Allah zai kunyata masu ɗaukar nauyin ta’addanci a Zamfara — Gwamna Dauda
Published: 14th, August 2025 GMT
Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara, ya ziyarci wasu garuruwa a Ƙaramar Hukumar Kauran Namoda, bayan jerin hare-haren ’yan bindiga da suka yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama.
Gwamnan, ya la’anci kisan gillar, tare da bayyana shi a matsayin marasa imani, kuma Allah zai fallasa su ya kunyata su.
Majalisar Zartaswa ta dakatar da ƙirƙirar sabbin manyan makarantu a Nijeriya Tinubu zai tafi ziyarar ƙasashe 3A ranar Laraba, ya ziyarci ƙauyuka biyar da abin ya fi shafa; Banga, Sakajiki, Kuryar Madaro, Maguru, da Tambarawa, inda mutane da dama suka rasa ’yan uwansu.
Bayan samun labarin hare-haren, nan da nan ya tura mataimakinsa ya je ya jajanta wa mutanen da abin ya shafa.
Bayan dawowarsa Gusau, ya je da kansa ya duba ɓarnar da aka yi tare da yi wa iyalan mamatan ta’aziyya.
Ya bayyana maharan a matsayin maƙiyan zaman lafiya da ke son haifar da tsoro da rikice-rikice, sannan ya roƙi jama’a su ci gaba da addu’a don kawo ƙarshen aikata laifuka a jihar.
Gwamnan, ya yi alƙawarin ƙara ƙaimi wajen yaƙi da ’yan bindiga ta hanyar amfani da sabbin dabaru da ƙarfafa haɗin gwiwa.
Sarkin Kauran Namoda, Dakta Sunusi Ahmad, ya yaba wa gwamnan bisa ziyarar da ya kai, inda ya bayyana cewa hakan ya ƙarfafa guiwar mutanen yankin.
Haka kuma, Gwamna Lawal, ya sanar da shirin inganta rayuwar jama’a ta hanyar gyaran hanyoyi, samar da wutar lantarki, ruwan sha, da inganta sadarwar wayar salula a yankin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Gwamna Dauda hare hare Zamfara
এছাড়াও পড়ুন:
Allah Ya yi wa Sheikh Dahiru Bauchi rasuwa
Fitaccen malamin addinin Musulunci nan daga Jihar Bauchi, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya rasu.
Ɗansa, Sayyadi Ali Dahiru Usman Bauchi ne, ya tabbatar wa Aminiya rasuwar malamin.
Juyin mulki ya rutsa da Jonathan a Guinea-Bissau Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban AmurkaYa ce sun karɓi wannan ƙaddara tare da gode wa Allah bisa rayuwar da malamin ya yi.
“Tabbas Sheikh ya koma ga Mahaliccinsa. Daga Allah muke, kuma gare Shi za mu koma,” in ji Sayyadi.
“Lokacin Sheikh ya yi. Mun gode wa Allah Maɗaukaki. Ya bai wa Sheikh tsawon rai, kuma rayuwarsa ta yi kyau. Alhamdulillah,” in ji shi.
Sayyadi, ya ce zuwa yanzu ba su yanke inda za a yi jana’izar malamin ba.