A farkon wannan shekarar da ta gabata, Jaridar LEADERSHIP ta ruwaito Ministan Sufurin Ma’aikatar Jiragen Sama Festus Keyamo, a wani taro ya bai wa kungiyoyin na Sufurin Jiragen Sama tabbacin cewa, Gwamnatin Tarayya za ta tabbatar da bi ka’ida wajen sayar da hannun jarin Tashoshin Jiragen Saman kasa.

Keyamo ya kuma bai wa shugabannin kungiyoyin tabacin cewa, suma a sanya kan batun na yarjejeniyar ta sayar da hannun jarin Tashoshin Jiragen Saman.

Kazalika, ba su tabbacin cewa, zai umarci hadiminsa domin ya ci gaba da sanar da shugabannin kungiyoyin kan abinda ke tafiya game da yarjejeniyar.

Sai dai, a jawabin da shuwagabbin kungiyar da kuma na ma’aikatan suka gabatar a wani babban taronsu a shalakwar Tashar Jiragen Sama da ke a jihar Legas, sun soki Ministan Sufurin Ma’aikatar Jiragen Sama Festus Keyamo, bisa zagaye shugabannin kungiyoyin kan batun na jarjejeniyar.

A jawabinsa shugaban kungiyar ma’aikatan zirga-zirga ta jiragen sama na kasa NUATE Kwamarade Ben Nnabue ya yi kira da sake sabon lale kan batun na yarjeniyar musamman domin a bai wa sauran masu ra’ayin shiga cikin yarjejeniyar.

“Ya kamata a sake faro yarjejeniyar tun daga farkonta, domin a bai wa sauran ‘yan Nijeriya damar shiga cikin yarjejeniyar,”Inji Shugaban.

Nnabue ya ci gaba da cewa, a matsayinsu na shuwagabannin kungiyoyin sam ba su da wata masaniya game da wannan yarjejiniyar da da Gwamnatin ta kulla.

Ya kara da cewa, hatta shuwagabannin kungiyoyin kwadago ba a sanar da su, game da yarjejiniyar ba, amma sai kawai muka ji, Ministan Sufurin Ma’aikatar Jiragen Sama Festus Keyamo, sanar da cewa, Majalisar Zartwar kasar ta amince da wannan yarjejeniyar, musamman ta Tashar Jirgin Sama na jihar Enugu.

“Muna son mu sanar da duniya cewa, dole kafin a gudanar da duk wata yarjejniya a fara tattaunawa da shuwagabbin kungiyoyin kwadago tukunna, ” A cewar Kwamarade Ben.

Ya sanar da cewa, hanyoyin da ake bi na gudanar da wannan yarjejeniyar, cike take da kura-kurai domin ba mu da wata masaniya ko an bayar da talla ga manyan Jaridun kasar nan kan batun na yarjeniyar.

“Tashoshin Jiragen Sama na kasar nan, mallakin ‘yan Nijeriya, a saboda haka ba za ta sabu kawai a cikin dare daya mu ji an yanke shawarar cewa, akwai wasu ‘yan lele da ake so su kadai a yi yarjejeniyar da sub a, domin kamata ya yi ba bar abin a bude domin suma ‘yan kasar, su gyada ta su sa’ar, a saboda haka, muna bukatar a soke wannan yarjejniyar har sai idan an bi ka’idar da ta dace, “ Inji shugaban.

Shi ma a na sa bangaren shugaban kungiyar kwarru ta ANAP Kwamarade Alale Adedayo, ya yi tir da hanyoyin da Ministan ya bi domin yin wannan yarjejeniyar ba tare da janyo shugabannin kungoyoyin ba kamar yadda ya yi masu alkwari a baya.

Kwamarade Adedayo ya bukaci da sake sabon lale kan batun wannan yarjejeniyar, musamman domin a tabbatar da an bi ka’aida da kuma yin gaskiya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Jirage wannan yarjejeniyar Jiragen Sama

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe

A cewarta, shirin ya taimaka wajen noman shinkafa da ta kai kimanin tan 99,452, wacce kuma kudinta ya kai kimanin Naira biliyan 13.527 tare kuma da noman rogo da ya kai kimanin tan 87,237, wanda kudinsa ya kai Naira biliyan 3.925, musamman domin a kara samar da wadataccen abinci da kuma kara bunkasa fannin tattalin arzikin jihar.

 

Sai dai, ta bayyana cewa; har yanzu a jihar ba a samar da wani cikakken tsari a hukumance ba, a kan tsarin na shirin na CAF wanda hakan ke haifar wa da shirin koma baya a jihar.

 

Ta yi kira ga sauran masu ruwa da tsaki a fannin bunkasa aikin noma, domin samun riba a jihar da su bayar da hadin kai wajen shiga cikin tsarin na CAF, musamman a bangaren noman shinkafa da rogo da sauran amfanin gona.

 

Kazalika, ta bukaci mahukunta a jihar da su samar da tsari a hukumance, musamman na dogon zango domin ci gaba da samar da wadataccen abinci a fadin jihar baki-daya.

 

Shi ma a nasa bangaren, jami’in shirin na jihar; Dakta Emmanuel Igbaukum ya bayyana cewa, masu ruwa da tsaki a jihar, sun nuna sha’awarsu ta shiga cikin shirin tare kuma da sanya shi a cikin tsarin jihar na samar da abinci mai gina jiki.

 

Ya kara da cewa, shirin zai kuma taimaka matuka wajen kara bunkasa fannin aikin noma na jihar baki-daya.

 

A nata jawabin, Babbar Sakatariya a ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci, Pharm. Elijah ta bayar da tabbacin cewa; gwamnatin jihar za ta bayar da kason kudi a kan lokaci tare kuma da yin rangwame wajen sayen kayan aikin noma cikin rahusa.

 

Ta bayyana cewa, gudunmawar shirin na IFAD ya taimaka matuka wajen kara bunkasa fannin tattalin arziki da kuma fannin aikin noma na jihar.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Noma Da Kiwo Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara October 11, 2025 Noma Da Kiwo Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina October 3, 2025 Noma Da Kiwo Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo October 3, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kungiyar (ASUU) Ta Sanar Da Shiga Yajin Aikin  Gargadi A Kasa Baki Daya .
  • Soja ya kashe matarsa, ya hallaka kansa a Jihar Neja
  • Yemen Ta Gargadi Isra’ila Kan Fuskantar Hare-Hare Idan Ta Karya Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta
  • Mutumin da ya sayar da ɗansa kan N1.5m ya shiga hannu a Ebonyi
  • Al’ummar Karamar Hukumar Dutse Sun Bukaci Gwamnatin Jigawa Ta Yashe Madatsar Ruwa Ta Warwade
  • Mutane 2 sun rasu a rikicin manoma da makiyaya a Kebbi
  • Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe
  • Kungiyoyin Falasdinawa Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Tsagaita Bude Wuta A Gaza
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida
  • Majalisar Turai Ta Bukaci Kasashen Nahiyar Su Kakkabo Jiragen Yakin Rasha