Mazauna unguwar da asibitin kula da ido ta kasa yake wato Mahuta da ke jihar Kaduna sun amince da Gwamna Uba Sani ya zarce karo na biyu, biyo bayan warware takaddamar filaye da aka dade ana yi wanda ya yi sanadiyar rushe gidaje da dama a gwamnatin da ta gabata.

Wannan na zuwa ne bayan gwamnatin jihar Kaduna ta hannun hukumar kula da bayanan kasa ta jihar Kaduna (KADGIS) ta bayar da shedar mallakar filayen sama da 300 ga al’ummar da rusau da aka yi a zamanin tsohon Gwamna Nasir El-Rufai ya shafa.

Da yake jawabi a madadin mazauna yankin, Kanar Haruna Idris Zaria mai ritaya, ya yabawa Gwamna Sani bisa abin da ya bayyana a matsayin tsarin sa na tausayi da kishin al’umma.

Ya ce matakin da gwamnan ya dauka cikin gaggawa da tsari ba kawai ya kawo karshen rashin tabbas na tsawon shekaru ba har ma ya dawo da kwarin gwiwar mazauna yankin ga gwamnati.

“Mun sha wahala na tsawon shekaru, ba tare da sanin ko gidajenmu za su taba zama namu ba, amma Gwamna Uba Sani ya ba mu goyon bayan doka da kwanciyar hankali, abin da ya yi ya nuna shugaba mai saurare da tausayawa,” in ji Zaria.

Mazauna yankin sun ce bayar da takardun mallakar filaye ya rage tashe-tashen hankula a tsakanin al’ummar Mahuta, inda aka dade ana jira a tabbatar da mallakar kadarorin.

Mazauna yankin sun ce bayar da takardun mallakar filaye ya rage tashe-tashen hankula a tsakanin al’ummar Mahuta, inda aka dade ana jira a tabbatar da mallakar kadarorin.

Har ila yau, sun yaba wa Gwamna Sani da ya dakatar da duk wani rusau na gidaje, inda ya baiwa iyalai damar rayuwa ba tare da fargabar gudun hijira ba.

“Wannan ya wuce nasara ta doka, na jin kai ne,” in ji wani mazaunin.

“Gwamnan ya dawo mana da mutunci da kwanciyar hankali a rayuwarmu.”

An yaba da yadda Gwamna Sani ya tafiyar da rikicin filaye na Mahuta a matsayin abin koyi wajen magance rikicin filaye a birane.

An bayyana shirin a matsayin shaida na yadda gwamnatinsa ta himmatu wajen tabbatar da adalci, gudanar da mulki tare da kare hakkin talakawan kasa.

Masu lura da al’amuran siyasa na ganin cewa, wannan goyon bayan da aka samu daga tushe na iya karawa Gwamna Sani karfin guiwa a siyasance gabanin zabe mai zuwa, musamman idan aka yi la’akari da yadda al’amuran mallakar filaye ke damun garuruwan Kaduna.

Ga mazauna Mahuta kuwa, amincewar su ya samo asali ne daga godiya ba siyasa ba.

“Ya sami amanarmu ta hanyar yin abin da wasu ba za su yi ba,” in ji Kanar Zaria.

“Mun yi imanin ya cancanci wa’adi na biyu don ci gaba da kyakkyawan aiki,” in ji masu lura da al’amuran.

Umar S Fada

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Filaye

এছাড়াও পড়ুন:

An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

Cikin kwanaki uku na hutun bikin Dragon Boat na kasar Sin, an samu karuwar tafiye-tafiye zuwa ketare da suka kusa miliyan 5.91. Masu tafiye-tafiye sun karu matuka tun daga Asabar har jiya Litinin, inda aka samu karuwar kaso 2.7 bisa dari kan adadin da aka samu a bara.

Alkaluman da hukumar lura da shige da ficen al’umma ta kasar Sin ta fitar a Talatar nan, sun nuna karuwar baki masu shigowa kasar Sin daga ketare, musamman wadanda suka ci gajiyar manufar nan ta kawar da bukatar biza. Albarkacin wannan manufa, adadin baki daga ketare da suka shigo kasar Sin yayin ranaku uku na bikin ya kai 231,000, adadin da ya karu da kaso 59.4 bisa dari kan na shekarar bara.

A bana an gudanar da bikin Dragon Boat ne tun daga ranar Asabar 31 ga watan Mayu zuwa jiya Litinin 2 ga watan Yuni. (Mai Fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnan Akwa Ibom ya sauya sheƙa daga PDP zuwa APC
  • Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano
  • Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno
  • Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba
  • Tinubu ya gana da Fubara a Legas
  • Medvedev : babu makawa Rasha za ta mayar da martani mai zafi ga hare-haren kyiv
  • Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG
  • An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin
  • Aragchi: Iran Tana Goyon Bayan Tattaunawa Saboda Hadin Kai Tsakanin Mutanen Lebanon