Aminiya:
2025-10-13@15:50:02 GMT

Matsalar tsaro na iya hana mu ci gaba da rijistar masu zabe a Borno – INEC

Published: 15th, August 2025 GMT

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta ce matsalar tsaro na iya hana ta gudanar da aikin rijistar masu zabe a kananan hukumomin jihar Borno guda hudu.

Kananan hukumomin da lamarin zai iya shafa su ne Abadam, Guzamala, Marte da Kala-Balge.

Jama’a ba sa yaba wa kokarinmu na hana aikata laifi – Babban Sufeton ’Yan Sanda NAJERIYA A YAU: Halin ƙuncin da ’yan fansho ke ciki a Najeriya

Bayanin hakan dai ya fito ne daga bakin Kwamishinan Zabe na jihar, Abubakar Ahmad Ma’aji a jawabin sa ga manema labarai a Maiduguri, a wani vangare na shirye-shiryen fara gudanar da aikin rijistar masu kada kuri’a a ranar Litinin da ke tafe.

A cewar shi, INEC ta mayar da rijistar masu zaben a karamar hukumar Abadam zuwa kan hanyar Baga, daura da ofishin Yerwa Peace.

Kazalika, ya ce a karamar hukumar Guzamala an mayar da wurin yin rajistar sashen kashe gobara na rukunin gidaje 1,000.

Ya ce sauran kananan hukumomin kamar karamar hukumar Kala-Balge an mayar da aikin ya koma zuwa  makarantar firamare ta Goni Kachalari da ke birnin Maiduguri.

Shi kuma aikin rijistar masu kada kuri’a na qaramar hukumar Marte an mayar da shi ya zuwa Kachamai, wadanda dukkansu suna cikin birnin Maiduguri ne.

Don haka kwamishinan ya yi kira ga mutanen kananan hukumomin da su yi hakuri da wannan canji da aka samu, inda ya ce an yi ne da kyakkyawar manufar da duk wanda abin ya shafa zai samu rijistarsa cikin kwanciyar hankali.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: matsalar tsaro rijistar masu

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Uba Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 

 

A cikin nuna jajircewa da hadin kai tsakanin gwamnati jiha da ta tarayya, Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, a ranar Juma’a ya gana da Ministan Ayyuka, Sanata David Umahi, CON, domin yin cikakken bitar aikin titin Abuja–Kaduna–Abuja

 

Taron, wanda aka gudanar a birnin Abuja, ya nuna irin salon jagorancin Gwamna Uba Sani na jajircewarsa wajen tabbatar da kammala wannan muhimmin titi wanda ke da matuƙar tasiri ga tattalin arzikin ƙasa.

 

Tattaunawar ta mayar da hankali ne kan yadda za a hanzarta kammala ɓangaren Abuja–Jere da Kaduna, wanda ke da muhimmanci ga miliyoyin ‘yan Nijeriya da ke amfani da shi kullum wajen sufuri, kasuwanci da hulɗar zamantakewa.

 

Gwamna Uba Sani ya jaddada cewa wannan titin ba na yankin Arewa kadai ba ne, ya bayyana shi a matsayin jijiyar ƙasa da ƙasa ne wadda ke haɗa yankuna daban-daban tare da ƙarfafa haɗin kai da bunƙasar tattalin arziki.

 

Ya kara da cewa titin Abuja- Kaduna da Kano na ɗaya daga cikin manyan ayyukan gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu a ƙarƙashin Manufar Sabon Fata na (Renewed Hope Agenda), wadda ke nufin sabunta manyan gine-ginen ƙasa da inganta tattalin arziki.

 

Yace “Wannan titi ba hanya ce kawai ba inda yace wata hanya ce ta tattalin arziki wadda ke haɗa mutane, kasuwanni, da dama a fadin Arewacin Nijeriya da ma bayan haka,”

 

A nasa jawabin, Sanata Umahi ya yaba wa Gwamna Uba Sani bisa yadda yake kaiwa da komowa domin kare muradun al’ummar Kaduna, tare da tabbatar da cewa gwamnatin tarayya ta kuduri aniyar kammala aikin cikin lokaci. Ya bayyana cewa an umarci kamfanonin da ke aikin da su rika aiki sau biyu a rana domin hanzarta cigaba ba tare da rage inganci ba.

 

Ministan ya kara da cewa amfani da fasahar siminti mai ɗorewa wanda zai tabbatar da cewa titin zai dawwama tare da rage kudin gyara nan gaba.

 

Kamfanonin da ke aikin sun yi alkawarin ƙara gaggautawa musamman a yankin Jere dake jihar Kaduna, inda ake sa ido sosai kan ci gaban aiki. Gwamnatin Jihar Kaduna ta kuma tabbatar da ci gaba da haɗin kai da Ma’aikatar Ayyuka ta Tarayya domin magance ƙalubalen da ke iya janyo tsaiko.

PR: Shettima Abdullahi

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku
  • Kungiyar Malaman Jami’o’in Najeriya ASUU ta Shiga Yajin Aiki
  • Za A Yi Wa Masu Lalurar Ido Aiki Kyauta A Jihar Jigawa
  • Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa
  • Al’ummar Karamar Hukumar Dutse Sun Bukaci Gwamnatin Jigawa Ta Yashe Madatsar Ruwa Ta Warwade
  • Gwamna Uba Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 9, Sun Ƙwato Naira Miliyan 5 A Borno
  • 2027: INEC Ta Nemi A Gaggauta Amincewa Da Ƙudirin Sake Fasalin Tsarin Zaɓe
  • ’Yan Najeriya miliyan 60 na fama da taɓin hankali – Likita
  • Sojoji sun mutu yayin da Boko Haram ta kai hari sansanin soji a Borno