Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi
Published: 15th, August 2025 GMT
Sojojin Nijeriya a Lokoja, tare da haɗin gwuiwar sauran hukumomin tsaro, sun kuɓutar da mutane shida da aka yi garkuwa da su a yankin Obajana na Jihar Kogi. Cikin waɗanda aka ceto akwai Sarkin Fulani na Asinwe a ƙaramar hukumar Okehi, wanda aka sace a gidansa, tare da wasu mutum huɗu da aka sace a ranar 12 ga Agusta, da kuma mutum biyu da aka sace a ranar 28 ga Yuli a Apata, Lokoja.
Kwamandan bataliya ta 12, kuma Kwamandan Operation Accord III, Birgediya Janar Kasim Sidi, wanda Commanding Officer na bataliya ta 126, Laftanar Kanal Francis Nwoffiah ya wakilta, ya ce an samu nasarar kuɓutar da fursunonin ne bayan samun sahihan bayanan leƙen asiri, inda dakarun suka bi sawun ƴan bindigar har cikin daji. Ya ce ƴan bindigar sun tsere da raunuka bayan fuskantar ƙarin ƙarfin Soji, suka bar waɗanda suka sace da kuma kayan su, ciki har da alburusai.
Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata ’Yansanda Sun Gano Gawar Ɗan Jaridar Da Aka Kashe A Jihar KogiYa ƙara da cewa, an kuɓutar da dukkan waɗanda aka sace ba tare da wani rauni ba, kuma za a haɗa su da iyalansu bayan sun sami kulawar likita. Janar Sidi ya gargaɗi ƴan ta’adda da masu garkuwa da mutane a Kogi da jihohin makwabta su tuba, in ba haka ba za su fuskanci mummunar sakamako.
Wani daga cikin waɗanda aka ceto, Sarkin Fulani na Asinwe, Malam Adamu Zage, ya gode wa Sojojin da sauran jami’an tsaro bisa jarumtar da suka nuna. Gwamnan jihar, Ahmed Usman Ododo, ya ce gwamnati ba za ta lamunci aikata laifuka a Kogi ba, tare da bayyana cewa ana ci gaba da kai farmaki kan masu aikata miyagun laifuka a jihar da kewaye.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Garkuwa Sojojin Nijeriya
এছাড়াও পড়ুন:
Sarkin Musulmi ya buƙaci gwamnonin Arewa suke saurarar ƙorafin jama’a
Sarkin Musulmi, Sa’ad Abubakar III, ya shawarci gwamnonin jihohin Arewa 19 su riƙa sauraron masu sukarsu tare da amfani da shawarwarin da ake ba su domin inganta salon mulkinsu.
Ya bayar da wannan shawara ne a ranar Litinin, yayin taron haɗin gwiwar Gwamnonin Arewa da Sarakunan Gargajiya a Kaduna.
’Yan sanda sun gano zinaren N23m bayan shekara 13 da ɓacewarsu a Borno ’Yan bindiga sun sace fasto da matarsa masu ibada a KogiSarkin Musulmi, ya ce bai kamata shugabanni su yi biris da ƙorafin jama’a ba, musamman a wannan lokaci da Arewa ke fama da matsalolin rashin tsaro, talauci da matsin tattalin arziƙi.
A cewarsa, babu wani gwamna ko shugaban ƙasa da zai nemi ƙuri’un jama’a sannan bayan ya hau mulki ya juya musu baya.
Ya nuna damuwa cewa mutane da dama na zargin gwamnonin da rashin yin aiki, alhali suna fuskantar matsin lamba.
Sarkin ya shawarce su da su rika karɓar ƙorafe-ƙorafe masu amfani tare da gyara inda ya dace, domin hakan na taimakawa wajen yanke shawara mai kyau.
Haka kuma, ya yi kira da a ƙara samun haɗin kai a tsakanin gwamnonin, inda ya ce hakan ne zai taimaka wajen inganta Arewa da daidaita ƙasa baki ɗaya.
Sarkin Musulmi ya tabbatar wa gwamnonin cewa sarakunan gargajiya na tare da su, kuma a shirye suke ba su goyon baya a kowane lokaci.
Ya kuma bayar da shawarar cewa ya kamata gwamnoni da sarakunan gargajiya su riƙa gudanar da taruka akai-akai domin tattauna matsaloli da yanke shawara tare.
A ƙarshe, ya ce sarakunan gargajiya za su ci gaba da bayar da gudummawa wajen samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Arewa da Najeriya gaba baki ɗaya.