Tinubu ya cancanci yabo kan daidaita tattalin arzikin Nijeriya —Ngozi
Published: 14th, August 2025 GMT
Shugabar Kungiyar Cinikayya ta Duniya (WTO), Ngozi Okonjo-Iweala, ta bayyana cewa Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya cancanci yabo kan daidaita tattalin arzikin ƙasar nan da yake ci gaba da yi.
Okonjo-Iweala ta shaida wa manema labarai hakan ne ranar Alhamis bayan ta gana da shugaban ƙasar a Abuja.
“Shugaban ƙasa [Tinubu] da muƙarrabansa sun yi ƙoƙari sosai wajen daidaita tattalin arzikin Nijeriya.
“Wannan namijin ƙoƙarin na Tinubu abu ne da ya zama dole a yaba masa da ba kowa zai iya yi ba.
Tsohuwar Ministar Kuɗin ta Nijeriyar ta ƙara da cewa, yanzu aikin da ke gaban shugaban shi ne ya haɓaka tattalin arzikin ta yadda kowane ɗan ƙasa zai samu na kansa cikin sauƙi.
Ngozi ta yi kira ga gwamnatin Nijeriyar ta tanadi hanyoyi da dabarun sauƙaƙa wa talakawan ƙasar da ke fama da raɗaɗin tsare-tsaren tattalin arziƙi da gwamnatin Tinubu ke aiwatarwa.
Duk da ta yaba wa shugaban ƙasar kan tsare-tsarensa na tattalin arziki da suka haɗa da cire tallafin man fetur, tsohuwar Ministar Kuɗin ta ce dole ne gwamnatin ta tallafa wa ’yan ƙasar.
Iweala ta ce “muna ganin shugaban ƙasar da gwamnatinsa sun daidaita tattalin arzikin Najeriya, amma duk da haka sai sun tabbatar da ɗorewar sauyin mai kyau da aka samu zuwa yanzu.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Tattalin Arziki daidaita tattalin arzikin
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Ya Nada Hukumar Gudanarwa Ta NCC Da Sauran su
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da kundin tsarin mulki na hukumar sadarwa ta Najeriya (NCC) da asusun samar da ayukka na kasa da kasa (USPF), dukkanin su a karkashin ma’aikatar sadarwa, kirkire-kirkire da tattalin arziki na zamani.
A cikin wata sanarwa da Bayo Onanuga, mai baiwa shugaban kasa shawara kan yada labarai ya fitar, ya ce an nada Idris Olorunnimbe a matsayin shugaban hukumar NCC, yayin da Dr. Aminu Waida ya ci gaba da zama mataimakin shugaban zartarwa/Babban jami’in gudanarwa, mukamin da aka nada shi a watan Oktoban 2023 kuma majalisar dattawa ta tabbatar da shi a watan Nuwamba na wannan shekarar.
A baya Olorunnimbe ya yi aiki a hukumar kula da ayyukan yi na jihar Legas (LSETF), inda ya jagoranci kwamitin masu ruwa da tsaki da gudanar da mulki tare da jagorantar shirye-shiryen samar da ayyukan yi da samar da kasuwanci ga matasa.
Sauran mambobin hukumar NCC sun hada da Abraham Oshidami (Kwamishina, Ayukkan Fasaha), Rimini Makama (Kwamishiniyar Gudanarwa), Hajia Maryam Bayi (Kwamishinar kula da ma’aikata), Col. Abdulwahab Lawal (Rtd), Sanata Lekan Mustafa, Chris Okorie, Gimbiya Oforitsenere Emiko, da Sakataren Hukumar.
Ga USPF, Dokta Bosun Tijani, Ministan Sadarwa, Ƙirƙiri da Tattalin Arziki na Zamani, zai zama shugaba. Olorunnimbe kuma an nada mataimakin shugaba.
Sauran mambobin sun hada da Oshidami, Makama, Aliyu Edogi Aliyu (wakilin FMCIDE), Joseph B. Faluyi (Ma’aikatar Kudi ta Tarayya), Auwal Mohammed (Ma’aikatar Kasafi da Tsare-tsare ta Tarayya), Uzoma Dozie, Peter Bankole, Abayomi Anthony Okanlawon, Gafar Oluwasegun Quadri, da Sakataren USPF.
PR/Bello Wakili