Aminiya:
2025-08-14@12:36:59 GMT

Ba a ba mu dala 100,000 da gwamnati ta mana alƙawari ba — Super Falcons

Published: 14th, August 2025 GMT

Kyaftin ɗin ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta mata ta Najeriya, Super Falcons, Rasheedat Ajibade, ta ce har yanzu ba a ba su dala 100,000 da Gwamnatin Tarayya ta yi musu alƙawari bayan sun lashe gasar WAFCON a ƙasar Maroko ba.

Ajibade, ta bayyana takaicinta game da jinkirin biyan kuɗin da aka musu alƙawari.

Amurka za ta sayar wa Najeriya makaman N530bn don yaƙi da ta’addanci ’Yan ci-rani 26 sun nitse a teku suna ƙoƙarin tsallakawa Turai

“Ba mu karɓi kuɗin ba tukunna, amma ina fata za a biya mu.

Duk alƙawuran da aka mana, yanzu dai ba mu samu komai ba.”

Ajibade ta jagoranci tawagar zuwa ga nasara, inda suka sake lashe kofin WAFCON a bana.

Bayan nasarar, Shugaba Bola Tinubu ya bai wa ’yan wasan da masu horar da su lambar yabo ta ƙasa (Officer of the Order of Niger – OON).

Haka kuma ya yi musu alƙawarin bai wa kowannensu dalar Amurka 100,000 da gida mai ɗaki uku.

Lokacin da ya karɓe su a Fadar Shugaban Ƙasa, Tinubu ya yaba da jajircewarsu, da kuma ƙoƙarinsu, inda ya ce nasararsu ta ɗaga mutuncin Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan wasa Alƙawari Kyaftin Ƙwallon ƙafa WAFCON

এছাড়াও পড়ুন:

Ruwan Wutan sojan Nijeriya Ya Kashe ‘Yan Bindiga A Zamfara.

Dakarun Operation FANSAN Yamma (OPFY) sun yi nasarar fatattakar ‘yan ta’adda da dama a wani hari da suka kai ta sama da kasa a yankin Makakkari da ke dajin Gando a karamar hukumar Bukkuyum a jihar Zamfara.

 

Wannan farmakin wanda ya gudana a ranar 10 ga watan Agustan shekarar 2025, ya biyo bayan wasu bayanan sirri da suka samu cewa dimbin ‘yan ta’addan da ke biyayya ga marigayi Halilu Buzu da Alhaji Beti sun taru a cikin dajin inda suka shirya kai harin ramuwar gayya kan al’ummomin Addabka da Nasarawan Burkullu a garin Bukkuyum.

 

Jami’in yada labarai na rundunar ‘Operation Fansan Yamma OPFY’ Kyaftin David Adewusi, ya ce bayanan sirri sun nuna cewa, harin da suka shirya kai harin shi ne ramuwar gayya da suka sha a baya-bayan nan a arangamar da suka yi da jami’an tsaro da wasu rundunonin tsaro.

 

Ya bayyana cewa, a wani samame na hadin gwiwa na kasa da ya biyo baya, dakarun da ke karkashin sashe na 2 sun kame tare da fatattakar ‘yan ta’addan da suka gudu daga inda aka kai harin ta sama.

 

Kyaftin Adewusi ya tabbatar wa ‘yan kasa masu bin doka da oda cewa ‘yan ta’adda da sauran masu rike da makamai ba za su samu mafaka a yankin Arewa maso Yamma da wasu sassan shiyyar Arewa ta tsakiya ba.

 

Ya nanata kudurin sojojin na fatattakar abokan gaba a duk inda suka taru ko kuma suka matsa sannan ya bukaci mazauna yankin da su baiwa jami’an tsaro hadin kai ta hanyar ba da rahoton abubuwa, yana mai cewa bayanan da suka dace kan lokaci na da matukar muhimmanci wajen kare al’umma da kuma kawo karshen barazanar ta’addanci da ‘yan fashi.

 

 

 

REL/AMINU DALHATU.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka za ta sayar wa Najeriya makaman N530bn don yaƙi da ta’addanci
  • Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe Jama’a A Kauyukan Sakkwato
  • Ma’aikatar Cinikayya Ta Kasar Sin Ta Yi Karin Haske Kan Batun Saka Wasu Sassa Cikin Wadanda Ta Sanyawa Takunkumin Sayar Musu Da Kayayyaki
  • Dasuki: Kotu ta bai wa Gwamnatin Tarayya wa’adin kammala shari’ar kuɗin makamai
  • Ruwan Wutan sojan Nijeriya Ya Kashe ‘Yan Bindiga A Zamfara.
  • Yajin Aikin NLC Da TUC Ya Gurgunta Ayyukan Gwamnati A Taraba.
  • NAJERIYA A YAU: Yadda matasa ke bayar da gudunmawa ga ci-gaban al’umma
  • UNICEF Da Gavi Sun Bada Na’urorin Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Ga Jihar Kano