Leadership News Hausa:
2025-07-25@05:09:47 GMT

Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027

Published: 23rd, March 2025 GMT

Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027

Ita maganar bada damar tsayawa takara ba tare da zaben fidda gwani ba an dauki matakin ne saboda yadda aka ga ‘yan adawa ko jam’iyyun adawa suke kokarin tayar da babbar kura mai hayaki,wa ita jam’iyyar mai rike da kambun mulki a 2027 domin “Ba a san maci Tuwo ba sai Miya ta kare”.

Ana dai ganin tarurrukan da aka yi na mambobin APC,wadanda suke ganin ba,a kyauta masu ba da kuma Shugabannin adawa suna yin wani shiri wanda zai iya sa wasu daga cikinsu su yi jerin Tururuwa na komawa jam’iyyar SDP,kamar dai yadda tsohon Gwamnan Jihar Kaduna,Malam Nasiru El Rufa’i ya fara kasancewa na farko wanda ake ganin akwai wadanda za su iya goyo masa baya.

Idan dai ba a manta ba mako biyu da ya wuce kwamitin zartarwar jami’iyyar ya nuna amincewa da ayyukan da Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi,hakan yana nuna ko dai su amince da bashi tikitin takara k kuma akashin hakan.

Akwai majiya mai tushe da ta bayyana a cikin taron kwamitin zartarwa na jam’iyyar da aka yi a Abuja ya nuna cewa kamar yadda abin yake an tattauna ne kan yadda tsarin Shugabancin jam’iyyar yake tun daga sama zuwa kasa,ko kuma daga na kasa, Jiha, Karamar Hukuma har zuwa na mazabar Kansila (Ward) an tattauna komai kan hakan.

Akwai majiyar da bata son a ambacin sunanta, da yi bayanin akwai wasu daga cikin Gwamnonin da basu amince da lamarin ba gaba daya ba,su ma da akwai wani tsarin da ake yi wanda zai basu damar su zabi wadanda suke son tsayawa takarar majalisar Jiha a Jihohinsu.

Idan har shi tsarin da aka yi an samu yin amfani da shi kwatin zartarwar jam’iyyar na kasa karkashin jagorancin Dakta Umar Abdullahi Ganduje da takwarorinsu na Jihohi za a barsu su ci gaba da tafiyar da jam’iyyar,saboda su taimakawa shirin da ake yi na kasancewar Bola Ahmed Tinubu shi ne dan takarar jam’iyyar.

Dankararar jam’iayyr daya tilo,suma ‘yan majalisun Dattawa da Wakilai wadanda suka ba jam’iayyar goyon baya tun daga lokacin da,Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya fara mulki.

“Shugabannin jam’iyyar sun san kura- kuren da aka yi a baya wanda matsala ce ta cikin gida wadda ta so sa wa jam’iyyar wani babban Tarnaki abinda daga karshe ya sa lakar jam’iyya ta kasance tamkar “Kazar da Kwai ya fashe ma ta a Ciki”. Wannan lokacin, ana bukatar ne kada a samu wata matsalar da zata iya kawo koma-baya. Hanya mafi dacewa ta yin hakan ita ce a ci gaba da tafiya irin yadda TSARIN Shugabancin jam’iyyar APC ya tsara ayi, domin a kaucewa aukuwar lamarin da zai sa ayi ta yin kumfar Baki saboda zaben fidda gwani.

“Idan za a tuna a zaben shekarar 2019, a babban zaben a Jihar Zamfara, mun rasa Jihar Zamfarar ne “inda jam’iyyar PDP ta samu dame a kala”,saboda rikicin cikin gida wanda ya fara ne sanadiyar zaben fidda gwani wanda aka ci gaba har zuwa 2023.

“Hakanan ma jam’iyyar APC, bata da ‘yan takara a Jihar Ribas saboda zaben fidda gwanin da mambobin jam’iyyar suka yi sau biyu kuma mabambanci.Hakanan ma akwai matsala wadda zaben Shugabannin jam’iyyar ya kusan gamawa da Jihar Imo. Idan ba lamarin kotu ba mun kusa rasa kujerar mu jam’iyyar PDP ta samu.”

Shugaban kasa ya samu rahoton sirri wanda ya nuna wadansu ‘yan jam’iyyar ba a kyautata masu ba, suna shirin barin jam’iyyar su koma wasu jam’iyyun adawa.

“Salon farko na su shi ne su samar da matsala cikin jam’iyyar APC idan an yi sabon zaben Shugabannin jam’iyyar.Domin maganin hakan, hanya mafita ita ce kada ayi zaben Shugabannin jam’iyyar,da kuma zaben kasa na jam’iyyar kafin babban zaben 2027.

“Hankalin sa kwance yake wajen tabbatar da babu wata matsala cikin jam’iyya,da kuma hana yiyuwar rigingimun bayan zabe wadanda suna iya kawo koma- baya. Ci gaba da wadannan Shugabannin ita ce mafita kuma zai taimaka wajen samun kwanciyar hankali kamar yadda majiyar ta ce”.

An samu labarin cewa jam’iyyar tana son ta amince da wata doka tunda har yanzu ba a bada sanarwa game da zaben kasa wanda za a ci gaba da tafiya da Shugabannin da ake da su a ci gaba da tafiya da su,tun daga na kasa har zuwa ta karshe ta matakin mazabar Kansila wato ward ke nan.

Matakin zai kara karfin Tinubu kan yadda taswirar jam’iyyar ta ke da kuma zabubbukan fidda gwani.

“Jam’iyyar ta shirya yadda zata zabi Shugabannin ta wanda a ranar ce, wani zai bada shawarar cewa a ci gaba da tafiya da Shugabnnin da ake fara tafiyar da su,tun daga na kasa har zuwa Ward har sai bayan babban zabe na shekarar 2027 kamar yadda bayanin ya nuna”.

Wadanda ake damawa da su a jam’iyya sun ce matakin shi ne abinda aka fi amincewa da shi, watao kwamitin zartarwar kasa na jam’iyyar ya amince da yadda Ganduje ya tafiyar da aikinsa tare da kwamitin gudanarwar sa.Matakin ya amince ne da yadda suka iya tafiyar da jam’iyyar duk kuwa da ta fuskanci matsaloli ma su yawa.Duk da hantarar da suka rika fama da ita sai da suka yi duk yadda suka iya suka samu aka amince da shi ne dantakarar ta na Shugaban kasa a shekarar 2027 ba tare da bata wani lokaci ba.

Hakanan ma ‘yan majalisun Dattawa dana Wakilai na jam’iyyar suma za su amfana da tsarin jam’iyyar su sake tsayawa ba tare da wata hamayya ba.

“Akwai maganar amincewa a jam’iyya kan lamarin amincewa da sa ita jam’iyyar ta sa kanta yin wani abinda zai iya kawo masu ko mata matsala. Yawancin ‘yan jam’iyyar da suke majalisun Dattawa da na Wakilai wadanda suka nunawa jam’iyyar ladabi da shi Shugaban kasa,ba sai sun tsaya sun fuskanci zabubbukan tantance gwani ba.Maimakon haka ma dama ce kawai za a basu su, su sake tsayawa takara ba tare da wata matsala ba sais u sake komawa kujerar tasu,”cewar wani babban kusa a jam’iyyar da baya son a ambaci sunansa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Shugabannin jam iyyar a ci gaba da tafiya zaben fidda gwani jam iyyar da na jam iyyar jam iyyar su jam iyyar ta a jam iyyar

এছাড়াও পড়ুন:

Wata Kungiyar Ta Bukaci Shugaban Kasa Ya Cika Alkwarin Marigayi Shugaba Buhari Game Da Shehu Usman Aliyu Shagari

A wani roko da wata kungiya da aka fi sani da Sokoto Heritage Reloaded Initiative ta yi kira ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da ya cika alkawarin da tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya dauka a lokacin wata ziyarar aiki da ya kai a jihar.

 

An yi wannan roko ne a yayin wani taron manema labarai da aka gudanar a jihar Sokoto, inda shugaban kungiyar Farfesa Uthman Abdulqadir, ya jaddada muhimmancin girmama abubuwan da Shagari ya bari.

 

Ya tuna cewa shugaba Buhari ya yi wannan alkawari ne a ziyarar da ya kai Sokoto.

 

Farfesa Uthman ya bayyana irin rawar da Shehu Shagari yake takawa wajen ciyar da ilimi gaba a Najeriya, inda ya bayyana cewa ya taka rawa wajen aza harsashin kafa Budaddiyar Jami’ar Nijeriya.

 

Ya bayyana Shagari ba wai kawai shugaba ba, a’a a matsayin alama ce ta tawali’u, rikon amana da kishin kasa, mutumin da ya sadaukar da rayuwarsa wajen yi wa kasarsa hidima.

 

Farfesa Uthman ya bayyana kwarin guiwar cewa shugaba Tinubu, wanda ya shahara da mutunta shuwagabannin kasa da jajircewar hadin kai, zai gane muhimmancin tunawa Shehu Shagari.

 

Ya yi imanin cewa wannan aikin zai bayyana a fili karara Tinubu a matsayin jagora mai girmama kimar tawali’u, hidima, da kishin kasa.

 

Farfesa Uthman ya jaddada cewa sanyawa wurare sunayen Dattijai ba karamin alfanu ne ga rayuwa jama’ar ba.

 

Ya bayyana shi a matsayin muhimmin kayan aiki don ilimi, zaburarwa, da kuma kiyaye dabi’un da suka dace da al’ummomin yanzu da na gaba.

 

NASIR MALAL

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ruwa da iska sun kashe mutum 5, sun raba sama da 5,000 da muhallansu a Yobe
  • Ruwa da iska sun kashe mutum, sun raba sama da 5,000 da muhallansu a Yobe
  • Nentawe Yilwatda ne zai zama sabon shugaban APC na kasa
  • An Kaddamar Da Bikin BIRTV2025 A Beijing
  • Tinubu Ya Tattauna da Gwamnonin APC Kafin Muhimmin Taron NEC
  • 2027: Obi zai iya takara ba tare da ni ba — Datti Baba-Ahmed
  • NAJERIYA A YAU: Yadda tsadar taki ke hana noman masara da shinkafa
  • A tsananta hukunci kan masu dukan mata — Sarki Sanusi
  • Wata Kungiyar Ta Bukaci Shugaban Kasa Ya Cika Alkwarin Marigayi Shugaba Buhari Game Da Shehu Usman Aliyu Shagari
  • APC Ta Zabi Kamilu Sa’idu A Matsayin Dan Takarar Kaura Namoda Ta Kudu A Zamfara