su da muhimmanci a kananan hukumomi da abin ya shafa.

Tinubu ya cancanci yabo kan daidaita tattalin arzikin Nijeriya —Ngozi An kama Mai Unguwa kan yi wa yarinya fyaɗe a Gombe

Ya ce, “Tun kusan makonni uku da suka gabata aka riga da tura kayayyakin da ba su da muhimmanci wadanda aka tanadar wa mazabu da rumfunan zabe.

“Yanzu haka kayan zaben masu muhimmanci sun iso, kuma za a tura su kananan hukumomi yau da yamma tare da wakilan jam’iyyun siyasa da jami’an tsaro.”

Ya kuma bayyana cewa an kammala horas da dukkan ma’aikatan wucin gadi kuma an tura su wuraren da za su yi aikin, yayin da jami’an tsaro karkashin kwamitin tsaro na haɗin gwiwa sun ba da tabbacin duk wasu tanade-tanade da suka kamata.

Da yake karin haske, Zango ya ce duk na’urorin BVAS wadanda za a yi amfani da su wajen tantance masu kada kuri’a su ma an tanade su tare da tabbatar da nagartarsu.

Ya jaddada kudirin INEC na gudanar da sahihin zabe na gaskiya da adalci, inda ya ce hukumar za ta sanar da wanda ya yi nasara ne kawai bisa kuri’un da aka kada.

“Babbar damuwarmu a yanzu ita ce ’yan siyasa. Amma dai su ma sun rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya, sun kuma shaida mana za su yi zabe cikin lumana. Saboda kwanciyar hankali ne kawai zai ba ’yan kasa ’yancin zaben shugabanninsu,” in ji shi.

Dangane da yadda za a tattara sakamako, Zango ya ce za a bayyana sakamakon akwatuna a duk rumfunan zabe kafin a kai shi cibiyoyin tattarawa na mazabu.

Ana iya tuna cewa, tun a watan Yunin da ya gabata ne INEC ta ayyana 16 ga watan Agustan bana, a matsayin ranar da za a gudanar da zaben cike gurbi a kananan hukumomin na Kano.

Za a gudanar da zaben ne sakamakon rasuwar dan Majalisar Tarayya mai wakiltar Bagwai da Shonono, Halilu Ibrahim Kundila na jam’iyyar APC, wanda ya riga mu gidan gaskiya a ranar 6 ga watan Afrilun 2024.

Sai dai kuma za a gudanar da zaben cike gurbin ne a Karamar Hukumar Ghari — wadda a baya ake kira Kunc— a rumfunan zabe 10 da masu kada kuria 5200 bisa umarnin kotu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kano za a gudanar a gudanar da

এছাড়াও পড়ুন:

An kama mai babur ɗauke da ƙoƙunan kan mutane a Ogun

Rundunar ’yan sanda a Jihar Ogun ta ce, ta kama wani mai babur mai suna Kadir Owolabi, yana ɗauke da ƙoƙon kan mutane uku.

Mai magana da yawun rundunar, CSP Omolola Odutola ce ta bayyana hakan a wata sanarwa da ta fitar a Abeokuta ranar Talata.

Gwamnati ta amince a kafa sabbin jami’o’i masu zaman kansu guda 9 Bello Turji bai miƙa wuya ba har yanzu — DHQ

Odutola ta ce, binciken da jami’an ’yan sandan tafi da gidanka suka yi a jakar wanda ake zargin, ya kai ga gano wasu kan mutane guda uku.

Ta ce, jami’an tsaro ne suka gudanar da aikin bincike na yau da kullum daga rundunar ’yan sanda na tafi da gidanka na 71 PMF, a yankin Awa da ke Ijebu, da ƙarfe 2:00 na rana.

A ranar Litinin, a kan babbar titin Ijebu Ode zuwa Ibadan a mahaɗar ’yan gudun hijira, Oru Ijebu.

“A yayin atisayen, jami’an sun cafke Kadir Owolabi wanda ke kan babur, inda aka gudanar da bincike a kan jakunkunansa, an gano wasu kan mutane guda uku.

“Bincike na farko ya kai ga kama wani wanda ake zargi, mai suna Jamiu Yisa, mai shekara 53, a bayan sakatariyar Ƙaramar hukumar Ijebu Ode,” in ji ta.

Odutola ta ce, Kwamishinan ’yan sanda jihar, Lanre Ogunlowo ya umurci hukumar binciken manyan laifuka ta jihar da ta ɗauki ragamar lamarin domin gudanar da bincike mai zurfi.

Kakakin rundunar ta ƙara da cewa, rundunar ta sake jaddada aniyarta na ɗaukar ƙwararan matakai na yaƙi da miyagun laifuka, ta kuma  buƙaci mazauna yankin da su ba ’yan sanda haɗin kai tare da ba jama’a tabbacin amincewa da su da kuma basu kariyar sirri.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe
  • ‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Za Su Gudanar Da Zagaye Na 3 Na Aiki A Wajen Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Sin
  • An kama mai babur ɗauke da ƙoƙunan kan mutane a Ogun
  • Rashin Lantarki: Babu wanda za mu zaɓa a 2027 — Jama’ar Talasse
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 128
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 124
  • Gwamna Namadi Ya Yaba Wa Kungiyar NBA Bisa Inganta Manufofi Da Ka’idojin Aikin Lauya
  • EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi
  • Rundunar ‘Yan Sandan Kano Ta Yi Gargadi Game Da Sabawa Dokokin Fitillun Bada Hannu A Titinan Jihar