“Tsarin mulkin ADC ta bayyana cewa duk wanda ke neman zama shugaban jam’iyyar, dole ne ya kasance mamba nagari na jam’iyya. Wannan shi ne muhimman bukata ta asali wadda ba za a iya yin watsi da ita ko kauce mata ta kowace hanya ba.

“A cewar tsarin mulkin ADC, hanyar da ta dace don cike gurbin jagoranci bayan tafiyar Cif Nwosu ita ce, ta hanyar taron kwamitin zartarwa na kasa.

Tsaagin jam’iyyar ta sake tabbatar da cewa Alhaji Nafiu shi ne halastaccen shugabanta na kasa tare da kira ga ‘ya’yan jam’iyyar da su ci gaba da kasancewa cikin kwanciyar hankali da hadin kai.

Ya kuma bayyana kwarin giwa kan ikon hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) na kiyaye ka’idojin kundin tsarin mulki da na dimokuradiyya a cikin harkokin jam’iyyar siyasa.

Ya kara da cewa, “Wannan taron zai zama dandalin tattaunawa kan hanyar ci gaba kuma za a biyo bayansa da tantancewa a matakai na gaba na taron jam’iyyar. Wannan ne inda za mu tabbatar da cewa jagorancin jam’iyyarmu an kayyade ta ne daga wadanda ke da gaske suna sha’awar ra’ayoyi da manufofin ADC.”

“Muna so mu jaddada cewa babu wani tanadi a cikin tsarin dokokin hukumar zabe da tsarin mulki ko dokokin jam’iyyar ADC da ke ba mutum damar karbar jagoranci ba tare da cika sharuddan zama mamba ba da tsarin dimokuradiyya ya tanada.

“Ayyukan da Dabid Mark da abokan huldarsa ke yi ba kawai saba wa tsarin mulkin jam’iyyarmu ba ne, yana kuma nuna rashin girmamawa ga ka’idojin dimokuradiyya da ADC ta tsayu a kai.

“Muna kira ga mambobinmu masu muhimmanci da jajircewa, ku da ku kasance cikin zaman lafiya da kuma mayar da hankali a wannan lokaci na neman samun sauye-sauye. Ci gaban da muka yi a matsayin jam’iya shaida ce ga aikin tukuru da jajircewar mambobinmu na asali.

“Dole ne mu kalubanci abubuwa marasa kyau na wadanda ke son kawo cikas ga hadin kanmu da ci gabanmu. ADC jam’iyya ce da aka gina bisa ginshikin gaskiya, hadin kai, da dabi’un dimokuradiyya, kuma dole ne mu yi aiki tare wajen kare wadannan ka’idoji.

“A daidai wannan lokaci, muna kuma son tabbatar da cewa muna da kwarin giwa kan hukumar zabe ta kasa wacce ba ta dogaro da gwamnati da shiga cikin wannan lamari. Muna yarda da sadaukarwarta wajen tabbatar da bin doka da tsari da tabbatar da cewa ana girmamawa kuma ana bin tsarin dimokuradiyya a cikin jam’iyyun siyasa. Jam’iyyar ADC ta ci gaba da jajircewa wajen yin aiki tare da INEC don inganta yanayin siyasa wanda zai kasance mai kyau tare da martaba tsarin dimokuradiyya.

“A karshe, muna goyon bayan Alhaji Nafiu a matsayin shugaban jam’iyyar ADC na gaskiya. Jagorancinsa zai zama mai mutunta ka’idojin jam’iyyarmu a wannan lokaci na canji, kuma muna da tabbacin cewa zai kula da hakkin asalin mambobinmu masu daraja. Muna kira ga dukkanin ‘ya’yan jam’iyyar ADC na asali su goyi bayan Alhaji Nafiu da kuma aiki tare da shi don inganta jam’iyyarmu da al’umar da muke yi wa hidima.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: tabbatar da cewa jam iyyar ADC jam iyyarmu

এছাড়াও পড়ুন:

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

Muryoyi daga ko’ina cikin duniya sun nemi a warware matsalar bisa turbar adalci. Shugabannin tarayyar Turai sun yi ta kira ga kasashen Sin da Amurka da su kiyaye bude kasuwanni da gudanar da gasa ta gaskiya. Kasashen kudu maso gabashin Asiya, sun ba da shawarar tabbatar da kwanciyar hankali. Kasashen Afirka da na Latin Amurka sun nuna damuwa da halin da ake ciki saboda barazanar da lamarin yake yi ga damarmakin zuba jari da kasuwancin kasashensu.

Gyaruwar dangantakar tattalin arziki tsakanin Sin da Amurka za ta iya haifar da wani sabon zamani na hadin gwiwa, da kirkire-kirkire, da ci gaban da ya kunshi kasashen duniya baki daya. A wannan duniyar tamu wadda bukatar hada hannu da juna ke kara bayyana, kiran a bayyane yake, wato duniya tana bukatar Sin da Amurka ba kawai don zama tare ba, har ma su zama ababen buga misali a bangaren aiki tare. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • UBEC Ta Kaddamar Da Makarantun Zamani 21 A Sassan Nijeriya
  • An zabi sabuwar firaminista a Luthuania
  • Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu
  • Rangwame: Tinubu Ya Bada Umarnin Sake Bitar Tsarin Yadda Ake Karɓar Haraji 
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 126
  • An naɗa sabon Sarkin Alkaleri a Bauchi
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 125
  • ETFund Ta Koka Kan Gibin Da Ake Samu A Sashin Lafiyar Najeriya
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe Jama’a A Kauyukan Sakkwato