Ambaliya: Magidanta da dama sun rasa muhallinsu a Yobe
Published: 15th, August 2025 GMT
Ruwan sama kamar da bakin ƙwarya da aka yi a garin Potiskum a daren Juma’a zuwa safiyar yau Juma’a ya haifar da ambaliya, wanda ya haifar da tashin hankali ga mazauna garin.
Kamar yadda majiyar da ke garin ta shaidawa Aminiya cewa, ruwan sama kamar da bakin ƙwarya da aka fara shi tun kusan tsakar daren Alhamis ya yi sanadiyyar rugujewar gidaje da dama, inda wasu gine-gine suka ruguje ƙarƙashin ruwan.
Sakamakon ambaliyar ruwan ya sa mazauna wasu unguwanni da dama suka rasa matsugunansu inda suke hijira ya zuwa gidajen ‘yan uwa da makarantu, inda suke kokawa kan yadda iftala’in ta afku.
Wannan ambaliyar ruwa da ta faru rahotanni na nuna cewa, wasu gine-gine sun ruguje tare da rushewar maƙabarta yayin da wasu kuma suka nutse kamar yadda aka ambata a baya.
Nura Badamasi da ke unguwar bayan tsohon gidan gyaran hali wanda ɗaya ne daga cikin waɗanda abin ya shafa ya tabbatarwa da Aminiya cewa, bai fita da komai ba daga cikin gidansa sai da rigar da ke jikinsa kaɗai sauran kayayyakinsa da na iyalansa duka babu domin ambaliyar ta tafi da su da muhallinsa gaba ɗaya abin ba’a cewar komai sai dai Allah SWT ya kawo musu ɗauki.
Don haka ne ma yake roƙon gwamnatin Jihar Yobe da Ƙaramar hukumar Potiskum da su kawo musu ɗauki da kuma taimaka musu domin shawo kan matsalar ambaliyar ruwan da a kullum suke fuskantar barazana akai, kana su kuma kawo musu ɗaukin gaggawa don tallafa musu.
Unguwanni da wannan ambaliyar tafi shafa sun haɗa da: Unguwar Jigawa da Bayan tsohon gidan yari da Unguwar makafi da wasu unguwannin gabas da Kasuwa.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi sauye-sauyen jagoranci a Hukumar Talabijin ta ƙasa (NTA), inda ya naɗa Rotimi Richard Pedro a matsayin sabon Darakta-Janar. Sauran naɗe-naɗen sun haɗa da Karimah Bello a matsayin Babbar Darakta ta Sashen Tallace-Tallace, Stella Din a matsayin Babbar Darakta ta Sashen Labarai, da Sophia Essahmed a matsayin Manajing Darakta ta Kamfanin NTA Enterprises Limited.
Pedro, ɗan asalin jihar Lagos, ƙwararren mai ba da shawara ne a harkar kafofin watsa labarai, mai gogewa sama da shekaru 30 a fannoni da suka haɗa da talabijin, haƙƙoƙin watsa wasanni, da dabarun tallace-tallace a Afrika, da Birtaniya da Gabas ta Tsakiya. Kwararre ne a fannin nishaɗi da mallakar fasaha, tare da digirin na biyu a Gudanar da Zuba Jari daga jami’ar City Business School, London.
2027: Jagororin APC Na Kudu-maso-Yamma Sun Amince Da Tinubu Ya Sake Tsayawa Takara Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – SoludoA 1995, ya kafa Optima Sports Management International (OSMI), wanda ya shahara wajen yaɗa manyan gasanni kamar Premier League na Ingila, da UEFA Champions League, da Gasar Cin Kofin Duniya ta FIFA, da wasannin CAF zuwa ƙasashe sama da 40. Haka kuma, ya yi aiki a manyan muƙamai a Bloomberg Television Africa, Rapid Blue Format, da kuma matsayin mai ba da shawara ga FIFA, da UEFA, da Fremantle Media, da Ƙungiyar Masu Watsa Labarai ta Afrika (AUB).
Masana sun bayyana Pedro a matsayin wanda ya yi fice wajen samar da kafafen yaɗa labarai masu ƙarfi a kasuwanci, da ƙara samun kuɗin tallafi, da kawo shirye-shirye masu inganci ga masu kallo a Afrika. Wannan naɗin na nuna manufar Gwamnatin Tarayya na sabuntawa da sake gina NTA domin ta yi gogayya a kasuwar watsa labarai ta zamani.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp