Tun Farko tawagar gwamnatin ta Isa fadar hakimin Barnawa domin isar da sakon ta’aziyyar gwamnatin jihar kaduna na rashin matashi inda suka tabbatar wa da Hakimin cewa gwamnatin jihar kaduna zatayi duk Mai yiwuwa wajen ganin anyiwa matashi Abubakar adalci da kuma gano dalilin mutuwarsa.

 

Hakazalika, tawagar gwamnan sun Kai ziyarar jaje gidan mamacin domin jajantawa iyayensa da ‘yan uwansa .

 

“kwamishinan ya Kara da cewa ‘Mai girma gwamna Uba Sani Yaso yazo da kansa amma bisa wasu abubuwa da suka bijiro hakan ya sanya ya wakilto mu saboda haka gwamna ya kadu matuka da samun labarin rasuwar Abubakar”.

 

Maiyaki, yace domin ganin an dakile matsalar yawaitar tu’ammali da muyagun kwayoyi, gwamnatin jihar Kaduna ta Kafa wani kwamitin hadin gwiwa na jami’an tsaro yaki da masu sha da fataucin muyagun kwayoyi a jihar.

 

Hakazalika, ya bukaci daukacin alummar jihar musamman matasa da su kaucewa tu’ammali da muyagun kwayoyi domin Kara samum zaman lafiya a fadin jihar baki daya.

 

Akan, yayi Kira ga iyaye da matasa da su baiwa jami’an tsaro goyon bayan da suka kamata wajen dakile matsalar shaye-shayen muyagun kwayoyi.

 

Ya kuma jinjinawa kokarin Hakimin Barnawa Alhaji Kabiru Zubairu na Kara hada kan al’umma da wajen tabbatar da zaman lafiya ya Kara sanuwa a garin Barnawa Dama jihar Kaduna baki daya.

 

A nasa jawabin Kwanishinan Ma’aikatar tsaro da harkikin cikin gida na jihar kaduna Barista Suleman Shu’aibu ( SAN) yace zaman lafiya da Samar da tsaro yana daga cikin manyan kudurorin gwamna Uba Sani inda ya bayar da tabbacin cewa zasu ci gaba da duk Mai yiwuwa wajen kare rayuka da dukuyoyin alummar jihar Baki daya.

 

Akan hakan, yayi Kira ga alummar jihar da su ci gaba da baiwa jami’an tsaro goyon bayan da suka kamata wajen ganin an magance matsalar bata gari Wanda hakan zai tqimakawa kokarin gwamnati na kara Samar da ayyukan ci gaba a ciki da wajen jihar.

 

Da yake nasa jawabin hakimin Barnawa kuma Madaucin Arewan Zazzau Alhaji Kabiru Zubairu, yace babu abunda da zasu cewa gwamnatin jihar kaduna sai Fatan alkhairi da samun nasara.

 

Yace alummar Barnawa zasu tabbatar da cewa su ci gaba da marawa gwamnatin Uba Sani baya domin ci gaba da aiwatar da ayyukan da takeyi na ci ga.

 

Anasa jawabin kwamishinan da lamuran cikin gida Barista Suleiman Shu’aibu ( SAN) yace gwamnatin jihar Kaduna bata ji dadin abinda da faru ba inda lamarin ya faru ne bisa kuskure inda Yayi addu’ar Allah ya gafartawa mamacin.

 

A nasa jawabin hakimin Barnawa Alhaji Kabiru Zubairu ( Badauchin Arewan Zazzau) yace tun lokacin da lamarin ya faru jami’an tsaro sun bayar da gudummawa wajen ganin an samu zaman lafiya.

 

‘Wannan yaro da ya rasu jika ne a wurina Saboda ‘ya ta ce ta haife shi saboda haka muna da tabbacin cewa yayi shahada ne. Wannan mataki da gwamnan jihar Kaduna ya dauka na kawo mana gaisuwa bazamu manta da shi saboda ya karrrama mu kwarai da gaske Kuma.

 

Suma iyayen mamacin sun nuna Jin dadinsu da irin matakin da gwamnatin jihar kaduna ta dauka na aiwatar da bincike abin a yaba ne.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: gwamnatin jihar Kaduna gwamnatin jihar kaduna muyagun kwayoyi jami an tsaro zaman lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Bago Ya Yabawa Tinubu Kan Kama Shugaban Kungiyar Ta’addanci A Neja

Gwamna Mohammed Umar Bago na jihar Neja, ya yaba wa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu kan kama Abubakar Abba, jagoran kungiyar Mahmuda, daya daga cikin manyan kungiyoyin ta’addanci da hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta yi a Najeriya.

 

An ce an kama shi ne a Wawa da ke karamar hukumar Borgu ta Jihar Neja inda aka kai shi Abuja domin ci gaba da bincike.

 

Gwamna Umar Bago ya bayyana matakin a matsayin nuni da irin jajircewar da shugaba Bola Ahmed Tinubu ke yi na tabbatar da tsaro da walwalar ‘yan Nijeriya.

 

Gwamnan wanda ya yi magana ta bakin babban sakataren yada labaran sa, Bologi Ibrahim, ya ce, “Eh gaskiya ne, zan iya tabbatar da cewa hukumar tsaron farin kaya ta DSS ta kama shugaban kungiyar Mahmuda da ke daya daga cikin kungiyoyin ta’addanci a yammacin Afirka, Abubakar Abba, wanda jami’an tsaron farin kaya DSS suka kama shi da ransa.

 

“Wannan babbar nasara ce a gare mu a matsayinmu na jama’a da kuma gwamnati, kuma Shugaba Tinubu ya cancanci a yaba masa kan wannan labari mai ban sha’awa, yana mai jaddada cewa “Kamun Abba ya nuna cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya jajirce wajen kawo karshen rashin tsaro da kuma inganta rayuwar ‘yan Nijeriya. In ji Gwamna Bago.

 

Gwamnan ya yi alkawarin cewa gwamnatin jihar Neja za ta ci gaba da hada kai da gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro domin ganin an dakile ta’addanci a jihar Neja da Najeriya.

 

ALIYU LAWAL.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Cire Tallafin Mai Ya Taimaka Mana Wajen Aiwatar da Ayyuka, In Ji Gwamna Mbah
  • Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe
  • An kama mai babur ɗauke da ƙoƙunan kan mutane a Ogun
  • ’Yan sanda sun kama matashi kan zargin aikata fashi a Gombe
  • Jama’a sun koka kan rashin kammala aikin titi a Kafanchan
  • Gwamna Namadi Ya Yaba Wa Kungiyar NBA Bisa Inganta Manufofi Da Ka’idojin Aikin Lauya
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe Jama’a A Kauyukan Sakkwato
  • Wani Bangaren Majalisar Dokokin Jihar Zamfara Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Da Ta Karbe Mulkin Jihar
  • Gwamna Bago Ya Yabawa Tinubu Kan Kama Shugaban Kungiyar Ta’addanci A Neja