An kama ɗan shekara 18 kan zargin fashi da makami a Gombe
Published: 13th, August 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe ta cafke wani matashi mai shekaru 18, Hassan Aminu Sadiq, bisa zargin aikata fashi da makami a lokuta daban-daban, bayan wani samame da aka kai unguwar unguwar Yelwa da ke garin Kwadon a Karamar Hukumar Yemaltu Deba.
Mai magana da yawun rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya ce an kama wanda ake zargin ne a ranar 9 ga Agusta, 2025, da misalin ƙarfe 2:30 na rana, yana ɗauke da kunshin ganyen da ake zargin tabar wiwi ne.
Binciken da aka soma gudanarwa ya nuna cewa Hassan yana cikin jerin mutanen da ake nema ruwa-a-jallo, bisa zarginsa da hannu a manyan hare-hare biyu na fashi da makami da ake ci gaba da shari’arsu a Babbar Kotun Jihar Gombe.
“An kama shi ne bayan samun bayanan sirri, kuma ya amsa cewa ya shiga cikin waɗannan hare-hare biyu na fashi da makami,” in ji DSP Abdullahi.
Kwamishinan ’Yan Sanda, CP Bello Yahaya, ya ba da umarnin a mika wanda ake zargin tare da kayan laifin da aka samu ga sashen binciken manyan laifuka domin ƙarin bincike da gurfanar da shi a gaban kotu.
Rundunar ta jaddada aniyarta na kawar da miyagun laifuka a jihar tare da kira ga jama’a da su ci gaba da bayar da bayanai cikin lokaci domin taimaka wa ayyukan jami’anta.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: jihar Gombe
এছাড়াও পড়ুন:
NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas
Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA) ta kama wanda ya kafa kuma yake kula da cocin ‘The Turn of Mercy’, Adefolusho Olasele, wanda aka fi sani da Abbas Ajakaiye, bisa zarginsa da hannu wajen safarar miyagun kwayoyi da dama daga Ghana zuwa Nijeriya. Fasto Olasele, wanda ya shafe watanni ba a san inda yake ba, an kama shi ne a ranar Lahadi, 3 ga watan Agusta, 2025, a cocinsa da ke Okun Ajah, yankin Lekki, a Legas. NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho Wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar, Femi Babafemi, ya fitar a ranar Lahadi, ta ce, jami’an hukumar sun jira har zuwa lokacin da ya gama wa’azi na ranar Lahadi kafin su kama shi a lokacin da ya fito daga harabar cocin. A cewarsa, faston ya gudu zuwa Ghana a cikin watan Yuni don gujewa kama shi bayan da jami’an tsaro suka alakanta shi da laifin safarar miyagun kwayoyi kulli biyu kimanin kilo 200 da aka gano a bakin tekun Okun Ajah a ranar 4 ga watan Yuni da kuma kilo 700 da aka samu a cikin motarsa ta kai sako a ranar 6 ga watan Yuli.Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp