Aminiya:
2025-10-13@18:05:30 GMT

An sake ceto matafiya 10 da aka sace a Kogi

Published: 15th, August 2025 GMT

Jami’an tsaro sun kuɓutar da wasu fasinjoji 10 da aka yi garkuwa da su a hanyar Itobe – zuwa Ochadamu – Anyigba a Ƙaramar hukumar Ofu a Jihar Kogi.

Fasinjojin da aka kuɓutar an yi garkuwa da su ne a ranar 11 ga watan Agusta a ƙauyen Ugbakpedo da ke kan titin, lokacin da wata mota ta yi wa fasinjojin kwanton ɓauna.

Tinubu ya bar Abuja zuwa Japan da Brazil Matsalar ƙofa ta hana fasinjoji 58 hawa jirgin Abuja zuwa Landan

Jami’an tsaron da suka haɗa da: ’yan sanda da ’yan banga da mafarautan yankin sun bayyana cewa sun afkawa dajin da ke yankin kafin ceto matafiyan.

“A ranar 13 ga watan Agusta da misalin ƙarfe 4:30 na Asubahi ne yayin wani gagarumin farmaki tare da amfani da hayaƙi mai sa hawaye, masu garkuwa da mutanen suka yi watsi da waɗanda kama suka gudu.

“An ceto dukkan mutane 10 da aka yi garkuwan da su ba tare da sun samu rauni ba, kuma tuni aka  haɗa su da iyalansu,” in ji wani rahoton tsaro kan lamarin.

Rahoton jami’an tsaro ya ƙara da cewa, ana ƙara tattara bayanan sirri da sa ido da kuma ganowa tare da yunkurin kama waɗanda ake zargin da suka tsere inda zargin masu garkuwa da mutane ne.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan Jihar (PPRO), SP William Aya ya tabbatar da ceto matafiya da aka yi garkuwa da su a ranar Juma’a a Lokoja.

Ya ce, an kuɓutar da matafiyan ne tare da haɗin gwiwa jami’an tsaro, tare da ‘yan banga da mafarauta wanda ya yi nasarar ceto waɗanda aka sace.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan banga Yan Sanda

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’ar MDD: Taron Kolin Matan Duniya Ya Zo Daidai Lokacin Da Ya Dace

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Mutane A Fadin Duniya Sun Soki Ayyukan Neman ‘Yancin Kan Taiwan October 12, 2025 Daga Birnin Sin Sharhi: Lai Qingde Ba Zai Iya Jirkita Gaskiya Ba October 12, 2025 Daga Birnin Sin Wang Yi: Sin Na Maraba Da Dukkanin Matakai Na Dawo Da Zaman Lafiya A Gaza October 11, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno
  • Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku
  • ASUU ta tsunduma yajin aikin mako 2
  • Jami’ar MDD: Taron Kolin Matan Duniya Ya Zo Daidai Lokacin Da Ya Dace
  • Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna
  • Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba
  • Babban Kwamanda Ya Jagoranci Ceton Mutanen Da Aka Sace A Kwara
  • ’Yan bindiga sun kashe Civilian JTF 8 a Zamfara