Aminiya:
2025-08-13@21:54:23 GMT

Majalisar Zartaswa ta dakatar da ƙirƙirar sabbin manyan makarantu a Nijeriya

Published: 14th, August 2025 GMT

Gwamnatin Tarayya ta yanke shawarar dakatar da ƙirƙirar sabbin manyan makarantu har na tsawon shekaru bakwai masu zuwa a duk faɗin Nijeriya.

Dakatarwar ta shafi ƙirƙirar sabbin jami’o’i, kwalejojin ilimi da kuma kwalejojin kimiyya da fasaha na tarayya kamar yadda Majalisar Zartarwa ta Tarayya (FEC) ta tabbatar.

Tinubu zai tafi ziyarar ƙasashe 3 An naɗa sabon Sarkin Alkaleri a Bauchi

Wannan mataki, a cewar Ministan Ilimi Dakta Olatunji Alausa, an ɗauke shi ne domin rage yawan makarantun da ba a amfani da su yadda ya kamata, lamarin da zai ba da damar mayar da hankali wajen gyara da inganta waɗanda ake da su yanzu.

Da yake zantawa da manema labarai bayan taron na FEC a fadar shugaban ƙasa ranar Laraba, Alausa ya bayyana cewa binciken da aka gudanar ya nuna cewa samun damar shiga jami’a a Nijeriya “ba ita ce matsala ba” a halin yanzu.

Sai dai ministan ya ce yawan kafa makarantu marasa inganci da maimaita su ne ke jawo matsaloli irin su gine-ginen da ba su dace ba, ƙarancin ma’aikata, da raguwar ɗalibai.

Ya ce “akwai wasu jami’o’in gwamnatin tarayya da ke aiki ƙasa da yadda ya dace da su, inda wasu ke da ɗalibai da ba su haura 2,000 ba. A wata jami’a ma, ma’aikata 1,200 ne ke kula da ɗalibai ƙasa da 800.

“Wannan asarar kuɗin gwamnati ne, saboda a yanzu muna da jami’o’i 199, amma ƙasa da ɗalibai 100 ne suka nemi shiga kowace ta hanyar JAMB. Har ma akwai jami’o’i 34 da babu wanda ya nema gaba ɗaya,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Zartarwa Majalisar Zartaswa ta Tarayya manyan makarantu

এছাড়াও পড়ুন:

An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami

Rijistaran makarantar, Alhaji Kasimu Salihu, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa an rufe makaranta kuma an umarci ɗalibai su bar harabar makarantar har sai an bayar da sanarwa ta gaba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7
  • Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati
  • Majalisar Dokokin Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukumar Rano Na Tsawon Watanni Uku
  • Shugaban Tinubu Ya Rantsar Da Farfesa Dakas James Shugaban Hukumar Gyaran Dokoki Ta Kasa
  • Majalisar Kano ta dakatar da ciyaman kan zargin karkatar da taki
  • Wani Bangaren Majalisar Dokokin Jihar Zamfara Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Da Ta Karbe Mulkin Jihar
  • ‘Yan Nijeriya Miliyan 14 Sun Yi Bikin Murnar Karɓar Kyautar N23m Daga Bankin STANBIC IBTC
  • Babban Sakataren Majalisar Kolin Tsaron Kasar Iran Ya Ce: ‘Yan Gwagwarmaya Sun San Abubuwan Da Suka Dace
  • An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami