Ranar Matasa: Ciyaman ya jinjina wa gwamnatin Gombe kan ɗaukar matasa aiki
Published: 13th, August 2025 GMT
Shugaban Ƙaramar Hukumar Gombe, Barista Sani Ahmad Haruna, ya gode wa Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya saboda ɗaukar matasan da aka horar ƙarƙashin shirin GOSTEC aiki a matsayin cikakkun ma’aikata.
Ya ce wannan mataki ya nuna jajircewar gwamnati wajen taimaka wa matasa domin rage zaman banza da kuma ba su damar dogaro da kai.
Ya ƙara da cewa, yanzu wasu daga cikin matasan sun za su hidimata wa al’umma, saɓanin halin da suke ciki a baya.
Ya roƙi matasan su zama masu gaskiya, riƙon amana da kishin ƙasa, inda ya bayyana cewa su ne ginshiƙin ci gaban kowace al’umma.
Ɗaya daga cikin matasan da aka ɗauka aikin, Musa Abdullahi, ya ce shirin GOSTEC, ya sauya rayuwarsa daga neman aiki zuwa taimakawa wajen bunkasa tattalin arziƙin jihar.
Ita ma, Fatima Mohammed, ta bayyana farin cikinta da samun aikin gwamnati bayan samun horo a fannin shafukan Intanet, tare da yaba wa gwamnati saboda ƙoƙarin inganta rayuwar matasa.
Bikin, ya samu halartar jami’an gwamnati, ƙungiyoyin matasa, inda aka tattauna kan makomar matasa, ilimi da ci gaban tattalin arziƙi a jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Barista Sani ranar matasa ta duniya Shugaban karamar hukuma
এছাড়াও পড়ুন:
El-Rufai ya koma jami’yyar haɗaka ta ADC
Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai ya sauka sheƙa daga jam’iyyar SDP zuwa jami’yyar haɗaka ta ADC.
Komawar El-Rufai jam’iyyar ADC a hukumance wani mataki ne da ake ganin zai kawo sabon salo a siyasar adawa wajen ƙalubalantar jam’iyyar APC mai mulki a Zaɓen 2027.
An janye ’yan sanda 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya Mbappe ya ci ƙwallaye 4 rigis a wasan Madrid da OlympiacosA wannan Alhamis ɗin ce El-Rufai ya kammala rajistar zama mamba na jam’iyyar ADC a mazaɓarsa ta Unguwar Sarki da ke birnin Kaduna, inda ya yi alƙawarin amfani da jam’iyyar ADC wajen fuskantar abin da ya kira rashin ƙwarewa a jagorancin gwamnatin jihar.
“Ina da cikakkiyar rajista a jam’iyyar African Democratic Congress,” in ji shi a gaban manyan jami’an jam’iyyar, ciki har da Mataimakin Shugaban ADC na Arewa maso Yamma, Jafaru Sani, da Sakataren Yi wa Mambobi Rajistar Jam’iyyar na Ƙasa, Sanata Sadiq Yar’adua.
A watan Maris na bana ne dai El-Rufai ya sauya sheƙa daga APC zuwa SDP a wani yunƙuri na shirya haɗin gwiwar adawa, sai dai ya ce tattaunawar da suke yi a SDP ɗin ta gaza haifar da ɗa mai ido wajen cimma muradinsu saboda “tsoma bakin gwamnati da kuma cin hanci da wasu shugabannin jam’iyyar ke yi.”
Da yake jawabi kan siyasar Jihar Kaduna, El-Rufai ya yi kira ga jama’a da su yi rajista da ADC domin “maimaita abin da muka yi a 2015,” yana mai zargin gwamnatin APC mai ci da sakaci da jagorancin al’umma.
“Ina kira ga dukkan ’yan Kaduna masu shekaru 18 zuwa sama da su fito su yi rajista. Da ikon Allah, zamu sake kawar da gwamnatin da ta nuna gazawa.
“Mu da muka taimaka muka ɗora su a kujerar mulki, za mu taimaka wajen dawo da su gida… kafin su wuce kotu,” in ji El-Rufai.