Mazauna unguwar da asibitin kula da ido ta kasa yake wato Mahuta da ke jihar Kaduna sun amince da Gwamna Uba Sani ya zarce karo na biyu, biyo bayan warware takaddamar filaye da aka dade ana yi wanda ya yi sanadiyar rushe gidaje da dama a gwamnatin da ta gabata.

Wannan na zuwa ne bayan gwamnatin jihar Kaduna ta hannun hukumar kula da bayanan kasa ta jihar Kaduna (KADGIS) ta bayar da shedar mallakar filayen sama da 300 ga al’ummar da rusau da aka yi a zamanin tsohon Gwamna Nasir El-Rufai ya shafa.

Da yake jawabi a madadin mazauna yankin, Kanar Haruna Idris Zaria mai ritaya, ya yabawa Gwamna Sani bisa abin da ya bayyana a matsayin tsarin sa na tausayi da kishin al’umma.

Ya ce matakin da gwamnan ya dauka cikin gaggawa da tsari ba kawai ya kawo karshen rashin tabbas na tsawon shekaru ba har ma ya dawo da kwarin gwiwar mazauna yankin ga gwamnati.

“Mun sha wahala na tsawon shekaru, ba tare da sanin ko gidajenmu za su taba zama namu ba, amma Gwamna Uba Sani ya ba mu goyon bayan doka da kwanciyar hankali, abin da ya yi ya nuna shugaba mai saurare da tausayawa,” in ji Zaria.

Mazauna yankin sun ce bayar da takardun mallakar filaye ya rage tashe-tashen hankula a tsakanin al’ummar Mahuta, inda aka dade ana jira a tabbatar da mallakar kadarorin.

Mazauna yankin sun ce bayar da takardun mallakar filaye ya rage tashe-tashen hankula a tsakanin al’ummar Mahuta, inda aka dade ana jira a tabbatar da mallakar kadarorin.

Har ila yau, sun yaba wa Gwamna Sani da ya dakatar da duk wani rusau na gidaje, inda ya baiwa iyalai damar rayuwa ba tare da fargabar gudun hijira ba.

“Wannan ya wuce nasara ta doka, na jin kai ne,” in ji wani mazaunin.

“Gwamnan ya dawo mana da mutunci da kwanciyar hankali a rayuwarmu.”

An yaba da yadda Gwamna Sani ya tafiyar da rikicin filaye na Mahuta a matsayin abin koyi wajen magance rikicin filaye a birane.

An bayyana shirin a matsayin shaida na yadda gwamnatinsa ta himmatu wajen tabbatar da adalci, gudanar da mulki tare da kare hakkin talakawan kasa.

Masu lura da al’amuran siyasa na ganin cewa, wannan goyon bayan da aka samu daga tushe na iya karawa Gwamna Sani karfin guiwa a siyasance gabanin zabe mai zuwa, musamman idan aka yi la’akari da yadda al’amuran mallakar filaye ke damun garuruwan Kaduna.

Ga mazauna Mahuta kuwa, amincewar su ya samo asali ne daga godiya ba siyasa ba.

“Ya sami amanarmu ta hanyar yin abin da wasu ba za su yi ba,” in ji Kanar Zaria.

“Mun yi imanin ya cancanci wa’adi na biyu don ci gaba da kyakkyawan aiki,” in ji masu lura da al’amuran.

Umar S Fada

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Filaye

এছাড়াও পড়ুন:

Bayanin Bayan Taron Doha Ya Yi Kira Da A Kafa Runduwar Hadin Gwiwa Ta Kare Kai

A yau Litinin ne dai kungiyoyin kasashen musulmi da na larabawa su ka yi taron gaggawa a birin Doha na kasar Qatar da aka tattauna harin wuce gona da iri da HKI ta kai wa kasar.

Bayanin bayan taron ya kunshi bangarori mabanbanta da su ka hada da daukar matakai kwarara domin taka wa HKI birki akan ta’addancin da take yi, da kuma hanyoyin kare kai anan gaba.

 Kungiyar kasashen larabawan yankin tekun fasha ta sake jaddada muhimmancin aiki da dokar kafa rundunar hadin gwiwa ta kare kai daga duk wani wuce gona da iri daga waje.

Bugu da kari, mahalarta taron sun amince da dukar dukkanin matakan dokoki a fagen duniya domin hukunta jami’an HKI da su ka tafka laifukan yaki.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Burkina Faso: Masu Ikirarin Jihadi Sun Kashe Fararen Hula 50 A Cikin Watanni Hudu September 15, 2025 Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar September 15, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha September 15, 2025  Dan Kasar Iran Mai Kirkira Ya Sami Kyautar Yabo A Kasar China September 15, 2025 Fizishkiyan:  Wajibi Ne Musulmi Su Hada Kai Domin Dakatar Da Laifukan HKI September 15, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha September 15, 2025 Kwamitin Kolin Tsron Kasar Iran Ya Amince Da Yarjejeniyar Da Aka Cimma Da Hukumar IAEA September 15, 2025 Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar September 15, 2025 Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000 September 15, 2025 Gwamnatin Sudan Ta Ce: Babu Sulhu Da ‘Yan Tawayen Kasar Na Kungiyar Rapid Support Forces September 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
  • Iran Ta Bukaci Musulmi Su Goyi Bayan Yunkurin Kasa da Ka Na Kauracewa Isra’ila
  • Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo
  • Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
  • Bayanin Bayan Taron Doha Ya Yi Kira Da A Kafa Runduwar Hadin Gwiwa Ta Kare Kai
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
  • Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff