Harin ’yan fashi: An rufe Federal Poly Bauchi Bauchi
Published: 12th, August 2025 GMT
Hukumomin Kwalejin Kimiyya da Kere-kere ta Gwamnatin Tarayya sun ufe makarantar a sakamakon zanga-zangar da dalibai suka gudanar domin nuna fushinsu kan harin da ’yan fashi suka kai dakunan kwanansu.
Daliban sun tayar da tarzoma ne da sanyin safiyar Talata bayan harin ’yan fashin ya ya yi sanadiyyar jikkatar wasu dalaibai da dama, suna mazu zargin hukumomin kwalejin da kasa kare su daga abin da ya faru cikin dare.
Rahotanni since ’yan fashin sun kwace wa daliban kayayyakinsu, tare da jikkata mutum tara.
An dai ga fusatattun daliban suna gudanar da zanga-zanga a kan hanyar Bauchi zuwa Dass, inda suka daura shingen hana zirga-zirga a kofar shiga kwalejin.
’Yan sanda sun harba barkonon tsohuwa domin tarwatsa jama’a, lamarin da ya sa wasu daliban suka mayar da martani da duwatsu kafin daga bisani ’yan sanda su ci karfinsu.
Shugaban Kungiyar Dalibai (SUG) ta kwalejin, Haruna Umar, ya yi Allah-wadai da harin, inda ya bayyana shi a matsayin irinsa na farko a tarihin makarantar.
“’Yan fashin sun ji wa dalibi mai wakiltar aji daya na na matakin Difloma a fannin Kimiyyar Kwamfuta, Matta Musa rauni a kai. Wasu da suka samu raunuka an kai su Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBUTH) da ke Bauchi,” in ji shi.
Jami’in Hulda da Jama’a na kwalejin, Rabiu Wadda, ya shaida wa wakilinmu, cewa hukumar gudanarwar makarantar ta yi koqarin shawo kan lamarin kuma nan take ta rufe makarantar har zuwa wani lokaci domin hana tabarbarewar doka da oda.
Ya ce “Na kasance a makarantar tun karfe 4:00 na safe, muna kowarin shawo kan lamarin. A halin da ake ciki, ban samu shiga harabar ba.
“Yanzu, ba zan iya ba ku ainihin adadin daliban da abin ya shafa ba, amma na san an kai wasu daliban asibiti,” in ji shi.
“Hukumar gudanarwar Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta tarayya ta Bauchi, ta bayar da umarnin rufe harkokin ilimi a kwalejin,” a cewar wata sanarwa da aka rabawa jama’a a ranar Talata.
Magatakardar kwalejin, Kasimu Salihu, ya bayyana cewa wasu bata-gari sun mamaye dakin kwanan dalibai maza, inda suka kwashe kayansu tare da raunata kimanin dalibai biyu.
“Bayan wannan mummunan lamari, daliban sun fito daga babbar kogar kwalejin don nuna rashin jin dadinsu, suna masu kira ga hukumar da ta dauki matakin gaggawa, tare da duk manyan jami’an gudanarwa da ma’aikatan gudanarwa”
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
HKI Ta Kashe Mutane 19 A Gaza Duk Tare Da Tsagaita Wuta
Majiyar asbitoci a yankin gaza na kasar Falasdinu da aka mamaye ta bada labarin cewa HKI ta kashe falasdinawa 19 a safiyar yau Asabar duk tare da cewa an fara tsagaita budewa juna wuta a yankin.
Tashar talabian ta Presstv a nan Tehran ta nakalto majiyar asbitoci a gaza na cewa bayan janyewar sojojin HKI daga wasu yankuna a Gazar sun zakulo gawakin falasdinawa 155 daga burbushin gine-gine wadanda HKI ta rusa a bayan.
Banda haka an kawo masu sabbin gawaki 19 wadanda sojojin HKI suka kashe a safiyar yau duk tare da cewa an fara yarjeniyar dakatar da budewa juna wuta.
Labarin ya kara da cewa gawaki 135 daga cikin 155 da aka kawo na kashe-kashen baya ne. Labarin ya kara da cewa an kashe mutane 16 a lokacinda wani jirgin yakin HKI ya kai hari kanwani gida a Khan Yunus a safiyar yau Asabar. Wadanda suka mutun dangi guda ne.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Tana Goyon Bayan Duk Wani Shirin Zaman Lafiya Da Ya Hada Da Kawo Karshen Kisan Kiyashi A Gaza October 11, 2025 Faransa Da Jamus Da Kuma Birtaniya Sun Bayyana Aniyarsu Ta Ganin An Farfado Da Tattauna Da Iran October 11, 2025 Kungiyoyin Falasdinawa Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Tsagaita Bude Wuta A Gaza October 11, 2025 Venezuala Ta Bukaci Kwamitin Sulhun M.D.D Da Ya Tabbatar Da Cewa: Amurka Tana Barazana Ga Zaman Lafiya October 11, 2025 Pakistan Ta Kai Hari Kan Kasar Afganistan, Inda Ake Rade-Radin Kashe Shugaban Taliban Na Kasarta October 11, 2025 Putin: Natanyahu Yana Son Warware Matsaloli Da Iran Cikin Lumana Ba Tare Da Yaki Ba October 10, 2025 Majalisar Turai Ta Bukaci Kasashen Nahiyar Su Kakkabo Jiragen Yakin Rasha October 10, 2025 Sa’o’ii Da Fara Janyewar Sojojin HKI A Gaza An Fara Gano Gawakin Falasdinwa October 10, 2025 Falasdinawa Daga Kudancin Gaza Sun Fara Komawa Gidajensu Da Aka Rusa A Arewacin Yankin October 10, 2025 Rahotanni : Isra’ila ta fara janye dawa wasu yankuna na Gaza October 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci