‘Yan Majalisa Na Amsar Cin Hanci Har Naira Miliyan 3 Kafin Su Gabatar Da Wani Ƙudiri – Kamfani.
Published: 15th, August 2025 GMT
A yayin da yake martani kan suka da ake yi masa na rashin gabatar da kudirori a gaban majalisar, ya bayyana cewa, “tun da na je Majalisar, ba bu wani dan mazabata da ya rubuto min wani kudiri ko bukata da zan gabatar a gaban Majalisa, duk zarge-zargen karya ne suke yi min, kuma idan har akwai, wani ya fito ya kalubalance ni,” inji shi.
“Hatta gabatar da kudirori da korafe-korafe a majalisar, wasu sai sun amso cin hancin kimanin naira miliyan 1, ko naira miliyan 2, ko naira miliyan 3, domin karantawa a zauren majalisar, bayan an karanta kudirin, kuma dole sai sun bibiyi ‘yan majalisa sama da 360 domin su goyi bayan a amince da kudirin.”
Dan majalisar ya kuma yi watsi da zarge-zargen da ake masa na cewa, ya yi watsi da shirye-shiryen tallafawa matasa a mazabarsa, inda ya ce galibin ayyukan da yake yi suna amfanar da matasa kai tsaye.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Sin Ta Gabatar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakaninta Da Amurka A Stockholm
Biyo bayan sanarwar hadin gwiwa bayan taro kan tattalin arziki da cinikayya da aka yi tsakanin Sin da Amurka a birnin Geneva a ranar 12 ga watan Mayun 2025 wato sanarwar Geneva, da tarukan da aka yi a birnin London a ranekun 9 da 10 ga watan Yunin 2025, da wanda aka yi a Stockholm a ranekun 28 da 29 ga watan Yulin 2025, gwamnatin jamhuriyar jama’ar kasar Sin da gwamnatin Amurka, sun waiwayi alkawuran da suka dauka karkashin sanarwar hadin gwiwa ta Geneva, kuma sun amince cewa daga ranar 12 ga watan nan na Agusta, za su fara aiwatar da matakai kamar haka:
Amurka za ta ci gaba da gyara matakan karin haraji kan kayayyakin kasar Sin, ciki har da na yankin musammam na Hong Kong da na Macau, wanda tana cikin umarni shugaban kasar mai lamba 14257 na ranar 2 ga watan Afrilun 2025, ta hanyar dakatar da maki kaso 24 na karin har na tsawon kwanaki 90, daga ranar 12 ga watan Agustan bana, yayin da za a ci gaba da aiwatar da karin harajin kaso 10 kan wadannan kayayyaki bisa tanade tanaden wannan umarni.
Ita kuma a nata bangare, kasar Sin za ta ci gaba da gyara matakan karin haraji kan kayayyakin Amurka da aka tanada cikin umarni mai lamba 4 ta 2025, na babbar hukumar kwastam ta majalisar gudanarwar kasar, ta hanyar dakatar da maki kaso 24 na karin har tsawon kwanaki 90, daga ranar 12 ga watan Agustan bana, yayin da za a ci gaba da aiwatar da karin harajin kaso 10 kan wadannan kayayyaki. Haka kuma, Sin za ta ci gaba da aiwatar da matakan dakatarwa ko cire matakan ramuwa da ba na haraji ba da ta dauka kan Amurka, kamar yadda bangarorin biyu suka amince cikin sanarwar hadin gwiwar da suka fitar a Geneva. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp