Mutum 12 sun rasu, 5 sun jikkata a hatsarin mota a Kano
Published: 15th, August 2025 GMT
Mutum 12 sun rasu yayin da wasu biyar suka jikkata a wani hatsarin mota da ya auku a ƙauyen Samawa, da ke Ƙaramar Hukumar Garun Malam a Jihar Kano.
Hatsarin ya faru ne da misalin ƙarfe 2:40 na daren ranar Juma’a a kan titin Zariya zuw Kano.
Ambaliya: Magidanta da dama sun rasa muhallinsu a Yobe An sake ceto matafiya 10 da aka sace a KogiTirela ƙirar DAF mai lambar KMC 931 ZE, wadda ke ɗauke da kaya da fasinjoji ta yi hatsarin.
Hukumar Kiyaye Haɗura ta Ƙasa (FRSC) reshen Kano, ta ce bincike ya nuna cewar matsala ce ta haddasa hatsarin.
Tirelar na ɗauke da mutum 19, wanda 12 daga cikinsu suka rasu, sai wasu biyar da suka jikkata.
Mutum biyu ne kacal suka tsallake rijiya da baya ba tare da sun ji rauni ba.
An kai waɗanda suka jikkata Babban Asibitin Garin Kura, sannan an kai gawarwakin waɗanda suka rasu Asibitin Nasarawa.
Kwamandan FRSC na Kano, M.B. Bature, ya ziyarci wajen da hatsarin ya auku, inda ya zargi lodin kaya masu yawa da rashin bin dokokin hanya da haddasa hatsarin.
Ya gargaɗi direbobi kan haɗa kaya, dabbobi da fasinjoji a mota ɗaya.
A madadin Babban Kwamandan FRSC, Dauda Ali Biu, ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda suka rasu, tare da yi wa waɗanda suka jikkata fatan samun sauƙi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: hatsarin mota waɗanda suka
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba
Ya bayyana cewa an riga an hada wadanda aka ceto da iyalansu, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike da aikin ceton domin gano wadanda suka aikata laifin da kuma kubutar da sauran wadanda ake tsare da su, idan suna nan.
A halin da ake ciki kuma, kwamandan Runduna ta 6 ta Sojan Nijeriya, Birgediya Janar Kingsley Chidiebere Uwa, ya yaba da saurin daukar mataki da hadin kai tsakanin sojoji da ‘yansanda wanda ya kai ga nasarar aikin ceton.
Ya sake jaddada kudirin rundunar wajen tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a a Jihar Taraba.
Sai dai, ya bukaci jama’a da su ci gaba da bai wa sojoji da sauran hukumomin tsaro goyon baya ta hanyar samar da sahihan bayanai a kan lokaci domin taimaka wa a ayyukan tsaro da ake gudanarwa a fadin jihar.
A wani labari mai nasaba da haka, Kungiyar Matan Sojoji da ‘Yansanda (DEPOWA) ta yaba da jajircewa da sadaukarwar dakarun rundunonin sojojin Nijeriya da sauran jami’an tsaro, wadanda ke ci gaba da sadaukar da rayuwarsu domin kare kasar.
Kungiyar ta kuma yi addu’a ga Allah domin kare mazajensu, wadanda ke kwana suna tashi a kan bakin aiki domin tabbatar da tsaron ‘yan Nijeriya.
Shugabar kungiyar DEPOWA, kuma matar Babban Hafsan Tsaro na Kasa (CDS), Mrs. Oghogho Musa, ta bayyana wannan godiya tare da yin addu’o’i a birnin Abuja yayin gudanar da wasan motsa jiki na rawa (Dance Aerobics Edercise) da aka gudanar a makarantar DEPOWA da ke sansanin Mogadishu.
Shugabar DEPOWA ta kuma jaddada kudirin kungiyar na gudanar da yakin addu’a da godiya na tsawon shekara guda ga dakarun da ke bakin daga, domin nuna yabo da godiya ga jajircewarsu wajen kare kasar Nijeriya, duk da hadarin da ke tattare da aikin.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA