Ambaliya: Magidanta da dama sun rasa muhallinsu a Yobe
Published: 15th, August 2025 GMT
Ruwan sama kamar da bakin ƙwarya da aka yi a garin Potiskum a daren Juma’a zuwa safiyar yau Juma’a ya haifar da ambaliya, wanda ya haifar da tashin hankali ga mazauna garin.
Kamar yadda majiyar da ke garin ta shaidawa Aminiya cewa, ruwan sama kamar da bakin ƙwarya da aka fara shi tun kusan tsakar daren Alhamis ya yi sanadiyyar rugujewar gidaje da dama, inda wasu gine-gine suka ruguje ƙarƙashin ruwan.
Sakamakon ambaliyar ruwan ya sa mazauna wasu unguwanni da dama suka rasa matsugunansu inda suke hijira ya zuwa gidajen ‘yan uwa da makarantu, inda suke kokawa kan yadda iftala’in ta afku.
Wannan ambaliyar ruwa da ta faru rahotanni na nuna cewa, wasu gine-gine sun ruguje tare da rushewar maƙabarta yayin da wasu kuma suka nutse kamar yadda aka ambata a baya.
Nura Badamasi da ke unguwar bayan tsohon gidan gyaran hali wanda ɗaya ne daga cikin waɗanda abin ya shafa ya tabbatarwa da Aminiya cewa, bai fita da komai ba daga cikin gidansa sai da rigar da ke jikinsa kaɗai sauran kayayyakinsa da na iyalansa duka babu domin ambaliyar ta tafi da su da muhallinsa gaba ɗaya abin ba’a cewar komai sai dai Allah SWT ya kawo musu ɗauki.
Don haka ne ma yake roƙon gwamnatin Jihar Yobe da Ƙaramar hukumar Potiskum da su kawo musu ɗauki da kuma taimaka musu domin shawo kan matsalar ambaliyar ruwan da a kullum suke fuskantar barazana akai, kana su kuma kawo musu ɗaukin gaggawa don tallafa musu.
Unguwanni da wannan ambaliyar tafi shafa sun haɗa da: Unguwar Jigawa da Bayan tsohon gidan yari da Unguwar makafi da wasu unguwannin gabas da Kasuwa.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza
ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya October 10, 2025
Daga Birnin Sin CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa October 10, 2025
Daga Birnin Sin Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka October 10, 2025