Aminiya:
2025-08-12@17:03:18 GMT

Harin ’yan fashi: An rufe Federal Poly Bauchi Bauchi

Published: 12th, August 2025 GMT

Hukumomin Kwalejin Kimiyya da Kere-kere ta Gwamnatin Tarayya sun ufe makarantar a sakamakon zanga-zangar da dalibai suka gudanar domin nuna fushinsu kan harin da ’yan fashi suka kai dakunan kwanansu.

Daliban sun tayar da tarzoma ne da sanyin safiyar Talata bayan harin ’yan fashin ya ya yi sanadiyyar jikkatar wasu dalaibai da dama, suna mazu zargin hukumomin kwalejin da kasa kare su daga abin da ya faru cikin dare.

Rahotanni since ’yan fashin sun kwace wa daliban kayayyakinsu, tare da jikkata mutum tara.

An dai ga fusatattun daliban suna gudanar da zanga-zanga a kan hanyar Bauchi zuwa Dass, inda suka daura shingen hana zirga-zirga a kofar shiga kwalejin.

’Yan sanda sun harba barkonon tsohuwa domin tarwatsa jama’a, lamarin da ya sa wasu daliban suka mayar da martani da duwatsu kafin daga bisani ’yan sanda su ci karfinsu.

Shugaban Kungiyar Dalibai (SUG) ta kwalejin, Haruna Umar, ya yi Allah-wadai da harin, inda ya bayyana shi a matsayin irinsa na farko a tarihin makarantar.

“’Yan fashin sun ji wa dalibi mai wakiltar aji daya na na matakin Difloma a fannin Kimiyyar Kwamfuta, Matta Musa rauni a kai. Wasu da suka samu raunuka an kai su Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBUTH) da ke Bauchi,” in ji shi.

Jami’in Hulda da Jama’a na kwalejin, Rabiu Wadda, ya shaida wa wakilinmu, cewa hukumar gudanarwar makarantar ta yi koqarin shawo kan lamarin kuma nan take ta rufe makarantar har zuwa wani lokaci domin hana tabarbarewar doka da oda.

Ya ce “Na kasance a makarantar tun karfe 4:00 na safe, muna kowarin shawo kan lamarin. A halin da ake ciki, ban samu shiga harabar ba.

“Yanzu, ba zan iya ba ku ainihin adadin daliban da abin ya shafa ba, amma na san an kai wasu daliban asibiti,” in ji shi.

“Hukumar gudanarwar Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta tarayya ta Bauchi, ta bayar da umarnin rufe harkokin ilimi a kwalejin,” a cewar wata sanarwa da aka rabawa jama’a a ranar Talata.

Magatakardar kwalejin, Kasimu Salihu, ya bayyana cewa wasu bata-gari sun mamaye dakin kwanan dalibai maza, inda suka kwashe kayansu tare da raunata kimanin dalibai biyu.

“Bayan wannan mummunan lamari, daliban sun fito daga babbar kogar kwalejin don nuna rashin jin dadinsu, suna masu kira ga hukumar da ta dauki matakin gaggawa, tare da duk manyan jami’an gudanarwa da ma’aikatan gudanarwa”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan fashi Ɗalibai

এছাড়াও পড়ুন:

Runduunar ‘Yan Sandan Jihar kwara Ta Karfafa Tsaro A Banbila

Rundunar ‘yan sandan jihar Kwara ta ce ta karfafa matakan tsaro a yankin Babanla biyo bayan harin da wasu da ake zargin mahara ne suka kai musu, inda suka kashe mutane 5 ciki har da dan sanda Adejumo Wasiu.

 

A cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sanda, SP Adetoun Ejinre-Adeyemi ya fitar, ya ce ‘yan fashi da makami da yawansu ya kai daruruwa, a kan babura, sun mamaye al’ummar Babanla a karamar hukumar Ifelodun.

 

A cewarsa wadanda ake zargin sun kai hari ne a hedikwatar ‘yan sanda inda suka kai farmaki cikin kasuwar.

 

Ya bayyana cewa maharan sun yi ta harbe-harbe kai-tsaye, inda suka kashe mutane 5 ciki har da dan sanda Adejumo Wasiu.

 

Sanarwar ta ce jami’an ‘yan sanda, jami’an Sojin Najeriya, ‘yan banga, da mafarauta cikin gaggawa sun dakile harin, tare da dawo da zaman lafiya, tare da fara farautar wadanda suka kai harin.

 

Ya yi nuni da cewa kwamishinan ‘yan sanda na jihar Kwara, Adekimi Ojo, tare da rakiyar daraktan hukumar tsaro ta farin kaya (DSS), sun kai ziyarar tantancewa Babanla domin tantance yanayin tsaro.

 

Sanarwar ta ci gaba da cewa, an samar da wani babban tsari domin tabbatar da zaman lafiya da karfafa hadin gwiwa tsakanin hukumomi da tsaro a cikin al’ummar da lamarin ya shafa.

 

Ta ce tawagar jami’an tsaron hadin gwiwa sun zagaya muhimman wurare a cikin al’umma – ciki har da kasuwa, da hedikwatar ‘yan sanda, da kewaye domin tabbatar da cewa an samu kwanciyar hankali.

 

REL/ALI MUHAMMAD RABIU

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Wasu Da Ake Zargin ‘Yan Kungiyar Asiri Ne A Jihar Kwara
  • Ruwan Wutan sojan Nijeriya Ya Kashe ‘Yan Bindiga A Zamfara.
  • ‘Yan Sandan Nasarawa Sun Kama Mutum Shida Da Laifin Fashi Da Makami Da Garkuwa Da Mutane
  • Runduunar ‘Yan Sandan Jihar kwara Ta Karfafa Tsaro A Banbila
  • Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara
  • Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas
  • An Maka Gwamnatin Neja Da NBC A Kotu Kan Barazanar Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM
  • Jefa Agajin Abinci Ta Sama A Zirin Gaza Ya Janyo Shahadan Falasdinawa 23 Tare Da Jikkata Wasu 124