An Yi Kira Ma’aikatan Watsa Labarai Su Tabbatar da Gaskiya A Ayukkan Su
Published: 13th, August 2025 GMT
An yi kira ga kwararrun kafafen yada labarai da su tabbatar da madogararsu domin tabbatar da samar da kyakykyawan rahoton abubuwan da ke faruwa a cikin al’umma.
Babban Limamin Masallacin Al-Waheed Central, Imam Mustapha Luqman ne ya yi wannan kiran a lokacin da yake jawabi a wajen taron hadin gwiwa da kungiyar ‘yan jarida ta NUJ ta shirya domin fara taron makon manema labarai na shekara ta 2025, da kuma bikin cika shekara 45 daka guda a Ilorin jihar Kwara
Ya shawarce su da su bi ka’ida wajen gudanar da ayyukansu na yada labarai.
Imam Lukman ya bukaci masu aikin yada labarai da su kasance masu adalci da kyautatawa a tsakaninsu .
A nasa jawabin, Fasto Adedoyin Adeyemi ya shawarci masu sana’ar yada labarai da su kasance masu halin kirki a lokacin da suke aikin su.
Ya bukace su da su tuna cewa ba za su iya kasancewa kan aikin ba har abada. ya kara da cewa ya kamata mambobin cocin su yi tasiri a rayuwar mutane.
Fasto Adeyemi ya shawarce su da su so juna da kyautatawa a kowane lokaci.
Ya shawarci ‘yan Najeriya da su kasance da ruhin yafiya da kuma yi wa shugabanni addu’a Allah ya sa su jagoranci al’umma daidai.
COV/ALI MUHAMMAD RABIU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kwara yada labarai
এছাড়াও পড়ুন:
Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano
ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya October 13, 2025
Manyan Labarai Ta’addanci: Ana Fuskantar Ƙarancin Man Fetur A Mali Sakamakon Datse Hanyoyin Shiga Bamako October 13, 2025
Manyan Labarai Tinubu Ya Isa Birnin Rome Don Halartar Taron Tsaro Na Aqaba October 12, 2025