Aminiya:
2025-08-12@23:07:20 GMT

An kama basarake kan zargin yi wa ’yar shekara 12 fyaɗe a Gombe

Published: 13th, August 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe ta cafke wani basarake, Mohammed Tukur mai shekaru 55, a kauyen Sabon Gari da ke yankin Zambuk na Ƙaramar Hukumar Yamaltu Deba, bisa zargin yi wa wata yarinya ’yar shekara 12 fyaɗe.

Mai magana da yawun rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya tabbatar da faruwar lamarin cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata.

EFCC ta saki Tambuwal Bankin Duniya zai kashe $300m domin inganta rayuwar ’yan gudun hijira a Arewacin Nijeriya

Ya ce abin ya faru ne da misalin ƙarfe 9:00 na daren ranar 9 ga Agusta, 2025, lokacin da ake zargin ya yaudari yarinyar wadda ya kaita wani wuri da babu idon jama’a ya aikata ta’asar.

Bayan samun rahoton faruwar lamarin ne, jami’an ’yan sanda daga ofishin Zambuk suka hanzarta zuwa wurin, sannan suka mika yarinyar zuwa Asibitin Zambuk domin duba lafiyarta.

Nan take dai rundunar ta cika hannu da wanda ake zargin, kuma a halin yanzu yana tsare a hannun ’yan sanda, yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: basarake fyaɗe jihar Gombe yarinya

এছাড়াও পড়ুন:

EFCC ta kama ’yan damfara a ɗakin karatun Obasanjo 

Jami’an Hukumar Yaƙi da Yi Wa Tattalin Arziƙi Zagon Ƙasa (EFCC), sun kai samame a Ɗakin Karatun Olusegun Obasanjo da ke Abeokuta, a Jihar Ogun, inda suka kama wasu matasa da ake zargin ’yan damfara ne.

Samamen ya faru ne da safiyar ranar Lahadi a sashen otal na ɗakin karatun.

’Yan bindiga sun kashe gomman mutane a ƙauyukan Sakkwato An ɗaure tsohon Firaminista Succes Masra shekaru 20 a Chadi

Gidan Obasanjo na musamman yana cikin harabar ɗakin karatun.

Wani faifan bidiyo da ya karaɗe kafafen sada zumunta, ya nuna yadda wasu matasa ke gudu domin ka da EFCC ta kama su.

Rahotanni sun ce jami’an EFCC sun ƙwace sama da motoci 20 tare da wasu kayayyaki masu daraja.

Wani jami’in EFCC ya shaida wa Aminiya cewa samamen ya samo asali ne daga Ofishin EFCC na Legas.

Daraktan Kamfanin OOPL Ventures, Mista Vitalis Ortese, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa suna ƙoƙarin samun ƙarin bayani daga EFCC.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya ce zai yi bincike kafin ya yi wa manema labarai ƙarin bayani.

Wannan na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan jami’an EFCC daga Ofishin Ibadan suka kama mutum 56 da ake zargi da aikata damfara a Intanet a wani otal mai suna K-Hotel da ke Itori, a Jihar Ogun.

An kama ɗaya daga waɗanda ake zargin da bindigogi guda biyu.

EFCC ta kuma ƙwato motoci shida masu tsada, wayoyin salula 89, kwamfutoci, da wasu takardu.

Hukumar ta ce nan ba da jimawa ba za ta gurfanar da dukkanin waɗanda ta kama a gaban kotu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ɗan shekara 18 kan zargin fashi da makami a Gombe
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Wasu Da Ake Zargin ‘Yan Kungiyar Asiri Ne A Jihar Kwara
  • Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe
  • An kama mutumin da ake zargi da kashe jami’in sibil difens a Jigawa
  • Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya
  • Sojoji sun kama wasu kan zargin kitsa juyin mulki a Mali
  • EFCC ta kama ’yan damfara a ɗakin karatun Obasanjo 
  • NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 
  • NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja