Wani Bangaren Majalisar Dokokin Jihar Zamfara Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Da Ta Karbe Mulkin Jihar
Published: 13th, August 2025 GMT
Majalisar Dokokin Jihar Zamfara karkashin jagorancin Bashar Aliyu Gummi, ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta hada kai da ayyukan tsaro a Jihar domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma, kamar yadda babi na biyu na kundin tsarin mulki ya tanada.
A zaman taron na ranar Talata, mambobin sun yi zargin cewa, ‘yan bindiga sun mamaye al’ummomi da dama a fadin jihar Zamfara, kuma sun zargi Gwamnan da mayar da hankali kan burin siyasa da kuma zargin abokan hamayya.
Sun kuma yi zargin cewa, Gwamnan bai kai ziyara ko aika tallafi ga al’ummomin da hare-hare ya shafa ba, inda suka ce ziyarar da ya shirya kai wa al’ummar Banga da ke karamar hukumar Kaura Namoda ta kasance da alaka da siyasa gabanin zaben fidda gwani na majalisar dokokin jihar.
A nasa gudunmuwar, Bashir Abubakar Masama na Bukkuyum ta Arewa ya yabawa kokarin gwamnatin tarayya na yaki da ‘yan fashi, inda ya bayyana cewa Adapka, Zauma, Gwashi, da Mayanchi a mazabarsa sun sha fama da hare-hare akai-akai.
Da yake goyon bayan kudirin, Bashir Bello Sarkin Zango na Bungudu ta Yamma, ya yi zargin cewa, Gidan Bugaje, Zaman Gida, Kukan Tara, da Gidan Dan-Inna, gungun miyagu sun mayar da yankin nasu, yayin da shugaban marasa rinjaye Aliyu Ango Kagara na Talata Mafara ta Kudu ya sanya Morai, Bobbo, Makera, Jangebe, Gwaram, da Ruwan Gizo a matsayin kauyukan da lamarin ya fi shafa a mazabarsa.
‘Yan majalisar sun bukaci gwamnatin tarayya da ta yi watsi da gwamnatin jihar a harkokin tsaro.
Sun yi kira ga mazauna yankin da su kasance masu bin doka da oda tare da bayar da sahihan bayanai ga hukumomin tsaro.
A nasa bangaren, Ibrahim Tudu Tukur na Bakura ya yi zargin cewa al’ummarsa na ci gaba da zama a killace da ‘yan bindiga, inda ya bayar da misali da harin da aka kai a kwanan nan a Damri, Dakko, Sama, Sabon Garin Damri, da Sade, yayin da Faruk Musa Dosara na Maradun ya yi kira da a duba yiwuwar tsige Gwamnan bisa zarginsa da yin sakaci da aikinsa.
Ya kuma jaddada bukatar mazauna yankin su baiwa jami’an tsaro sahihin bayanai kan duk wani nau’in da ake zargi da aikata laifuka domin a kama su kafin su aikata wani laifi.
Sun kuma yi alkawarin ci gaba da yin kira da a samar da shugabanci na gari a Zamfara domin ci gaban jihar.
AMINU DALHATU.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: siyasa yi zargin cewa
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba
Ya bayyana cewa an riga an hada wadanda aka ceto da iyalansu, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike da aikin ceton domin gano wadanda suka aikata laifin da kuma kubutar da sauran wadanda ake tsare da su, idan suna nan.
A halin da ake ciki kuma, kwamandan Runduna ta 6 ta Sojan Nijeriya, Birgediya Janar Kingsley Chidiebere Uwa, ya yaba da saurin daukar mataki da hadin kai tsakanin sojoji da ‘yansanda wanda ya kai ga nasarar aikin ceton.
Ya sake jaddada kudirin rundunar wajen tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a a Jihar Taraba.
Sai dai, ya bukaci jama’a da su ci gaba da bai wa sojoji da sauran hukumomin tsaro goyon baya ta hanyar samar da sahihan bayanai a kan lokaci domin taimaka wa a ayyukan tsaro da ake gudanarwa a fadin jihar.
A wani labari mai nasaba da haka, Kungiyar Matan Sojoji da ‘Yansanda (DEPOWA) ta yaba da jajircewa da sadaukarwar dakarun rundunonin sojojin Nijeriya da sauran jami’an tsaro, wadanda ke ci gaba da sadaukar da rayuwarsu domin kare kasar.
Kungiyar ta kuma yi addu’a ga Allah domin kare mazajensu, wadanda ke kwana suna tashi a kan bakin aiki domin tabbatar da tsaron ‘yan Nijeriya.
Shugabar kungiyar DEPOWA, kuma matar Babban Hafsan Tsaro na Kasa (CDS), Mrs. Oghogho Musa, ta bayyana wannan godiya tare da yin addu’o’i a birnin Abuja yayin gudanar da wasan motsa jiki na rawa (Dance Aerobics Edercise) da aka gudanar a makarantar DEPOWA da ke sansanin Mogadishu.
Shugabar DEPOWA ta kuma jaddada kudirin kungiyar na gudanar da yakin addu’a da godiya na tsawon shekara guda ga dakarun da ke bakin daga, domin nuna yabo da godiya ga jajircewarsu wajen kare kasar Nijeriya, duk da hadarin da ke tattare da aikin.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA