An kama ’yan daba 288 yayin zaɓen cike gurbi a Kano
Published: 16th, August 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, ta kama mutum 288 da ake zargin ’yan daba ne a lokacin zaɓen cike gurbi da aka gudanar a jihar.
Kakakin rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce an kama mutanen da makamai masu hatsari, ciki har da bindigogi ƙirar gida, wuƙaƙe da adduna.
Zaɓen cike gurbi: An kama ’yan daba 100 a Bagwai — INEC HOTUNA: Yadda zaɓen cike gurbi ke gudana a sassan NajeriyaYa bayyana cewa an yi wannan kamen ne domin tabbatar da zaman lafiya yayin gudanar da zaɓen.
Ya ce suna ci gaba da bincike, kuma duk wanda aka tabbatar na da laifi za a gurfanar da shi a kotu.
Kiyawa, ya kuma tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da tabbatar da doka da oda.
A gefe guda kuma, ya yi gargaɗin cewa rundunar ba za ra lamunci tashin hankali ko rikicin siyasa a Kano ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda yan daba Zaɓen Cike Gurbi zaɓen cike gurbi
এছাড়াও পড়ুন:
Mun shirya wa zaben ciki gurbi a Kano —INEC
Hukumar Zabe ta Kasa INEC ta sanar da kammala duk shirye-shiryen zaben ciki gurbi a kananan hukumomin Bagwai, Shanono da kuma Ghari (Kunchi) da ke Kano wanda za a gudanar a ranar Asabar.
Kwamishinan INEC a Kano, Zango Abdu, wanda ya tabbatar da hakan a yayin taron manema labarai, ya ce an riga an raba kayan zabe masu muhimmanci da wadanda ba su da muhimmanci a kananan hukumomi da abin ya shafa.
Tinubu ya cancanci yabo kan daidaita tattalin arzikin Nijeriya —Ngozi An kama Mai Unguwa kan yi wa yarinya fyaɗe a GombeYa ce, “Tun kusan makonni uku da suka gabata aka riga da tura kayayyakin da ba su da muhimmanci wadanda aka tanadar wa mazabu da rumfunan zabe.
“Yanzu haka kayan zaben masu muhimmanci sun iso, kuma za a tura su kananan hukumomi yau da yamma tare da wakilan jam’iyyun siyasa da jami’an tsaro.”
Ya kuma bayyana cewa an kammala horas da dukkan ma’aikatan wucin gadi kuma an tura su wuraren da za su yi aikin, yayin da jami’an tsaro karkashin kwamitin tsaro na haɗin gwiwa sun ba da tabbacin duk wasu tanade-tanade da suka kamata.
Da yake karin haske, Zango ya ce duk na’urorin BVAS wadanda za a yi amfani da su wajen tantance masu kada kuri’a su ma an tanade su tare da tabbatar da nagartarsu.
Ya jaddada kudirin INEC na gudanar da sahihin zabe na gaskiya da adalci, inda ya ce hukumar za ta sanar da wanda ya yi nasara ne kawai bisa kuri’un da aka kada.
“Babbar damuwarmu a yanzu ita ce ’yan siyasa. Amma dai su ma sun rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya, sun kuma shaida mana za su yi zabe cikin lumana. Saboda kwanciyar hankali ne kawai zai ba ’yan kasa ’yancin zaben shugabanninsu,” in ji shi.
Dangane da yadda za a tattara sakamako, Zango ya ce za a bayyana sakamakon akwatuna a duk rumfunan zabe kafin a kai shi cibiyoyin tattarawa na mazabu.
Ana iya tuna cewa, tun a watan Yunin da ya gabata ne INEC ta ayyana 16 ga watan Agustan bana, a matsayin ranar da za a gudanar da zaben cike gurbi a kananan hukumomin na Kano.
Za a gudanar da zaben ne sakamakon rasuwar dan Majalisar Tarayya mai wakiltar Bagwai da Shonono, Halilu Ibrahim Kundila na jam’iyyar APC, wanda ya riga mu gidan gaskiya a ranar 6 ga watan Afrilun 2024.
Sai dai kuma za a gudanar da zaben cike gurbin ne a Karamar Hukumar Ghari — wadda a baya ake kira Kunc— a rumfunan zabe 10 da masu kada kuria 5200 bisa umarnin kotu.