Aminiya:
2025-10-13@17:48:29 GMT

Ambaliya: Magidanta da dama sun rasa muhallinsu a Yobe

Published: 15th, August 2025 GMT

Ruwan sama kamar da bakin ƙwarya da aka yi a garin Potiskum a daren Juma’a zuwa safiyar yau Juma’a ya haifar da ambaliya, wanda ya haifar da tashin hankali ga mazauna garin.  

Kamar yadda majiyar da ke garin ta shaidawa Aminiya cewa, ruwan sama kamar da bakin ƙwarya da aka fara shi tun kusan tsakar daren Alhamis ya yi sanadiyyar rugujewar gidaje da dama, inda wasu gine-gine suka ruguje ƙarƙashin ruwan.

An sake ceto matafiya 10 da aka sace a Kogi Tinubu ya bar Abuja zuwa Japan da Brazil

Sakamakon ambaliyar ruwan ya sa mazauna wasu unguwanni da dama suka rasa matsugunansu inda suke hijira ya zuwa gidajen ‘yan uwa da makarantu, inda suke kokawa kan yadda iftala’in ta afku.

Wannan ambaliyar ruwa da ta faru rahotanni na nuna cewa, wasu gine-gine sun ruguje tare da rushewar maƙabarta yayin da wasu kuma suka nutse kamar yadda aka ambata a baya.

Nura Badamasi da ke unguwar bayan tsohon gidan gyaran hali wanda ɗaya ne daga cikin waɗanda abin ya shafa ya tabbatarwa da Aminiya cewa, bai fita da komai ba daga cikin gidansa sai da rigar da ke jikinsa kaɗai sauran kayayyakinsa da na iyalansa duka babu domin ambaliyar ta tafi da su da muhallinsa gaba ɗaya abin ba’a cewar komai sai dai Allah SWT ya kawo musu ɗauki.

Don haka ne ma yake roƙon gwamnatin Jihar Yobe da Ƙaramar hukumar Potiskum da su kawo musu ɗauki da kuma taimaka musu domin shawo kan matsalar ambaliyar ruwan da a kullum suke fuskantar barazana akai, kana su kuma kawo musu ɗaukin gaggawa don tallafa musu.

Unguwanni da wannan ambaliyar tafi shafa sun haɗa da: Unguwar Jigawa da Bayan tsohon gidan yari da Unguwar makafi da wasu unguwannin gabas da Kasuwa.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya October 10, 2025 Daga Birnin Sin CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa October 10, 2025 Daga Birnin Sin Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka October 10, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa
  • Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya
  • Kungiyar Malaman Jami’o’in Najeriya ASUU ta Shiga Yajin Aiki
  • Al’ummar Karamar Hukumar Dutse Sun Bukaci Gwamnatin Jigawa Ta Yashe Madatsar Ruwa Ta Warwade
  • ’Yan ta’adda sun kashe sojoji 4 a wani sabon hari a Borno
  • Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
  • Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara
  • Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza
  • Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya