An kama ɗan shekara 18 kan zargin fashi da makami a Gombe
Published: 13th, August 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe ta cafke wani matashi mai shekaru 18, Hassan Aminu Sadiq, bisa zargin aikata fashi da makami a lokuta daban-daban, bayan wani samame da aka kai unguwar unguwar Yelwa da ke garin Kwadon a Karamar Hukumar Yemaltu Deba.
Mai magana da yawun rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya ce an kama wanda ake zargin ne a ranar 9 ga Agusta, 2025, da misalin ƙarfe 2:30 na rana, yana ɗauke da kunshin ganyen da ake zargin tabar wiwi ne.
Binciken da aka soma gudanarwa ya nuna cewa Hassan yana cikin jerin mutanen da ake nema ruwa-a-jallo, bisa zarginsa da hannu a manyan hare-hare biyu na fashi da makami da ake ci gaba da shari’arsu a Babbar Kotun Jihar Gombe.
“An kama shi ne bayan samun bayanan sirri, kuma ya amsa cewa ya shiga cikin waɗannan hare-hare biyu na fashi da makami,” in ji DSP Abdullahi.
Kwamishinan ’Yan Sanda, CP Bello Yahaya, ya ba da umarnin a mika wanda ake zargin tare da kayan laifin da aka samu ga sashen binciken manyan laifuka domin ƙarin bincike da gurfanar da shi a gaban kotu.
Rundunar ta jaddada aniyarta na kawar da miyagun laifuka a jihar tare da kira ga jama’a da su ci gaba da bayar da bayanai cikin lokaci domin taimaka wa ayyukan jami’anta.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: jihar Gombe
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Shura ta fara ganawar sirri da Malam Triumph
Majalisar Shura ta Jihar Kano ta fara zama da Malam Lawan Shu’aibu Abubakar (Triumph) kan zargin da wasu kungiyoyi biyar ke masa zargin batanci ga Manzon Allah SallalLahu alaihi Wasallama.
Wannan tattaunawa tana gudana ne a cikin sirri a Ofishin Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) kuma ya samu halarcin fitattun malaman Musulunci na Jihar Kano.
Mahalarta sun haɗa shugaban majalisar shurar Malam Abba Koki da Wazirin Kano, Sa’ad Shehu Gidado, da sakatare, Shehu Wada Sagagi, da mambobin kwamitin da Majalisar Shurar ta kadfa domin zargin binciken zargin da ake wa Malam Triumph.