Gwamna Uba Sani Ya Samu Goyon Bayan Mazauna Mahuta Bayan Warware Rikicin Filaye
Published: 5th, June 2025 GMT
Mazauna unguwar da asibitin kula da ido ta kasa yake wato Mahuta da ke jihar Kaduna sun amince da Gwamna Uba Sani ya zarce karo na biyu, biyo bayan warware takaddamar filaye da aka dade ana yi wanda ya yi sanadiyar rushe gidaje da dama a gwamnatin da ta gabata.
Wannan na zuwa ne bayan gwamnatin jihar Kaduna ta hannun hukumar kula da bayanan kasa ta jihar Kaduna (KADGIS) ta bayar da shedar mallakar filayen sama da 300 ga al’ummar da rusau da aka yi a zamanin tsohon Gwamna Nasir El-Rufai ya shafa.
Da yake jawabi a madadin mazauna yankin, Kanar Haruna Idris Zaria mai ritaya, ya yabawa Gwamna Sani bisa abin da ya bayyana a matsayin tsarin sa na tausayi da kishin al’umma.
Ya ce matakin da gwamnan ya dauka cikin gaggawa da tsari ba kawai ya kawo karshen rashin tabbas na tsawon shekaru ba har ma ya dawo da kwarin gwiwar mazauna yankin ga gwamnati.
“Mun sha wahala na tsawon shekaru, ba tare da sanin ko gidajenmu za su taba zama namu ba, amma Gwamna Uba Sani ya ba mu goyon bayan doka da kwanciyar hankali, abin da ya yi ya nuna shugaba mai saurare da tausayawa,” in ji Zaria.
Mazauna yankin sun ce bayar da takardun mallakar filaye ya rage tashe-tashen hankula a tsakanin al’ummar Mahuta, inda aka dade ana jira a tabbatar da mallakar kadarorin.
Mazauna yankin sun ce bayar da takardun mallakar filaye ya rage tashe-tashen hankula a tsakanin al’ummar Mahuta, inda aka dade ana jira a tabbatar da mallakar kadarorin.
Har ila yau, sun yaba wa Gwamna Sani da ya dakatar da duk wani rusau na gidaje, inda ya baiwa iyalai damar rayuwa ba tare da fargabar gudun hijira ba.
“Wannan ya wuce nasara ta doka, na jin kai ne,” in ji wani mazaunin.
“Gwamnan ya dawo mana da mutunci da kwanciyar hankali a rayuwarmu.”
An yaba da yadda Gwamna Sani ya tafiyar da rikicin filaye na Mahuta a matsayin abin koyi wajen magance rikicin filaye a birane.
An bayyana shirin a matsayin shaida na yadda gwamnatinsa ta himmatu wajen tabbatar da adalci, gudanar da mulki tare da kare hakkin talakawan kasa.
Masu lura da al’amuran siyasa na ganin cewa, wannan goyon bayan da aka samu daga tushe na iya karawa Gwamna Sani karfin guiwa a siyasance gabanin zabe mai zuwa, musamman idan aka yi la’akari da yadda al’amuran mallakar filaye ke damun garuruwan Kaduna.
Ga mazauna Mahuta kuwa, amincewar su ya samo asali ne daga godiya ba siyasa ba.
“Ya sami amanarmu ta hanyar yin abin da wasu ba za su yi ba,” in ji Kanar Zaria.
“Mun yi imanin ya cancanci wa’adi na biyu don ci gaba da kyakkyawan aiki,” in ji masu lura da al’amuran.
Umar S Fada
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Filaye
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Ba Zai Taɓa Tauye ’Yancin Kafafen Yaɗa Labarai Ba, In ji Ministan Yaɗa Labarai
Ya ƙara da cewa, “Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ba zai taɓa, a kowace hanya ko salo, tauye ko hana ci gaban aikace-aikacen kafafen yaɗa labarai a wannan ƙasa ba. Amma dole ne mu duka ‘yan jarida da masu aikin yaɗa labarai mu haɗa kai, mu bi wannan hanya mai sarƙaƙiya, mu tabbatar da cewa al’umma tana ci gaba da zama cikin haɗin kai, yayin da muke riƙe shugabanni da gwamnati da alhakin aikin su.”
Idris ya jaddada muhimmancin kafafen yaɗa labarai wajen kula da tsarin dimokiraɗiyya, inda ya shawarci ’yan jarida da su kula da rawar da suke takawa domin kada su zama abin da zai jawo ruɗani ko rikici a cikin al’umma.
“A yayin da kuke yin wannan aiki, kuna da babban nauyi na riƙe gwamnati da shugabanni da alhakin aikin su. Amma ko da kuna yin hakan, dole ne ku sani cewa saboda matsayin ku na musamman da rawar da kuke takawa, za ku iya taimaka wa ƙasa matuƙa, amma idan ba a yi taka-tsantsan ba, ayyukan ku na iya cutar da al’umma,” inji shi.
Ya bayyana buƙatar sanin ya kamata da hankali wajen tantance sahihin bayani daga wanda zai iya ɓata zaman lafiya ko raba kan al’umma.
Ministan ya ce duk da ƙalubalen da ke fuskantar fannin yaɗa labarai, akwai haske a gaba domin kafafen sun ci gaba da nuna jajircewa da ɗorewa.
Ya kuma bayyana cewa ba shi ba ne Shugaban kamfanin jaridar Blueprint ba tun bayan da aka naɗa shi Minista.
“Ba ni ne shugaban jaridar Blueprint ba yanzu. Ni ma baƙo ne aka gayyata zuwa wannan taro. Na san cewa a baya ni ne ke gaba wajen shirya wannan taron na Blueprint, musamman tun lokacin da aka kafa ta shekaru 14 da suka wuce. Dole ne in gode wa waɗanda aka gayyata su haɗu da ni a watan Mayun 2005 domin tunanin fara jaridar Blueprint: Malam Ibrahim Sheme; Manajan Darakta, Malam Salisu Umar; Shugabar Kwamitin Tace Labarai, Hajiya Zainab Okino, da dukkan ma’aikatan jaridar Blueprint.
“Na gode da cigaba da tafiyar da abin da muka faro cikin nasara. Na shekara guda ban ziyarci ofishin ba, amma ina ganin lokaci ya yi da zan yi hakan. Ina so in ga ko har yanzu kuna ci gaba da tafiyar da abin da muka faro. Ina alfahari kuma ina farin ciki da cewa abin da muka fara ya ci gaba da bunƙasa,” inji shi.
Idris ya taya waɗanda suka samu kyaututtuka murna, inda ya bayyana cewa ba a yi masu kyautar bisa wani son zuciya ko tasiri daga wani waje ba, sai hukuncin jaridar ne kaɗai.
Cikin manyan baƙin da suka halarci taron akwai Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume; Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin; Ministan Ma’adanai, Dakta Dele Alake; Ministan Raya Noman Dabbobi, Idi Mukhtar Maiha; Etsu Nupe, Mai Martaba Alhaji Yahaya Abubakar, da babban baƙon jawabi na taron, Farfesa Attahiru Jega.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp