Aminiya:
2025-08-15@19:09:26 GMT

An sake ceto matafiya 10 da aka sace a Kogi

Published: 15th, August 2025 GMT

Jami’an tsaro sun kuɓutar da wasu fasinjoji 10 da aka yi garkuwa da su a hanyar Itobe – zuwa Ochadamu – Anyigba a Ƙaramar hukumar Ofu a Jihar Kogi.

Fasinjojin da aka kuɓutar an yi garkuwa da su ne a ranar 11 ga watan Agusta a ƙauyen Ugbakpedo da ke kan titin, lokacin da wata mota ta yi wa fasinjojin kwanton ɓauna.

Tinubu ya bar Abuja zuwa Japan da Brazil Matsalar ƙofa ta hana fasinjoji 58 hawa jirgin Abuja zuwa Landan

Jami’an tsaron da suka haɗa da: ’yan sanda da ’yan banga da mafarautan yankin sun bayyana cewa sun afkawa dajin da ke yankin kafin ceto matafiyan.

“A ranar 13 ga watan Agusta da misalin ƙarfe 4:30 na Asubahi ne yayin wani gagarumin farmaki tare da amfani da hayaƙi mai sa hawaye, masu garkuwa da mutanen suka yi watsi da waɗanda kama suka gudu.

“An ceto dukkan mutane 10 da aka yi garkuwan da su ba tare da sun samu rauni ba, kuma tuni aka  haɗa su da iyalansu,” in ji wani rahoton tsaro kan lamarin.

Rahoton jami’an tsaro ya ƙara da cewa, ana ƙara tattara bayanan sirri da sa ido da kuma ganowa tare da yunkurin kama waɗanda ake zargin da suka tsere inda zargin masu garkuwa da mutane ne.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan Jihar (PPRO), SP William Aya ya tabbatar da ceto matafiya da aka yi garkuwa da su a ranar Juma’a a Lokoja.

Ya ce, an kuɓutar da matafiyan ne tare da haɗin gwiwa jami’an tsaro, tare da ‘yan banga da mafarauta wanda ya yi nasarar ceto waɗanda aka sace.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan banga Yan Sanda

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda Ƙananan Hukumomi Ke Yin Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina

Wani mazaunin Safana, Iliyasu Sani, ya ce sulhun ya kawo sauƙi ga rayuwar jama’a, domin yanzu suna iya zuwa kasuwa da yin noma ba tare da fargaba ba.

Masani a fannin tsaro, Kabiru Adamu, ya ce talauci da rashin tsaro ne suka sa jama’a neman mafita da kansu.

Ya kuma bayyana cewa idan duk ɓangarorin suka tsaya kan alƙawarin da aka yi, wannan sulhu na iya zama mataki na farko na samun zaman lafiya na dindindin a yankin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutum 12 sun rasu, 5 sun jikkata a hatsarin mota a Kano
  • Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi
  • Sojoji Sun Kama Mutane 107 Da Ake Zargi, Sun Ceto Mutane 20 A Cikin Maku Guda – DHQ
  • Gwamnati ta amince a kafa sabbin jami’o’i masu zaman kansu guda 9
  • Bello Turji bai miƙa wuya ba har yanzu — DHQ
  • Gwamna Sule Ya Ziyarci Gidan Yarin Keffi Bayan Tserewar Fursunoni 16
  • ’Yan ci-rani 26 sun nitse a teku suna ƙoƙarin tsallakawa Turai
  • ’Yan bindiga sun kashe tsohon malamin makaranta a Edo
  • Yadda Ƙananan Hukumomi Ke Yin Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina