Aminiya:
2025-08-14@12:43:38 GMT

’Yan bindiga sun kashe tsohon malamin makaranta a Edo

Published: 14th, August 2025 GMT

Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kashe wani tsohon malami kuma manomi, Andrew Imuekheme, a Jihar Edo.

Lamarin ya faru ne a ranar Talata a garin Ikabigbo, da ke Masarautar Uzairue, a Ƙaramar Hukumar Etsako ta Yamma.

Allah zai kunyata masu ɗaukar nauyin ta’addanci a Zamfara — Gwamna Dauda Dalilan ƙaruwar mace-mace a hanyoyin Najeriya

Rahotanni sun ce Malam Andrew na kan hanyarsa daga gona lokacin da maharan suka tare shi, tare da ɗauke shi zuwa daji.

Wata mata da ta tsere daga hannun maharan ta koma cikin gari tare da sanar wa mafarauta, waɗanda suka fara bincike nan take.

Tuni jami’an tsaro suka umarci manoma da ke da gonaki a kusa da yankin da su koma gidajensu saboda tsaro.

Daga baya, ’yan sa-kai sun gano babur da takalman mamacin.

Bayan zurfafa bincike cikin dare suka gano gawarsa.

Sarkin garin, Cif Braimah Alegeh, ya yi Allah-wadai da kisan tare da bayyana mutanensa a matsayin masu zaman lafiya.

Ya roƙi gwamnati da jami’an tsaro su kawo musu ɗauki.

Wannan shi ne karo na uku da irin wannan kisan ke faruwa a garin.

Shekaru biyu da suka gabata, an kashe wani malamin Katolika da shugaban mafarauta.

Kakakin ’yan sandan jihar, CSP Moses Yamu, ya ce zai fitar da sanarwa daga baya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Harin ’yan fashi: An rufe Federal Poly Bauchi Bauchi

Hukumomin Kwalejin Kimiyya da Kere-kere ta Gwamnatin Tarayya sun ufe makarantar a sakamakon zanga-zangar da dalibai suka gudanar domin nuna fushinsu kan harin da ’yan fashi suka kai dakunan kwanansu.

Daliban sun tayar da tarzoma ne da sanyin safiyar Talata bayan harin ’yan fashin ya ya yi sanadiyyar jikkatar wasu dalaibai da dama, suna mazu zargin hukumomin kwalejin da kasa kare su daga abin da ya faru cikin dare.

Rahotanni since ’yan fashin sun kwace wa daliban kayayyakinsu, tare da jikkata mutum tara.

An dai ga fusatattun daliban suna gudanar da zanga-zanga a kan hanyar Bauchi zuwa Dass, inda suka daura shingen hana zirga-zirga a kofar shiga kwalejin.

’Yan sanda sun harba barkonon tsohuwa domin tarwatsa jama’a, lamarin da ya sa wasu daliban suka mayar da martani da duwatsu kafin daga bisani ’yan sanda su ci karfinsu.

Shugaban Kungiyar Dalibai (SUG) ta kwalejin, Haruna Umar, ya yi Allah-wadai da harin, inda ya bayyana shi a matsayin irinsa na farko a tarihin makarantar.

“’Yan fashin sun ji wa dalibi mai wakiltar aji daya na na matakin Difloma a fannin Kimiyyar Kwamfuta, Matta Musa rauni a kai. Wasu da suka samu raunuka an kai su Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBUTH) da ke Bauchi,” in ji shi.

Jami’in Hulda da Jama’a na kwalejin, Rabiu Wadda, ya shaida wa wakilinmu, cewa hukumar gudanarwar makarantar ta yi koqarin shawo kan lamarin kuma nan take ta rufe makarantar har zuwa wani lokaci domin hana tabarbarewar doka da oda.

Ya ce “Na kasance a makarantar tun karfe 4:00 na safe, muna kowarin shawo kan lamarin. A halin da ake ciki, ban samu shiga harabar ba.

“Yanzu, ba zan iya ba ku ainihin adadin daliban da abin ya shafa ba, amma na san an kai wasu daliban asibiti,” in ji shi.

“Hukumar gudanarwar Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta tarayya ta Bauchi, ta bayar da umarnin rufe harkokin ilimi a kwalejin,” a cewar wata sanarwa da aka rabawa jama’a a ranar Talata.

Magatakardar kwalejin, Kasimu Salihu, ya bayyana cewa wasu bata-gari sun mamaye dakin kwanan dalibai maza, inda suka kwashe kayansu tare da raunata kimanin dalibai biyu.

“Bayan wannan mummunan lamari, daliban sun fito daga babbar kogar kwalejin don nuna rashin jin dadinsu, suna masu kira ga hukumar da ta dauki matakin gaggawa, tare da duk manyan jami’an gudanarwa da ma’aikatan gudanarwa”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bello Turji bai miƙa wuya ba har yanzu — DHQ
  • Yadda Ƙananan Hukumomi Ke Yin Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe Jama’a A Kauyukan Sakkwato
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto
  • Nijeriya ta sake ƙulla alaƙar tsaro da Isra’ila
  • Harin ’yan fashi: An rufe Federal Poly Bauchi Bauchi
  • Ruwan Wutan sojan Nijeriya Ya Kashe ‘Yan Bindiga A Zamfara.
  • EFCC ta tsare tsohon Gwamnan Sakkwato Tambuwal kan zargin N189bn
  • Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi