HausaTv:
2025-08-17@07:40:53 GMT

Denmark na nazarin kakaba wa Isra’ila takunkumi kan batun Gaza

Published: 17th, August 2025 GMT

Firaministar kasarDenmark Mette Frederiksen, wadda a halin yanzu kasarta ke rike da shugabancin kungiyar Tarayyar Turai ta bayyana a wata sanarwa ga manema labarai a jiya Asabar cewa, kasarta na shirin kakabawa Isra’ila takunkumi, sakamakon yakin da take yi a zirin Gaza da yammacin kogin Jordan.

A wata hira da ya yi da Jyllands-Posten, Frederiksen ta ce “Yanzu Netanyahu ya zama matsala shi a kan kansa,” tana mai cewa “gwamnatin Isra’ila ta wuce gona da iri.

Ta bayyana halin da ake ciki na jin kai a Gaza a matsayin “mummunan bala’i,” tare da sukar shirin Isra’ila na ci gaba da aikin tsugunar da jama’a a Yammacin Kogin Jordan.

Firaministar Denmark ta jaddada cewa kasarta na cikin kasashen da ke neman kara matsin lamba kan Isra’ila, amma har yanzu baki bai zo daya kan wannan batu a tsakanin dukkanin mambobin kungiyar EU ba.

Ta kara da cewa tana son yin amfani da “matsi na siyasa da takunkumi, ko a kan ‘yan share wuri zauna ko ministoci, ko ma a kan gwamnatin Isra’ila baki daya.

Kimanin mako guda da ya gabata ne ministan harkokin wajen Denmark Lars Løkke Rasmussen ya yi kira ga Isra’ila da ta gaggauta janye matakin da ta dauka na mamaye yankin zirin Gaza, yana mai nuna matukar damuwarsa kan halin da ake ciki na jin kai da kuma wahalar da ake fuskanta wajen  kai agajin jin kai  ga al’ummar Gaza.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Jakadan Iran a Saudiyya: Kasashen biyu na tuntubar juna a kan muhimman batutuwa na yankin August 17, 2025 Gaza: A cikin sa’o’i 24 Mutane da dama sun yi shahada daruruwa sun jikkata a hare-haren Isra’ila August 17, 2025 An kashe mutane 17 a harin da dakarun RSF suka kai a  El Fasher, Sudan August 17, 2025 Kasashen Larabawa Da Na Musulmi Sun Yi Allah Wadai Da Kalaman Netanyahu Kan Mamaye Yankunan Kasashe August 16, 2025 Iran Ta Yi Allah Wadai Da Furucin Jami’ar Kotun ICJ Na Goyon Bayan Isra’ila August 16, 2025 Araqchi  Ya Gode Wa Gwamnatin Iraki Da Al’ummarta Kan Kyakkyawar Tarbar Masu Ziyarar Arba’een August 16, 2025 Hamas Ta Yi Allah Wadai Da Sanya Ta Cikin Jerin Sunayen Bakin Littafin MDD August 16, 2025 Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Tafka Muggan Ayyukansu A Yankin Zirin Gaza August 16, 2025 Mataimakiyar Shugaban Kotun ICJ Ta Ce Tana Goyon Bayan HKI August 16, 2025 Burtaniya Zata Gurfanar Da mutane 60 Saboda Goyon Bayan Falasdinawa August 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Bukaci Mayar Da Martani Kan Aniyar Isra’ila Ta Mamaye Yankunan Kasashe Domin Kafa ‘Babbar Isra’ila’

Kasar Iran ta jaddada wajabcin daukar kwararan matakai na kasa da kasa don dakile muradun gwamnatin mamaya na mulkin mallaka

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Ismail Baqa’i ya yi Allah wadai da kalaman fira ministan gwamnatin ‘yan sahayoniyya da ake nema ruwa a jallo a kotun kasa da kasa ya yi dangane da abin da ake kira “Kafa kasar babban Isra’ila”. Wadannan kalamai tana nuna karara aniyar gwamnatin mamayar Isra’ila na ci gaba da kai hare-hare kan yankunan kasashe masu cin gashin kansu da suka hada da Masar, da Jordan, da Lebanon da kuma Syria, tare da la’akari da su a matsayin babban misali na keta dokokin Majalisar Dinkin Duniya da dokokin kasa da kasa.

A cikin wani rubutu da ya wallafa a safiyar yau Alhamis, Baqa’i ya yi ishara da yadda ake ci gaba da keta doka da kuma aikata munanan laifuka da gwamnatin ‘yan sahayoniyya ta ke tafkawa, musamman ma mamaye yankunan Falasdinawa da kisan kare dangi da ake ci gaba da yi a kan al’umma Falasdinu.

Baqa’i ya ci gaba da cewa: Amincewar da fira ministan gwamnatin ‘yan sahayoniyya ya yi na cewa yana da ”aiki na tarihi da na ruhi” don tabbatar da wannan muguwar tunani tun daga kogin Nilu har zuwa Fırat, wata shaida ce karara ta mulkin mallaka ta masu yanke shawarar wannan gwamnati ta miyagun al’umma da kuma kai hari kan ‘yantacciyar kasa mai ikon domin mamaye yankunan kasashensu, kuma wajibi ne a yi Allah wadai da wannan muguwar manufa ta tunanin mamaye yankunan kasashen musulmi daga babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya da  kungiyar hadin kan kasashen musulmi, da dukkanin gwamnatoci, a matsayin wannan furuci na cin zarafi da keta ƙa’idodi da manufofin Yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya da dokokin dokokin ƙasa da ƙasa.”

Iran

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ya Bayyana Isra’ila A Matsayar ‘Yar Yaudara August 14, 2025 Hizbullahi Ta Yaba Wa Iran Kan Irin Gudumawarta Ga Lebanon Da Gwagwarmaya August 14, 2025 Majalisar Dinkin Duniya Ta Yi Fatali Da Batun Kafa Gwamnatin Hadaka A Kasar Sudan August 14, 2025 Larijani a Beirut: Iran A Shirye take ta taimaka ma Lebanon August 14, 2025 Masar ta yi Allawadai da furucin Netanyahu kan shirin kafa Isra’ila Babba August 14, 2025 Hamas ta aike da sakon jinjina ga al’ummar Yemen kan goyon bayan Gaza August 14, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 130 August 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 129 August 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 128 August 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Imam Hassan (a) 127 August 13, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gaza: A cikin sa’o’i 24 Mutane da dama sun yi shahada daruruwa sun jikkata a hare-haren Isra’ila
  • Kasashen Larabawa Da Na Musulmi Sun Yi Allah Wadai Da Kalaman Fira Ministan Isra’ila Kan Mamaye Yankunan Kasashe
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Tafka Muggan Ayyukansu A Yankin Zirin Gaza
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Kansu
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kai Wani Mummunan Hari Kan Gaza Tare Da Rusa Gidajen Mutane A Khan Yunis
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Kansu Bayan Yakin Gaza
  • Kungiyoyin Kasa Da Kasa Sun Koka Kan Hana Shigar Da Kayayyakin Jin Kai Yankin Gaza
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Yi Tsokaci Kan Furucin Netanyahu Game Da Kafa “Babbar Kasar Isra’ila’
  • Iran Ta Bukaci Mayar Da Martani Kan Aniyar Isra’ila Ta Mamaye Yankunan Kasashe Domin Kafa ‘Babbar Isra’ila’