Aminiya:
2025-11-27@23:35:54 GMT

Gwamnatin Gombe za ta ƙirƙiri sabbin ƙananan hukumomi 13

Published: 13th, August 2025 GMT

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya miƙa ƙudiri zuwa Majalisar Dokokin Jihar domin neman amincewarta a ƙirƙiri sabbin ƙananan hukumomi 13.

Gwamnan, ya bayyana cewa wannan mataki zai taimaka wa gwamnati wajen kusantar al’umma, da ayyukan raya ƙasa.

Jama’a sun koka kan rashin kammala aikin titi a Kafanchan Majalisar Kano ta dakatar da ciyaman kan zargin karkatar da taki

Sabbin ƙananan hukumomin da ake shirin ƙirƙira za su fito daga ƙananan hukumomin da ake da a jihar.

A cewar gwamnan sabbin ƙananan hukumomin za su mayar da hankali kan samar da tsaro, ilimi, kiwon lafiya, gina muhalli da sauran muhimman ayyukan jama’a musamman a yankunan karkara.

Za su kuma yi aiki tare da masarautu da shugabannin al’umma wajen tabbatar da zaman lafiya, bunƙasa ci gaba da magance matsalolin tsaro bisa tanadin dokar masarautu ta jihar.

Sabbin ƙananan hukumomin da za a ƙirƙira su ne Akko Arewa mai hedikwata a Amada, Akko Yamma mai hedikwata a Pindiga, Balanga Kudu mai hedikwata a Bambam, Billiri Yamma mai hedikwata a Tal, Dukku Arewa mai hedikwata a Malala, Funakaye Kudu mai hedikwata a Tongo.

Akwai Gombe Kudu mai hedikwata a Bolari, Kaltungo Gabas mai hedikwata a Wange, Kwami Yamma mai hedikwata a Bojude, Nafada Kudu mai hedikwata a Birin Fulani.

Sauran sun haɗa da Pero-Chonge mai hedikwata a Filiya, Yamaltu Gabas mai hedikwata a Hinna, da Yamaltu Yamma mai hedikwata a Zambuk.

Domin tabbatar da nasarar aiwatar da wannan shiri, ƙudirin ya tanadi kafa kwamiti na wucin gadi da zai jagoranci kowace ƙaramar hukuma har zuwa lokacin da za a gudanar da zaɓe.

Za a aiwatar da shirin a matakai tare da tsare-tsaren aiki, tsarin ma’aikata da kasafin kuɗi da zai tabbatar da harkokin gudanarwa.

Gwamnan, ya roƙi majalisar dokokin jihar da ta duba ƙudirin cikin gaggawa tare da amincewa da shi.

Sannan ya kira ga al’ummar jihar da su goyi bayan shirin wanda ya ce zai bunƙasa mulki da ci gaban Jihar Gombe.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamna Inuwa Majalisar Dokoki Yamma mai hedikwata a Kudu mai hedikwata a a mai hedikwata a

এছাড়াও পড়ুন:

Wata mata ta kashe ’yar shekara 7 a Ribas

Ana fargabar cewa wata mata mai suna Success ta kashe wata yarinya mai shekaru bakwai, Alicia Olajumoke, a unguwar Rumueme da ke birnin Fatakwal na Jihar Ribas.

Mazauna yankin sun shaida wa Aminiya cewa matar da ake zargin tana da kusanci da dangin mahaifiyar yarinyar, wacce ita kaɗai ce a wurin iyayenta.

El-Rufai ya koma jami’yyar haɗaka ta ADC An janye ’yan sanda 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya

Bayanai sun ce ita ma matar ta caka wa kanta wuƙa a wuya bayan kashe yarinyar, kuma bayan an garzaya da duk su biyun asibiti, likitoci suka tabbatar da cewa sun riga mu gidan gaskiya.

Lamarin wanda ya faru a ranar Talata ya ɗimauta mazauna yankin, la’akari da zargin cewa matar ta kashe yarinyar ce a gidanta bayan ta je har makarantarsu ta ɗauko ta ba tare da izinin mahaifiyarta ba.

Jami’ar hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sanda a Jihar Ribas, SP Grace Iringe-Koko, ta tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ta fitar ranar Alhamis, inda ta ce an kai gawar yarinyar ɗakin ajiye gawa domin bai wa likitoci damar kammala bincikensu na kimiyya gabanin soma nasu binciken.

“Mun ziyarci wurin da abin ya faru, mun ɗauki hotuna, kuma an garzaya da su asibiti inda aka tabbatar da mutuwarsu.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wata mata ta kashe ’yar shekara 7 a Ribas
  • El-Rufai ya koma jami’yyar haɗaka ta ADC
  • Jihar Jigawa Za Ta Rufe Karbar Kudaden Aikin Hajjin 2026 Ranar 24 Ga Watan Disamba
  • Shugaba Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Harkar Tsaro Tare da Bada Umurnin Daukar Sabbin Jami’ai
  • Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Yi Wa Yara Miliyan 1.5 Rigakafin Cutar Shan Inna
  • An buɗe wasu makarantu domin ci gaba da jarawaba a Katsina
  • Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina
  • Tsaron makarantu: ’Yan Sanda da Shugabannin Makarantu sun tsara sabbin matakai a Gombe
  • Gwamnonin Kudu Maso Yammacin Najeriya Sun Ce Lokacin Kafa Yansandan Jihohi Ya Yi