MDD : Gaza na cikin bala’i mafi muni tun soma yaki a Zirin a Oktoban 2023
Published: 1st, June 2025 GMT
Wani rahoto da ofishin kula da ayyukan jin kai na Majalisar Dinkin Duniya ya fitar, ya nuna cewa Gaza na fuskantar bala’i mafi muni tun soma yaki a Zirin a watan Oktoban 2023.
Wakilin Majalisar Dinkin Duniya na musamman kan hakkin bil adama a yankunan Falasdinawa da aka mamaye ya zargi gwamnatin Isra’ila da yin amfani da batun agajin jin kai da gangan domin ci gaba da aiwatar da munanan laifukan da take aikatawa a Gaza.
Francesca Albanese a cikin wata sanarwa da ta fitar ta ce: “Dukkan wadannan matakan an boye su ne a karkashin sunan agaji don karkatar da hankulan kasashen duniya.”
A wani labarin kuma Kakakin Majalisar Dinkin Duniya Stéphane Dujarric ya shaida wa manema labarai a ranar Juma’a da ta gabata cewa: Bukatun jin kai a Gaza ya karu sosai bayan kusan kwanaki 80 na hana shigar da tallafi a zirin.
‘’tallafin da ake samu a yanzu haka bai wadatar ba wajen biyan bukatun mutane sama da miliyan 2.1 da ke bukatar agajin gaggawa. » inji shi.
Adadin wadanda sukayi shahada a wannan yanki na Falasdinu tun daga ranar 7 ga watan Oktoban shekarar 2023 ya kai mutane 54,381, a cewar ma’aikatar lafiya ta Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ma’aikatar Lafiyar Sudan Ta Ce: An Dan Samu Ja Da Baya A Cutar Kwalara Da Ta Kunno Kai A Kasar
Ma’aikatar lafiyar kasar Sudan ta bayyana cewa: Ana ci gaba da daukan matakan ganin an shawo kan ci gaba da yaduwar masifar kwalara a kasar
Gidan talabijin na Al-Alam ya watsa rahoton cewa: A halin da ake ciki a fannin kiwon lafiya a birnin Khartoum fadar mulkin kasar bayan bullar cutar kwalara yana ta kokarin ya shawo kan matsalar tare da killace mutanen da suka kamu da cutar a wurare na musamman a babban birnin kasar Khartoum, rahotonni sun bayyana cewa: Cutar ta bazu cikin sauri a birnin. Sannan ma’aikatar lafiya ta Sudan da kungiyoyi da dama suna ci gaba da kokarin shawo kan cutar don kada ta zama annoba wadda za ta yadu zuwa jihohi da dama.
Wakilin gidan talabijin na Al-Alam na kasar Iran ya yi nuni da cewa: Akwai kuma jahohi da dama a yankin Darfur, wadanda wasu daga cikinsu suka kamu da cutar kwalara, inda ya ce daya daga cikin abubuwan da ke kawo wannan cuta shi ne yanayin da ake fama da shi a yankin Al-Salha, inda aka shafe fiye da wata guda ana gwabza fada tsakanin sojojin Sudan da ‘yan tawayen kasar na dakarun kai daukin gaggawa, inda gawarwakin mutane suke kwance a gefen hanya, kuma sun kwashe sama da wata guda, babu wani yunkurin kwashe su, don haka suke wari tare da gurbata yanayi, wasu gawarwakin kuma aka kai su cikin teku. Duk wannan na daya daga cikin dalilan da suka haifar da yaduwar wannan cuta, amma ta dan ja da baya, a cewar ministan lafiya na tarayya, wanda ya zo musamman Khartoum domin fayyace lamarin.