Aminiya:
2025-08-14@22:41:59 GMT

An zabi sabuwar firaminista a Luthuania

Published: 15th, August 2025 GMT

Shugaban ƙasar Lithuania, Gitanas Nauseda, ya zabi ’yar majalisa Inga Ruginiene ta jam’iyyar Social Democrat, a matsayin firaminista, bayan Gintautas Paluckas ya yi murabus sakamakon binciken rashawa da ake gudanarwa a kansa.

Sai dai Ruginiene ta taba fuskantar suka kasancewar tana da alaka da ’yan uwa a Rasha, wadanda ta ziyarta a shekarun 2015 da 2018.

Mun shirya wa zaben ciki gurbi a Kano —INEC Tinubu ya cancanci yabo kan daidaita tattalin arzikin Nijeriya —Ngozi

Sai dai ta ce yanzu daina kai musu ziyara, kuma ta jaddada cewa tun farko Ukraine take mara wa baya a yakin da take yi da Rasha, wadda ta kaiwa mamaya a 2022.

Majalisar dokokin ƙasar za ta amince da nadinta tare da ministocinta kafin ta kama aiki.

A makon da ya gabata ne gwamnatin Paluckas ta yi murabus, bayan jam’iyyar Democrat  ta janye goyon bayan hadin gwiwar da ke kunshe da jam’iyyar populist ta Nemunas Dawn, lamarin da ya haifar da rikicin siyasa.

Hukumar kula da laifukan kudi (FNTT) ta kama ɗan uwan Paluckas a ranar Alhamis tare da wasu mutum huɗu a wani bincike kan kamfanonin da ake alaka da tsohon firaministan.

Sai dai har yanzu babu wata tuhuma da aka gabatar a kan Paluckas.

AFP

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun kashe tsohon malamin makaranta a Edo

Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kashe wani tsohon malami kuma manomi, Andrew Imuekheme, a Jihar Edo.

Lamarin ya faru ne a ranar Talata a garin Ikabigbo, da ke Masarautar Uzairue, a Ƙaramar Hukumar Etsako ta Yamma.

Allah zai kunyata masu ɗaukar nauyin ta’addanci a Zamfara — Gwamna Dauda Dalilan ƙaruwar mace-mace a hanyoyin Najeriya

Rahotanni sun ce Malam Andrew na kan hanyarsa daga gona lokacin da maharan suka tare shi, tare da ɗauke shi zuwa daji.

Wata mata da ta tsere daga hannun maharan ta koma cikin gari tare da sanar wa mafarauta, waɗanda suka fara bincike nan take.

Tuni jami’an tsaro suka umarci manoma da ke da gonaki a kusa da yankin da su koma gidajensu saboda tsaro.

Daga baya, ’yan sa-kai sun gano babur da takalman mamacin.

Bayan zurfafa bincike cikin dare suka gano gawarsa.

Sarkin garin, Cif Braimah Alegeh, ya yi Allah-wadai da kisan tare da bayyana mutanensa a matsayin masu zaman lafiya.

Ya roƙi gwamnati da jami’an tsaro su kawo musu ɗauki.

Wannan shi ne karo na uku da irin wannan kisan ke faruwa a garin.

Shekaru biyu da suka gabata, an kashe wani malamin Katolika da shugaban mafarauta.

Kakakin ’yan sandan jihar, CSP Moses Yamu, ya ce zai fitar da sanarwa daga baya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe
  • ’Yan bindiga sun kashe tsohon malamin makaranta a Edo
  • ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
  • Wakilan Hamas sun isa a Alkahira don tattaunawa kan sabuwar shawarar tsagaita wuta a Gaza
  • Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello
  • Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana
  • Dasuki: Kotu ta bai wa Gwamnatin Tarayya wa’adin kammala shari’ar kuɗin makamai
  • Tinubu na amfani da EFCC ya muzguna wa ’yan adawa — Atiku
  • An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami