An zabi sabuwar firaminista a Luthuania
Published: 15th, August 2025 GMT
Shugaban ƙasar Lithuania, Gitanas Nauseda, ya zabi ’yar majalisa Inga Ruginiene ta jam’iyyar Social Democrat, a matsayin firaminista, bayan Gintautas Paluckas ya yi murabus sakamakon binciken rashawa da ake gudanarwa a kansa.
Sai dai Ruginiene ta taba fuskantar suka kasancewar tana da alaka da ’yan uwa a Rasha, wadanda ta ziyarta a shekarun 2015 da 2018.
Sai dai ta ce yanzu daina kai musu ziyara, kuma ta jaddada cewa tun farko Ukraine take mara wa baya a yakin da take yi da Rasha, wadda ta kaiwa mamaya a 2022.
Majalisar dokokin ƙasar za ta amince da nadinta tare da ministocinta kafin ta kama aiki.
A makon da ya gabata ne gwamnatin Paluckas ta yi murabus, bayan jam’iyyar Democrat ta janye goyon bayan hadin gwiwar da ke kunshe da jam’iyyar populist ta Nemunas Dawn, lamarin da ya haifar da rikicin siyasa.
Hukumar kula da laifukan kudi (FNTT) ta kama ɗan uwan Paluckas a ranar Alhamis tare da wasu mutum huɗu a wani bincike kan kamfanonin da ake alaka da tsohon firaministan.
Sai dai har yanzu babu wata tuhuma da aka gabatar a kan Paluckas.
AFP
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun kashe tsohon malamin makaranta a Edo
Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kashe wani tsohon malami kuma manomi, Andrew Imuekheme, a Jihar Edo.
Lamarin ya faru ne a ranar Talata a garin Ikabigbo, da ke Masarautar Uzairue, a Ƙaramar Hukumar Etsako ta Yamma.
Allah zai kunyata masu ɗaukar nauyin ta’addanci a Zamfara — Gwamna Dauda Dalilan ƙaruwar mace-mace a hanyoyin NajeriyaRahotanni sun ce Malam Andrew na kan hanyarsa daga gona lokacin da maharan suka tare shi, tare da ɗauke shi zuwa daji.
Wata mata da ta tsere daga hannun maharan ta koma cikin gari tare da sanar wa mafarauta, waɗanda suka fara bincike nan take.
Tuni jami’an tsaro suka umarci manoma da ke da gonaki a kusa da yankin da su koma gidajensu saboda tsaro.
Daga baya, ’yan sa-kai sun gano babur da takalman mamacin.
Bayan zurfafa bincike cikin dare suka gano gawarsa.
Sarkin garin, Cif Braimah Alegeh, ya yi Allah-wadai da kisan tare da bayyana mutanensa a matsayin masu zaman lafiya.
Ya roƙi gwamnati da jami’an tsaro su kawo musu ɗauki.
Wannan shi ne karo na uku da irin wannan kisan ke faruwa a garin.
Shekaru biyu da suka gabata, an kashe wani malamin Katolika da shugaban mafarauta.
Kakakin ’yan sandan jihar, CSP Moses Yamu, ya ce zai fitar da sanarwa daga baya.