Mazauna unguwar da asibitin kula da ido ta kasa yake wato Mahuta da ke jihar Kaduna sun amince da Gwamna Uba Sani ya zarce karo na biyu, biyo bayan warware takaddamar filaye da aka dade ana yi wanda ya yi sanadiyar rushe gidaje da dama a gwamnatin da ta gabata.

Wannan na zuwa ne bayan gwamnatin jihar Kaduna ta hannun hukumar kula da bayanan kasa ta jihar Kaduna (KADGIS) ta bayar da shedar mallakar filayen sama da 300 ga al’ummar da rusau da aka yi a zamanin tsohon Gwamna Nasir El-Rufai ya shafa.

Da yake jawabi a madadin mazauna yankin, Kanar Haruna Idris Zaria mai ritaya, ya yabawa Gwamna Sani bisa abin da ya bayyana a matsayin tsarin sa na tausayi da kishin al’umma.

Ya ce matakin da gwamnan ya dauka cikin gaggawa da tsari ba kawai ya kawo karshen rashin tabbas na tsawon shekaru ba har ma ya dawo da kwarin gwiwar mazauna yankin ga gwamnati.

“Mun sha wahala na tsawon shekaru, ba tare da sanin ko gidajenmu za su taba zama namu ba, amma Gwamna Uba Sani ya ba mu goyon bayan doka da kwanciyar hankali, abin da ya yi ya nuna shugaba mai saurare da tausayawa,” in ji Zaria.

Mazauna yankin sun ce bayar da takardun mallakar filaye ya rage tashe-tashen hankula a tsakanin al’ummar Mahuta, inda aka dade ana jira a tabbatar da mallakar kadarorin.

Mazauna yankin sun ce bayar da takardun mallakar filaye ya rage tashe-tashen hankula a tsakanin al’ummar Mahuta, inda aka dade ana jira a tabbatar da mallakar kadarorin.

Har ila yau, sun yaba wa Gwamna Sani da ya dakatar da duk wani rusau na gidaje, inda ya baiwa iyalai damar rayuwa ba tare da fargabar gudun hijira ba.

“Wannan ya wuce nasara ta doka, na jin kai ne,” in ji wani mazaunin.

“Gwamnan ya dawo mana da mutunci da kwanciyar hankali a rayuwarmu.”

An yaba da yadda Gwamna Sani ya tafiyar da rikicin filaye na Mahuta a matsayin abin koyi wajen magance rikicin filaye a birane.

An bayyana shirin a matsayin shaida na yadda gwamnatinsa ta himmatu wajen tabbatar da adalci, gudanar da mulki tare da kare hakkin talakawan kasa.

Masu lura da al’amuran siyasa na ganin cewa, wannan goyon bayan da aka samu daga tushe na iya karawa Gwamna Sani karfin guiwa a siyasance gabanin zabe mai zuwa, musamman idan aka yi la’akari da yadda al’amuran mallakar filaye ke damun garuruwan Kaduna.

Ga mazauna Mahuta kuwa, amincewar su ya samo asali ne daga godiya ba siyasa ba.

“Ya sami amanarmu ta hanyar yin abin da wasu ba za su yi ba,” in ji Kanar Zaria.

“Mun yi imanin ya cancanci wa’adi na biyu don ci gaba da kyakkyawan aiki,” in ji masu lura da al’amuran.

Umar S Fada

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Filaye

এছাড়াও পড়ুন:

Zargin Kisan Kiristoci: Maganar Trump a kan Najeriya tsagwaron ƙarya ce — Shehu Sani

Tsohon Sanatan Kaduna ta Tsakiya, Shehu Sani, ya soki Shugaban Amurka, Donald Trump, bisa kiran Najeriya “ƙasa mai matsala ta musamman” kan zargin yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi.

Sani, ya ce kalaman Trump sun samo asali ne daga bayanan da ba su da tushe, da wasu mutane suka ba shi domin su tayar da fitina a Najeriya.

Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa Zaɓen Tanzania: Shugaba Samia ta yi tazarce da kashi 97 an ƙuri’u

A ranar Juma’a ne, Trump ya wallafa rubutu a shafinsa na sada zumunta cewar Kiristanci yana cikin hatasri a Najeriya.

Ya yi iƙirarin cewa ’yan ta’adda sun kashe dubban Kiristoci, amma ya ce Amurka za ta yi duk mai yiwuwa wajen “ceto Kiristoci” a Najeriya da wasu ƙasashe.

Shehu Sani, ya mayar da martani da cewa wannan magana ba gaskiya ba ce, domin matsalar tsaro a Najeriya ba ta da nasaba da addini.

Ya ce Musulmai da Kiristoci dukkaninsu suna fuskantar hare-haren’yan ta’adda da garkuwa da su.

“Wannan zargi ƙarya ne. ’Yan ta’adda da ’yan bindiga a Najeriya suna kashe mutane ba tare da la’akari da addininsu ba. Wannan abin na faruwa tun kusan shekaru 15 da suka wuce,” in ji shi.

Sani, ya ƙara da cewa, saboda yawan Musulmai da Kiristoci a Najeriya, ba zai yiwu addini ɗaya ya zalunci ɗaya ba.

“Idan aka duba yadda Musulmai da Kiristoci suke kusan daidai a Najeriya, ba zai yiwu ɗaya ya zalunci ɗaya ba. Najeriya kamar zaki da damisa ce, dukkanin ɓangarorin suna da ƙarfi,” in ji shi.

Ya zargi waɗanda suka zuga Trump da amfani da rikice-rikicen cikin gida na Najeriya.

“Trump ya samu bayanan ƙarya daga mutanen da ke son raba Najeriya domin su ci moriya daga wannan,” in ji shi.

“Wannan makirci da aka yi wa ƙasar nan ba zai yi nasara ba.”

Sani, ya roƙi ƙasashen duniya su taimaka wa Najeriya wajen yaƙar ta’addanci, maimakon yaɗa labaran ƙarya.

“Najeriya na buƙatar taimako da haɗin kai wajen shawo kan matsalar tsaro, kamar sauran ƙasashen da ke fama da ta’addanci,” a cewarsa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Kasar Qatar Ta Ba Da Tallafin Gaggawa Ga Al’ummar Sudan Bayan Gumurzun El-Fasher
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • Zargin Kisan Kiristoci: Maganar Trump a kan Najeriya tsagwaron ƙarya ce — Shehu Sani
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara
  • Kofin kofi mafi tsada a duniya ya shiga kasuwa a kan Naira miliyan 1.5m
  • An Tube Yarima Mai Jiran Gado Na Birtaniya Bayan Da Aka Tabbatar Da Laifinsa
  • Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
  • Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai