Kano Na Karbar Bakuncin Babban Taron Kungiyar NUJ Na Kasa
Published: 13th, August 2025 GMT
Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya jaddada kudirin gwamnatinsa na samar da kyakkyawar alaka da kafafen yada labarai.
Gwamna Yusuf ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi bakuncin shugaban kungiyar ‘yan jarida ta kasa (NUJ), Kwamared Alhassan Yahaya, da ‘yan majalisar zartaswar NUJ na kasa (NEC) da suka je Kano domin taronsu.
Gwamnan wanda mataimakinsa, Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo ya wakilta, ya yaba wa kungiyar ta NUJ bisa zabar Kano a taron ta na kasa, yana mai jaddada cewa wannan shaida ce ta kyakkyawar alakar aiki tsakanin gwamnatin jihar Kano da kafafen yada labarai.
Ya ce gwamnatinsa ta samu gagarumar nasara wajen inganta rayuwar jama’a, da kuma tabbatar da cewa dole ne a cika alkawuran yakin neman zabe.
“Wadannan alkawuran sun hada da samar da ababen more rayuwa, ilimi, kiwon lafiya, noma, da karfafa matasa da mata,” in ji shi, yana mai tabbatar da cewa gwamnati za ta ci gaba da fitar da wasu ayyuka da za a yaba don inganta rayuwar al’umma.
Mataimakin gwamnan ya ci gaba da yaba wa kungiyar ta NUJ bisa rawar da take takawa wajen tabbatar da dimokuradiyya, da tabbatar da bin doka da oda, da wayar da kan al’umma, inda ya ce kafafen yada labarai na da matukar muhimmanci wajen samar da shugabanci na gari.
Ya kara da cewa “Gwamnatinmu tana da abokantaka da kafafen yada labarai kuma za ta ci gaba da bayar da dukkan goyon bayan da suka dace don tabbatar da cewa ‘yan jarida suna gudanar da ayyukansu cikin ‘yanci, da sanin ya kamata, da kuma samar da yanayi mai kyau,” in ji shi.
Shugaban kungiyar ta NUJ, Kwamared Alhassan Yahaya ya yabawa gwamnatin jihar Kano bisa karbar bakuncin taron, ya kuma yaba da ci gaban jihar, wanda tawagar ta lura da haka a ziyarar gani da ido da ta kai a babban birnin.
“Mun gamsu da ci gaban da aka samu kawo yanzu ta fuskar samar da ababen more rayuwa da ake samu a Kano,” inji shi.
Alhassan ya yabawa gwamnatin jihar Kano bisa goyon bayan da take baiwa kafafen yada labarai, kuma ya nemi a dore da wannan matakin.
Tun da farko kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Ibrahim Waiya ya yi maraba da shugabannin kungiyar ta NUJ tare da yi musu fatan zaman lafiya a yayin taron, inda ya jaddada muhimmancin hadin gwiwa tsakanin gwamnati da kafafen yada labarai.
Ana sa ran taron NUJ NEC zai tattauna kan muhimman batutuwan da suka shafi aikin jarida a Najeriya, da suka hada da jin dadin kafafen yada labarai, kare lafiyar ‘yan jarida, da dabarun kungiyar na kare ‘yancin ‘yan jarida.
ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: da kafafen yada labarai kungiyar ta NUJ tabbatar da
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
Rundunar ‘yan sandan jihar Neja ta tabbatar wa al’ummar jihar a shirye ta ke ta ci gaba da kare mutuncin daidaikun mutane da kungiyoyin da suka sadaukar da kansu domin samar musu da sahihin bayanan sirri da za su kara kaimi wajen kare rayuka da dukiyoyin al’ummar Nijar.
‘Yan sanda a jihar Neja da ma Nijeriya ƙwararru ne don haka za su ci gaba da aiki da kuma nuna basira da ƙwarewa tare da ƙa’idarta ta sirrin rashin bayyana tushen bayanansu don samun sakamako mafi girma.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar Neja Adamu Abdullahi Elleman wanda ya bayar da wannan tabbacin a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Minna, ya bayyana cewa a kwanan baya ya halarci wani taron bita da hedkwatar ‘yan sanda ta shirya kan masu bada bayanai wato Informant domin kara kwarewarsa.
Sai dai Adamu Abdullahi Elleman ya danganta raguwar ayyukan aikata laifuka a Minna babban birnin jihar da sahihan bayanai da aka samu daga jama’a, goyon baya daga babban sufeto Janar na ‘yan sanda, Kayode Egbetokun da gwamnatin jihar Neja a karkashin jagorancin Gwamna Umar Bago, da sarakunan gargajiya da kuma matakin da ya dauka na cewa a mafi yawan lokuta yakan shiga sintiri a Minna, wanda DPO da kwamandojin yankin suka goyi bayansa.
A cewarsa sakamakon wannan yunkurin da aka yi da dama daga cikin miyagu da suka tsunduma cikin ayyukan ‘yan daba, an kama su, an kuma gurfanar da su a gaban kuliya, tare da daure su a matsayin misali ga wasu.
Adamu Abdullahi Elleman ya ci gaba da cewa, ya kuma gargadi Hakimai na yankin da su rika taimaka wa miyagu cewa duk wanda aka kama za a gurfanar da shi a gaban kuliya manta sabo.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar Neja, ya kuma yabawa babbar mai shari’a ta jihar, Mai shari’a Halima Ibrahim bisa goyon bayan da ta bayar wajen ganin an samar da shari’a cikin gaggawa, tare da samun hadin kai tsakanin ‘yan sanda da sauran kungiyoyin tsaro baya ga sabon alkawari da jami’an sa da mazaje suke yi na yakar miyagun laifuka da aikata laifuka a duk lungu da sako na jihar.
Adamu Abdullahi Elleman ya kuma kara da cewa a karkashin sa a matsayinsa na sabon kwamishinan ‘yan sanda mai kula da jihar Neja, jin dadin jami’ansa da jami’an rundunarsa shi ne babban abin da ya fi ba da fifiko wajen kara musu kwarin gwiwa wajen gudanar da ayyuka masu inganci.
INT Aliyu Lawal.