An kama manyan shugabannin ’yan ta’addan ƙungiyar Ansaru — Ribadu
Published: 17th, August 2025 GMT
Jami’an tsaro sun kama manyan shugabannin ƙungiyar ’yan ta’adda ta Ansaru, ciki har da shugaban ƙungiyar, Mahmud Muhammad Usman wanda aka fi sani da Abu Baraa.
An daɗe ana zarginsa da kitsa hare-hare masu yawa a Najeriya.
’Yan sanda sun kama matashin da ya yi garkuwa da kansa a Ondo Majalisar dokokin Gombe ta fara duba ƙudirin ƙirƙirar sabbin gundumomi 13Mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu ne, ya tabbatar da kamen a wani taron manema labarai da ya gudanar a Abuja, a ranar Asabar.
Ya bayyana cewa an cafke Abu Baraa a watan Yuli bayan shafe tsawon watanni ana bin diddiginsa.
Haka kuma an kama wani shugaban ƙungiyar, mai suna Abubakar Abba.
Ribadu, ya ce wannan nasara babban ci gaba ne a yaƙi da ƙungiyar Ansaru, wacce ta ɓalle daga tsagin Boko Haram a shekarar 2012.
Duk da cewa a farko ta bayyana kanta a matsayin “ƙungiya mai tausayin jama’a” daga baya ta zama mai aikata mummunan ayyukan ta’addanci.
Ta kai wa sojoji, fararen hula da kuma gine-ginen gwamnati hare-hare.
Tsawon shekaru, ƙungiyar ta samar wa kanta maɓoya a cikin birane da kuma dazuka, musamman a kusa da yankin Kainji da ke tsakanin Jihohin Neja da Kwara har zuwa Jamhuriyar Benin.
A cewar Ribadu, Abu Baraa shi ne ke da alhakin shirya ayyukan ta’addanci a sassan Najeriya da kuma sace mutane da fashi don samun kuɗaɗen da suke amfani da su wajen aikata ta’addanci.
Mataimakinsa, Mahmud al-Nigeri wanda aka fi sani da Mallam Mahmuda, ya samu horo a ƙasar Libya tsakanin shekarar 2013 zuwa 2015, inda ya ƙware wajen amfani da makamai da kuma haɗa bama-bamai.
Ribadu, ya danganta su da wasu manyan laifuka da suka haɗa da ɓalle gidan yarin Kuje a 2022, da harin da suka kai wajen haƙar ‘uranium’ a Jamhuriyar Nijar.
Har ila yau, suna da hannu a sace injiniyan Faransa Francis Collomp a 2013, da kuma sace manyan mutane kamar Alhaji Musa Umar Uba na Daura a 2019 da Sarkin Wawa na Jihar Neja.
Ribadu, ya ce wannan kamen babban nasara ce a ƙoƙarin Najeriya na kawar da ta’addanci.
Ya ƙara da cewa jami’an tsaro sun samu muhimman bayanai daga hannunsu, kuma ana bincike a kansu domin kawo ƙarshen ƙungiyar.
Ya jinjina wa dakarun soja da sauran hukumomin tsaro bisa jajircewarsu, inda ya bayyana wannan babban ci gaba ne wajen rushe ƙungiyar Ansaru gaba ɗaya.
Ministan Watsa Labarai, Mohammed Idris, ya roƙi ’yan Najeriya da su ci gaba da bai wa jami’an tsaro bayanai masu amfani domin kawo ƙarshen ta’addanci, tare da tabbatar da tsaro da ci gaban tattalin arziƙi.
Wannan nasara na zuwa ne bayan shekara tara da kama wani tsohon shugaban Ansaru, Khalid al-Barnawi, a shekarar 2016.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan ta adda Ansaru Boko Haram hare hare Ƙungiya
এছাড়াও পড়ুন:
Isra’ila Tana Ci Gaba Da Rushe Gidaje A Yankin Gaza
Da safiyar Yau Laraba ne sojojin Haramtacciyar kasar Isra’ila su ka kai hare-hare a yankuna daban-daban na zirin Gaza, tare da rushe gidaje da dama. Sojojin mamayar sun yi amfani da jiragen sama marasa matuki da kuma tankokin yaki domin rushe gidajen. A arewacin Gaza da gabashin Jabaliya sojojin na mamaya sun yi amfani da manyan bindigogi akan gidajen fararen hular. A unguwar “Tuffah” ma an ga yadda sojojin mamayar su ka aike da jiragen yaki marasa matuki.A can kudancin Gaza kuwa jiragen yakin Haramtacciyar Kasar Isra’ila ne su ka kai hare-hare akan barin Bani-Suhaila a gabashin Khan-Yunus,a lokaci daya kuma manyan bingigoginsu su ka bude wuta akan iyaka.
Tun bayan da aka tsagaita wutar yaki a cikin watan Oktoba ne, Sojojin mamayar Haramtacciyar Kasar Isra’ilan suke ci gaba da kai hare-hare akan Gaza ba tare da kakkautawa ba. Daga tsagaita wutar zuwa yanzu adadin Falasdinawan da su ka yi shahada a sanadiyyar hare-haren na ‘yan sahayoniya sun haura 300.
Hukumar agaji a yankin na Gaza ta yi gargadi akan cincirindon ‘yan hijira da suke rayuwa a cikin hemomin da babu kayan da rayuwa take da bukatuwa da su domin ci gaba. Ruwan sama yana ci gaba da sauka a yankuna mabanbanta na Gaza da sanyi yake karuwa ba tare da samar da na’urorin dumama hemomin ba.
Kakakin kungiyar agaji a Gaza Mahmud Basal ya ce; Suna samun dubban koke daga Gaza cewa hemomin da mutane suke rayuwa a ciki ba su dace da rayuwa ba ko kadan.Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Uganda: An Kama Fiye Da ‘Yan Hamayyar Siyasa 300 A Lokacin Yakin Neman Zabe November 26, 2025 Reuters: Kungiyar Likitoci Ba Da Iyaka Ba Ta Fice Daga Asibitin Darfur Bayan Bude Wa Ma’aikatanta Wuta November 26, 2025 Shugaban Iran: Kasuwar jarin cikin gida sirrin nasarorin gwamnati na tattalin arziki November 26, 2025 Larijani: Hadin gwiwar Iran da Pakistan na taimaka wa zaman lafiya a yankin November 26, 2025 Al-Houthi ya yi ta’aziyyar shahadar babban kwamanda na Hizbullah November 26, 2025 UNIFIL: Isra’ila tana sabawa wa kudurorin MDD a cikin Lebanon November 26, 2025 Matsalolin Tsaro A Yankunan Bakin Ruwa A Kasar Siriya Ya Kai Ga Zanga-Zangar Lumana November 26, 2025 Aljeriya Ta Bukaci Kasashen Duniya Su Dauki Mataki Don Kawo Karshen Ta’asan HKI A Yankin Asiya Ta Kudu November 26, 2025 Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yabawa Pakistan Saboda Goyon Bayanta November 26, 2025 EU da AU na taro kan diyya ga laifukan mulkin mallaka da cinikin bayi November 25, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci