Aminiya:
2025-11-27@22:20:22 GMT

Harin ’yan fashi: An rufe Federal Poly Bauchi Bauchi

Published: 12th, August 2025 GMT

Hukumomin Kwalejin Kimiyya da Kere-kere ta Gwamnatin Tarayya sun ufe makarantar a sakamakon zanga-zangar da dalibai suka gudanar domin nuna fushinsu kan harin da ’yan fashi suka kai dakunan kwanansu.

Daliban sun tayar da tarzoma ne da sanyin safiyar Talata bayan harin ’yan fashin ya ya yi sanadiyyar jikkatar wasu dalaibai da dama, suna mazu zargin hukumomin kwalejin da kasa kare su daga abin da ya faru cikin dare.

Rahotanni since ’yan fashin sun kwace wa daliban kayayyakinsu, tare da jikkata mutum tara.

An dai ga fusatattun daliban suna gudanar da zanga-zanga a kan hanyar Bauchi zuwa Dass, inda suka daura shingen hana zirga-zirga a kofar shiga kwalejin.

’Yan sanda sun harba barkonon tsohuwa domin tarwatsa jama’a, lamarin da ya sa wasu daliban suka mayar da martani da duwatsu kafin daga bisani ’yan sanda su ci karfinsu.

Shugaban Kungiyar Dalibai (SUG) ta kwalejin, Haruna Umar, ya yi Allah-wadai da harin, inda ya bayyana shi a matsayin irinsa na farko a tarihin makarantar.

“’Yan fashin sun ji wa dalibi mai wakiltar aji daya na na matakin Difloma a fannin Kimiyyar Kwamfuta, Matta Musa rauni a kai. Wasu da suka samu raunuka an kai su Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBUTH) da ke Bauchi,” in ji shi.

Jami’in Hulda da Jama’a na kwalejin, Rabiu Wadda, ya shaida wa wakilinmu, cewa hukumar gudanarwar makarantar ta yi koqarin shawo kan lamarin kuma nan take ta rufe makarantar har zuwa wani lokaci domin hana tabarbarewar doka da oda.

Ya ce “Na kasance a makarantar tun karfe 4:00 na safe, muna kowarin shawo kan lamarin. A halin da ake ciki, ban samu shiga harabar ba.

“Yanzu, ba zan iya ba ku ainihin adadin daliban da abin ya shafa ba, amma na san an kai wasu daliban asibiti,” in ji shi.

“Hukumar gudanarwar Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta tarayya ta Bauchi, ta bayar da umarnin rufe harkokin ilimi a kwalejin,” a cewar wata sanarwa da aka rabawa jama’a a ranar Talata.

Magatakardar kwalejin, Kasimu Salihu, ya bayyana cewa wasu bata-gari sun mamaye dakin kwanan dalibai maza, inda suka kwashe kayansu tare da raunata kimanin dalibai biyu.

“Bayan wannan mummunan lamari, daliban sun fito daga babbar kogar kwalejin don nuna rashin jin dadinsu, suna masu kira ga hukumar da ta dauki matakin gaggawa, tare da duk manyan jami’an gudanarwa da ma’aikatan gudanarwa”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan fashi Ɗalibai

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaba Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Harkar Tsaro Tare da Bada Umurnin Daukar Sabbin Jami’ai

Daga Bello Wakili

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya ayyana dokar ta-baci kan harkar tsaro a duk fadin kasar, sakamakon karuwar kalubalen tsaro da ake fuskanta.

Shugaban ya ce za a dauki sabbin jami’an tsaro nan ba da jimawa ba, wadanda suka hada da na sojiin, ‘yan sanda da sauran hukumomin tsaro — domin karfafa matakan tsaron kasa.

A karkashin sabon umarnin, an bai wa Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ikon daukar karin jami’aaidubu ashirin,  wanda hakan zai kawo yawan sabbin  jami’an da za a dauka bana zuwa dubu hamsin.

Shugaban kasar ya kuma amince a yi amfani da sansanonin horas da matasa masu yi wa kasa  NYSC a matsayin wuraren horaswa na wucin gadi, sakamakon gyare-gyaren da ake yi a makarantun horar da ‘yan sanda a fadin kasar.

Haka zalika Jami’an da aka cire daga ayyukan tsaron manyan mutane za su samu horo na gaggawa kafin a tura su zuwa yankunan da ke da hadari.

Shugaban ya kuma bai wa Hukumar tsaro ta DSS umarnin gaggauta tura dakaru masu horo na musamman zuwa dazuka domin yaki da ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga. A don haka, hukumar ta DSS za ta dauki karin ma’aikata don karfafa wannan aiki.

Shugaba Tinubu ya bukaci ‘yan Najeriya su bada hadin kai ga matakan tsaron da ake dauka.

Ya yaba wa jami’an tsaro bisa ceto daliban Jihar Kebbi 24 da aka yi garkuwa da su, da masu ibada 38 a Jihar Kwara, tare da tabbatar da cewa ana ci gaba da kokarin kubutar da daliban da aka yi garkuwa da su a Jihar Niger da sauran wadanda ke tsare.

Shugaban ya umurci Rundunar Soji ta kara zafafa ayyuka a dukkan yankunan da ake rikici, tare da jaddada muhimmancin ladabi, gaskiya da kin amincewa da cin hanci ko sakaci.

Ya mika ta’aziyya ga iyalan wadanda aka kashe a hare-haren da suka faru a Kebbi, Borno, Zamfara, Niger, Yobe da Kwara, tare da karrama jaruman sojojin da suka rasa rayukansu, ciki har da Birgediya-Janar Musa Uba.

Shugaba Tinubu ya sake tabbatar da goyon bayansa ga jami’an saro na jihohi, tare da kira ga Majalisar Dokoki ta Kasa da ta fara nazarin dokokin da za su bai wa jihohin da ke son kafa ‘yan sandan jiha damar yin hakan.

Ya shawarci gwamnatocin jihohi su sake duba tsarin kafa makarantun kwana a wuraren da ke da nisa ba tare da wadatattun matakan tsaro ba, sannan ya yi kira ga cibiyoyin addini su kara inganta tsaron wuraren ibada.

Dangane da rikice-rikicen manoma da makiyaya, Shugaban ya bukaci kungiyoyin makiyaya da su rungumi tsarin kiwo na zamani (ranching) tare da yin aiki tare da Gwamnatin Tarayya ta hannun sabuwar Ma’aikatar Raya Kiwo.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati Za Ta Biya Wasu Kudaden Ariyas Ga Masu Fensho Wannan Wata
  • Gwamna Kefas Ya Bayyana Alhininsa Bisa Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
  • Juyin mulki ya rutsa da Jonathan a Guinea-Bissau
  • Shugaba Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Harkar Tsaro Tare da Bada Umurnin Daukar Sabbin Jami’ai
  • Sojoji sun yi juyin mulki a Guinea-Bissau
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi 34 a Kaduna
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi da 34 a Kaduna
  • Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS
  • Tinubu Ya Nuna Farin Cikinsa Bisa Bayyanar Daliban Kebbi, Ya Bukaci a Ceto Sauran
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano