Aminiya:
2025-07-09@05:28:07 GMT

Mutumin da girgizar ƙasa ta razana ya shekara 2 yana zaune a cikin kogo

Published: 23rd, March 2025 GMT

Wani ɗan ƙasar Turkiyya da ya rasa gidansa sakamakon wata gagarumar girgizar ƙasa a shekarar 2023, ya shafe shekara biyu yana zaune shi kadai a cikin wani ƙaramin kogo saboda yana ganin ya fi kowane gini da mutum zai yi karko.

 A watan Fabrairun 2023, Kudancin Turkiyya ya fuskanci ibtila’in girgizar kasa mai karfin 7.

8 da ta yi sanadiyyar mutuwar dubun-dubatar mutane tare da mayar da daukacin unguwanni tamkar kufai.

An yi wa wata karya tiyatar ceton rai Dakatar da Gwamnan Ribas zubar da ƙimar Nijeriya ne a idon duniya — Jonathan

Ali Bozoğlan, mahaifin ‘ya’ya uku daga lardin Hatay da ke kudancin kasar, ya rasa gidansa sakamakon girgizar kasar da aka yi a ranar 6 ga watan Fabrairu 2023.

Duk da cewa shi da iyalinsa sun tsira ba tare da wata matsala ba, Ali ya firgita da girgizar kasar har ya yanke shawarar ba ya son zama a ginin da mutum ya yi.

Maimakon haka, sai ya sami wani karamin kogo da zai iya zama lafiya a wajen birnin, inda ya mayar da shi gida.

Kodayake ya kasa shawo kan iyalinsa su hadu da shi don zama a cikin kogon da ba a saba gani ba, sai dai ya yi ikirarin cewa yana farin ciki kuma yana cikin kwanciyar hankali a inda yake.

Ali Bozoğlan ya shaida wa kafar yada labarai ta TGRT Haber cewa, “Na shafe shekara 2 ina zaune a nan bayan girgizar kasar kuma na sami kwanciyar hankali a cikin wannan kogon.

“Wannan kogon ya wanzu tsawon dubban shekaru kuma bai rushe ba.”

Bayan da an samu labarin yadda mutumin yake rayuwa, sai Hakimin Defne ya ba shi wata kwantenar gida mai kyau a wani wuri kusa da birnin, amma Ali ya so ya nisantar da kansa da birni mai cike da cunkoson jama’a, domin ya saba da rayuwar kwanciyar hankali a cikin karamin kogon nasa.

“Ina wanke kwanukan abincina da yin wanki da kuma yin abincin da zan ci. Ina yin kyakkyawar rayuwa a cikin kogon,” in ji Ali.

“Ba ni da kowa kuma ina hulda da yanayi. Mutanen da ba su da ilimi suna yin munanan maganganu game da rayuwata a cikin kogon.

“Domin ba sa zama da ni, suna magana da ni, kuma ba su san ni ba, suna yin kalamai daban-daban.”

 Ali ya yarda cewa zama shi kadai a cikin kogo bai dace ba. Domin wuri ne mai zafi sosai a lokacin hunturu da sanyi da rani, yana jawo macizai da beraye, amma duk da haka ya saba da shi.

Haka kuma ya so ya sami ya rika shiga bandaki da samun ruwan sha, amma ba zai yiwu ba.

Yanzu ya shirya saka na’urorin samar da lantarki ta hasken rana domin ya iya sarrafa injin wanki da firinjinsa, amma ko da mafarkinsa bai zama gaskiya ba, ba zai yi watsi jin dadin kogon nasa ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Girgizar kasa Turkiyya

এছাড়াও পড়ুন:

An ƙayyade maki da shekarun shiga jami’a a Nijeriya

Hukumar shirya jarrabawar shiga jami’o’i ta Nijeriya (JAMB) ta amince da maki 150 a matsayin mafi ƙanƙantar makin da za a bai wa ɗalibai guraben karatu a jami’o’in ƙasar.

Hukumar ta ɗauki matakin ne a taronta kan tsarin bayar da guraben karatu na 2025 da ta gudanar a babban ɗakin taro na Bola Ahmed Tinubu da ke Abuja.

An ceto mutum 6 daga hannun masu garkuwa a Kebbi Gwamnatin Tinubu na shirya mana zagon ƙasa — ADC

Haka kuma, ta ce mafi ƙanƙantar maki ga kwalejojin koyon aikin jinya shi ne 140, yayin da ta ƙayyade makin samun gurbin kwalejojin ilimi da na koyon aikin noma a 100.

Alƙaluma dai sun tabbatar da cewa an samu gagarumar faɗuwa a jarawabar JAMB da aka rubuta a wannan shekara.

A yayin da JAMB ke ƙayyade mafi ƙanƙantar makin samun gurbin karatu, ita ma Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya ta ƙayyade shekara 16 a matsayin mafi ƙanƙantar shekaru da ɗalibi zai kai kafin a ba shi gurbin karatu a jami’o’in ƙasar.

Ministan Ilimi, Tunji Alausa ne ya bayyana hakan a wannan Talatar a yayin taron tsara fitar da guraben karatu na 2025 a ƙasar da aka gudanar a babban ɗakin taro na Bola Ahmed Tinubu da ke Abuja.

Za a shigar da ƙa’idar cika shekara 16 a cikin manhajar Hukumar JAMB da ke tantance ƙa’idojin bayar da gurbin karatu.

Haka kuma, Ministan ya ce za a yi la’akari da ɗaliban da za su cika shekara 16 ranar 31 ga watan Agustan 2025.

A bayan nan dai ana ta cece-kuce kan bai wa ƙananan yara guraben karatu a jami’o’in ƙasar, wani abu da masana ke cewa zai shafi fahimtarsu da kuma yadda za su iya jure wa wahalhalun karatun jami’a.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An ƙayyade maki da shekarun shiga jami’a a Nijeriya
  • Gwamnatin Tinubu na shirya mana zagon ƙasa — ADC
  • HKI Tana Tana Son Ci Gaba Da Yaki Kuma Trump Yana Tare Da Shi
  • Olubadan Na Ibadan Ya Rasu Yana Da Shekara 90
  • Ƴan Arewa Za Su Yi Murna Idan Na Zama Shugaban Ƙasa — Peter Obi
  • Olubabadan ya rasu yana da shekara 90
  • Bincike ya nuna ’yan Najeriya ba su gamsu da gwamnatin Tinubu ba
  • Taron Ashura Ya Zama Lamari Mafi Girma Da Cinkoson Jama’a, Inda Masu Ziyara Daga Sassan Duniya Suka Isa Karbala
  • An kama ɗan Najeriya yana taimaka wa Rasha a yaƙinta da Ukraine
  • Imam Khaminae Ya Halarci Makokin Ashoora A Gidansa A Tehran