Zaunannen wakilin Sin dake ofishin MDD a Geneva da sauran kungiyoyin kasa da kasa a kasa Switzerland Chen Xu ya yi jawabi a gun taron hukumar kare hakkin dan Adam ta MDD karo na 58 kan batun kare hakkin dan Adam na kasa da kasa, inda ya yi bayani game da tunanin Sin kan kare hakkin dan Adam da kin amincewa da siyasantar da batutuwan da suka shafi hakkin dan Adam.

Chen Xu ya yi nuni da cewa, ana bukatar bin ra’ayin bangarori daban daban da tunanin kare hakkin dan Adam da yin hadin gwiwa mai amfani don sa kaimi ga raya sha’anin kare hakkin dan Adam. Wasu kasashe sun yi amfani da dalilin kare hakkin dan Adam wajen tsoma baki cikin harkokin cikin gida na wasu kasashe, da yin amfani da ma’auni biyu, da tada rikice-rikice, da kuma kakabawa wasu takunkumi daga bangare daya. Wadannan kasashe sun kau da kai daga yanayinsu na keta hakkin dan Adam, da maida kansu a matsayin alkalan kare hakkin dan Adam, da zargin wasu kasashe kan yanayin kare hakkin dan Adam, sun kawo illa ga tsarin kare hakkin dan Adam na MDD.

Chen Xu ya kara da cewa, kasar Sin ta tsaya tsayin daka kan tunanin kare hakkin dan Adam bisa tushen kyautatawa jama’a, da kiyaye tabbatar da moriyar jama’a. Kasar Sin tana girmama jama’ar sauran kasashe wajen zabar hanyar raya hakkin dan Adam da kansu, da kuma samar da gudummawa wajen raya tsarin siyasa na duk dan Adam baki daya. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kare hakkin dan Adam

এছাড়াও পড়ুন:

Xi Jinping Ya Ziyarci Sabon Bankin Raya Kasashen BRICS

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Najeriya Wajen Yin Watsi Da Kariyar Cinikayya Da Yin Adawa Da Danniya Da Cin Zarafi
  • Kar A Mika Wuya Ga “Damisar Takarda”
  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Tsara Nagartaccen Shirin Raya Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’umma Tsakanin 2026-2030
  • Saudiya Ta Yi Allawadai Da Kissan Kiyashin Da HKI Take Yi A Gaza A Gaban Kutun ICJ
  • Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara 
  • Kungiyar Amnesty International Ta Kafa Hujja Kan Ta’asar’Yan Sahayoniyya A Gaza
  • Xi Jinping Ya Ziyarci Sabon Bankin Raya Kasashen BRICS
  • Sin Ta Harba Sabon Tauraron Dan Adam Na Ayyukan Sadarwa
  • Babu Wata Tattaunawa Tsakanin Sin Da Amurka Game Da Batun Haraji
  • Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi