Gwamna Zulum Ya Ƙaddamar Da Aikin Gina Titi Da Gadar Sama Ta Huɗu A Borno
Published: 23rd, April 2025 GMT
A jawabin Gwamna Zulum wajen kaddamar da aikin titin, ya ce, “A ci gaba da tsarinmu na sabunta birane, a yau mun kaddamar da gina titi mai tsawon kilomita 7.1 daga tashar borno Express zuwa Molai, hadi da karin ginin gadar sama ta hudu.
“Abin da muke da burin aiwatar wa, shi ne ba don kawai kyawawan ayyuka ba, har ma don daukar nauyin ci gaban al’ummar Maiduguri, kuma ya zama dole mu fadada birnin Maiduguri.
Gwamna Zulum ya yi kira ga yan kwangilar su tabbatar da bin ka’idojin inganci da kuma kammala aikin a cikin lokacin da aka kayyade.
“Za a kammala aikin cikin watanni goma, an bayar da kwangilar kan naira biliyan 16, kuma mun biya kashi 50% na wannan adadin kudin. Don haka, muna kira ga yan kwangilar cewa, ba su da wani uzuri na bata lokacin aikin. Mun kuma ajiye sauran Naira biliyan 8, za a biya a lokacin da aikin ya kammala.” In ji Zulum.
A nashi bangaren, Kwamishinan Ayyuka da Gidaje a jihar borno, Injiniya Mustapha Gubio, ya bayyana cewa, gadar saman za ta hada sabuwar hanyar ta bangarorin biyu na kogin Ngada-bul.
Kwamishinan ya tabbatar da cewa ma’aikatar za ta sa ido kan ayyukan, tare da tabbatar da bin dukkan ka’idojin kwangila.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Nijeriya Na Ke Yi Wa Biyayya Ba Wani Ko Jam’iyya Ba – El-Rufai
“Lokacin da abubuwa suka fara lalacewa a lokacin shugaba Buhari, na fito na faɗi gaskiya. Lokacin da tsarin sauya fasalin Naira ya jefa jama’a cikin wahala, na ƙalubalanci gwamnati duk da cewa jam’iyyar APC ce ke kan mulki. Na fi biyayya ga Nijeriya fiye da kowane mutum,” in ji shi.
El-Rufai ya ƙaryata jita-jitar cewa fushinsa da gwamnatin Shugaba Tinubu ne ya sa ya fice daga APC.
Ya ce yana da shekaru 65, kuma babu wani abu da ya rage masa a siyasa da zai nema, sai dai kawai yana jin cewa matsalolin Nijeriya sun yi tsanani sosai wanda ba zai zauna ya yu shiru ba.
“Zan iya yin ritaya cikin kwanciyar hankali, amma Nijeriya na fuskantar babbar barazana. Wannan ba don kaina ba ne – don ceton ƙasa ne,” in ji shi.
Ya kuma bayyana cewa dole a zaɓi shugaban ƙasa mai nagarta da hangen nesa, ba wai kawai din ya fito daga wata jiha ba.
“Matsalolin da muke fuskanta sun fi girman la’akari da inda mutum ya fito. Muna buƙatar shugabanni masu hangen nesa da ƙwarewa don gyara Nijeriya,” ya bayyana.
Da yake magana kan sauya sheƙar wasu ‘yan siyasa zuwa APC, El-Rufai ya ce jam’iyyar SDP tana mayar da hankali ne kan gina goyon baya daga jama’a, ba wai kawai neman manyan ‘yan siyasa ba.
“Gwamna ɗaya yana da ƙuri’a ɗaya ne kawai. Jama’a ne ke yin zaɓe, ba manyan ‘yan siyasa ba,” ya jaddada.
A ƙarshe, El-Rufai ya ce tafiyar SDP tana ci gaba da karɓuwa a dukkanin sassan Nijeriya, ba a yankuna kaɗan kaɗai ba.
“Muna ci gaba da gina goyon baya a faɗin ƙasar nan. Aikin gina ƙasa yana faruwa ne a tsakanin talakawa, ba kawai a kafafen yaɗa labarai ba,” in ji shi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp