A kwanan nan ne sakatare janar na kungiyar ASEAN Kao Kim Hourn ya bayyana a wata hirar da ya yi da wakilin babban gidan rediyo da talibijin na kasar Sin na CMG cewa, nasarorin da Sin ta samu ta fuskar ci gaba ba sakamakon ‘siddabaru’ ba ne, illa sakamakon aiki tukuru kuma mai dorewa.

Kao Kim Hourn, wanda ya ziyarci kasar Sin sau da dama, ya yi tsokaci kan abubuwan da ya gani a wadannan ziyarce-ziyarcensa.

Ya bayyana cewa, tafiya daga filin jirgin sama zuwa tsakiyar gari, ya shaida yadda kasar Sin take da tsabta, da koren muhalli, da tsaro, da duk sakamakon ci gabanta na zahiri. Abin ban mamaki ne ganin yadda kasar Sin ta canza a cikin ‘yan shekarun nan. Abubuwan da ya gani a kasar Sin a cikin ‘yan shekarun nan sun matukar bambanta da abubuwan da ya gani lokacin da ya ziyarci kasar Sin a shekarun 1990.

Ya jaddada cewa, irin wadannan sauye-sauyen na nuna gagarumin kokari na bayan fage. Kana samun ci gaba yana bukatar aiki tukuru. Kao ya bayyana cewa, ci gaban da kasar Sin ta samu ne ba ta hanyar siddabaru ba, ta samu ne a sakamakon namijin kokarin da shugabannin kasar Sin da jama’arta suka yi. Ya kuma kara da cewa, ci gaban kasa yana bukatar kuzari mai yawa, da nagartaccen jagoranci, da dimbin albarkatu, da jajircewar al’ummarta. Kasar Sin misali ce ga hakan. (Mohammed Yahaya)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kasar Sin ta a kasar Sin

এছাড়াও পড়ুন:

DAGA LARABA: Asarar Da Hausawa Ke Tafkawa Sakamakon Bacewar Tatsuniya

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Tatsuniya wata hanya ce ta ilmantarwa da bayar da tarbiyya da kuma koyar da al’adu da halaye na gari a tsakanin Hausawa.

Tatsuniyoyi na ɗauke da darussa na rayuwa, suna kuma koya wa yara da manya jarumta da tausayi da sauran dabi’u kyawawa.

Sai dai a yayin da duniya take sauyawa, ba kasafai matasa suke sha’awar sauraron tatsuniya ba.

NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya DAGA LARABA: Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin Arewa

Wannan ne batun da shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi nazari a kai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Najeriya Wajen Yin Watsi Da Kariyar Cinikayya Da Yin Adawa Da Danniya Da Cin Zarafi
  • Yanayin Rudani Na Tsawon Kwanaki 100 Kashedi Ne Ga Amurka
  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Tsara Nagartaccen Shirin Raya Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’umma Tsakanin 2026-2030
  • Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
  • DAGA LARABA: Asarar Da Hausawa Ke Tafkawa Sakamakon Bacewar Tatsuniya
  • Gwamna Namadi Ya Nada Aisha Mujaddadi Sabuwar Shugabar Hukumar InvestJigawa
  • Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
  • An dawo da wutar lantarki a Sifaniya da Portugal
  • Shugaban Kungiyar Hizbullah Ya Abbaci Abubuwa 3 Wadanda Yakamata Kasar Ta Maida Hankali A Kansu
  • Iran Da Rasha Sun Jaddada Yin Aiki Tare A Fagen Kiwon Lafiya