Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-27@21:16:01 GMT

Kano Na Karbar Bakuncin Babban Taron Kungiyar NUJ Na Kasa

Published: 13th, August 2025 GMT

Kano Na Karbar Bakuncin Babban Taron Kungiyar NUJ Na Kasa

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya jaddada kudirin gwamnatinsa na samar da kyakkyawar alaka da kafafen yada labarai.

 

Gwamna Yusuf ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi bakuncin shugaban kungiyar ‘yan jarida ta kasa (NUJ), Kwamared Alhassan Yahaya, da ‘yan majalisar zartaswar NUJ na kasa (NEC) da suka je Kano domin taronsu.

 

Gwamnan wanda mataimakinsa, Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo ya wakilta, ya yaba wa kungiyar ta NUJ bisa zabar Kano a taron ta na kasa, yana mai jaddada cewa wannan shaida ce ta kyakkyawar alakar aiki tsakanin gwamnatin jihar Kano da kafafen yada labarai.

 

Ya ce gwamnatinsa ta samu gagarumar nasara wajen inganta rayuwar jama’a, da kuma tabbatar da cewa dole ne a cika alkawuran yakin neman zabe.

 

“Wadannan alkawuran sun hada da samar da ababen more rayuwa, ilimi, kiwon lafiya, noma, da karfafa matasa da mata,” in ji shi, yana mai tabbatar da cewa gwamnati za ta ci gaba da fitar da wasu ayyuka da za a yaba don inganta rayuwar al’umma.

 

Mataimakin gwamnan ya ci gaba da yaba wa kungiyar ta NUJ bisa rawar da take takawa wajen tabbatar da dimokuradiyya, da tabbatar da bin doka da oda, da wayar da kan al’umma, inda ya ce kafafen yada labarai na da matukar muhimmanci wajen samar da shugabanci na gari.

 

Ya kara da cewa “Gwamnatinmu tana da abokantaka da kafafen yada labarai kuma za ta ci gaba da bayar da dukkan goyon bayan da suka dace don tabbatar da cewa ‘yan jarida suna gudanar da ayyukansu cikin ‘yanci, da sanin ya kamata, da kuma samar da yanayi mai kyau,” in ji shi.

 

Shugaban kungiyar ta NUJ, Kwamared Alhassan Yahaya ya yabawa gwamnatin jihar Kano bisa karbar bakuncin taron, ya kuma yaba da ci gaban jihar, wanda tawagar ta lura da haka a ziyarar gani da ido da ta kai a babban birnin.

 

“Mun gamsu da ci gaban da aka samu kawo yanzu ta fuskar samar da ababen more rayuwa da ake samu a Kano,” inji shi.

 

Alhassan ya yabawa gwamnatin jihar Kano bisa goyon bayan da take baiwa kafafen yada labarai, kuma ya nemi a dore da wannan matakin.

 

Tun da farko kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Ibrahim Waiya ya yi maraba da shugabannin kungiyar ta NUJ tare da yi musu fatan zaman lafiya a yayin taron, inda ya jaddada muhimmancin hadin gwiwa tsakanin gwamnati da kafafen yada labarai.

 

Ana sa ran taron NUJ NEC zai tattauna kan muhimman batutuwan da suka shafi aikin jarida a Najeriya, da suka hada da jin dadin kafafen yada labarai, kare lafiyar ‘yan jarida, da dabarun kungiyar na kare ‘yancin ‘yan jarida.

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: da kafafen yada labarai kungiyar ta NUJ tabbatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Ramaphosa ya soki kalaman Trump na cewa ba zai gayyaci shi a taron G20

Shugaban Afirka ta kudu, Cyril Ramaphosa ya soki kalaman takwaransa na Amurka Donald Trump na cewa ba zai gayyace shi taron kasashen gungun G20 mafiya karfin tattalin arziki na duniya a shekara mai zuwa a Florida.

Ramaphosa ya ce abin takaici ne yadda Trump ke ci gaba da daukar matakai bisa labaran da ba na gaskiya ba ko kuma aka yi musu kwaskwarima.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, Shugaban Amurka Donald Trump ya ce ba zai gayyaci Afirka ta kudu taron na badi ba, da Amurka zata karbi bakunci, kuma ya nanata sukar da yake yi wa Afirka ta kudun, kan zargin cewa an aikata kisan kiyashi a Afirka ta Kudu a kan tsirarun fararen fata.

Amurka ta kauracewa taron na G20 na bana a Johannesburg, inda shugabanni suka amince da matakan da aka ayyana na magance matsalar dumamar yanayi da sauran matsaloli na duniya, duk da kin yardar Amurka.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka ECOWAS ta yi Allah wadai da juyin mulki a Guinea Bissau November 27, 2025 Faransa, Jamus, Italiya, da Burtaniya sun yi tir da “karuwar rikici” a yammacin kogon jodan November 27, 2025 Rasha A Shirye Take Ta Taimaka Wa Najeriya A Fada Da Ta’addanci November 27, 2025 Palasdinawa Sun Karbi Gawawwakin Shahidai 15 Daga ‘Yan Mamaya November 27, 2025 Makaman Iran Masu Linzami Ne Kandagarkon  Dake Takawa Makiya Birki November 27, 2025 Najeriya: Allah Ya Yi Wa Babban Malamin Addini Shehu Dahiru Bauchi Rasuwa November 27, 2025 An Zabi Iran A Cikin Majalisar Zartarwa Ta Hukumar Yaki Da Makamai Masu Guba Ta Duniya CWC November 27, 2025 HKI Tana Amfani Da Tsagaita Wuta A Gaza Don Sake Shata Kan Iyakokin Yankin November 27, 2025 Yawan Falasdinawa Da Suka Yi Shahada Na Karuwa Saboka Keta Yarjeniyar Tsagaita Wuta November 27, 2025 An Rutsa Da Tsohon shugaban Kasar Najeriya A Guine Bissau Bayan Juyin Mulki November 27, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ramaphosa ya soki kalaman Trump na cewa ba zai gayyaci shi a taron G20
  • Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya- Shugaba Tinubu
  • Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya
  • Jihar Jigawa Za Ta Rufe Karbar Kudaden Aikin Hajjin 2026 Ranar 24 Ga Watan Disamba
  • Reuters: Kungiyar Likitoci Ba Da Iyaka Ba Ta Fice Daga Asibitin Darfur Bayan Bude Wa Ma’aikatanta Wuta
  • Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yabawa Pakistan Saboda Goyon Bayanta
  • Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yawaba Pakistan Saboda Goyon Bayanta
  • Hizbullah: Isra’ila na kuskure idan ta na tunanin kashe-kashen kwamandodinmu zai kawo karshen kungiyar
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano
  • Mali: An Dakatar Da  Aikin Kafafen Watsa Labarun Faransa Biyu A Cikin Kasar Mali