Bankin Zenith ya kasance a kan gaba tare da samun ribar naira tiriliyan 1.32 kafin a biya haraji, wanda hakan ke nuna karin kashi 67 cikin 100 daga naira biliyan 796 da aka samu a shekarar 2023.

 

Bankin GTCO ya bi sahu, inda ya fitar da ribar kashi 107.8 kafin a fara biyan haraji zuwa naira tiriliyan 1.

266, daga naira biliyan 609 na bara.

 

Har ila yau, Access Corp da UBA sun taka rawar gani sosai, inda suka samu ribar naira biliyan 867 da kuma naira biliyan 803.7, wanda ya zarce adadin da suka samu a shekarar 2023 na naira biliyan 729 da kuma naira biliyan 757.6.

 

First HoldCo ya kuma samu ribar kashi 124 cikin 100 na ribar da aka samu, daga naira biliyan 347.9 a shekarar 2023 zuwa naira biliyan 781.9 a shekarar da ta gabata.

 

Masu gudanarwa sun yi amanar cewa juriyar da fannin banki ke nunawa ba wai kawai shaida ce ga daidaitawar cibiyoyin hada-hadar kudi ba har ma da nunin damar da za a samu nan gaba, musamman ga masu saka hannun jari da ke sa ran samun kwanciyar hankali.

 

Ko da yake sun bayar da hujjar cewa, idan aka yi hasashen farashin kudin ruwa zai ragu, kuma nairar za ta kara karfi tare da rage sauyin yanayi, ribar bankunan na iya fuskantar matsin lamba a bana.

 

Duk da haka, kwararrun sun ci gaba da jajircewa kan fannin, tare da lura da cewa bankunan da ke da kakkarfan habakar lamuni da kuma dabarun samun kudin shiga maras riba, musamman wadanda ke yin amfani da ayyukan kasuwanci, da alama za su kasance masu jan hankali ga masu zuba jari.

 

Wani manazarci, Charles Abuede, ya ce ayyukan bankunan Nijeriya a cikin shekara ta 2024 suna ba da manuniya mai kyau ga abin da ke gaba a 2025.

 

Ya ce, akwai hasashen za a samu karin tagomashi sosai a bangarorin a shekarar bana, wanda a cewarsu ayyukan na kyau matuka.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: naira biliyan

এছাড়াও পড়ুন:

NiDCOM Ta Ceto ‘Yan Nijeriya 13 Da Aka Yi Safarar Zuwa Ghana Da Mali

Ta kuma yi kira da a cafke masu safarar mutane tare da fallasa sunayensu bayan an gurfanar da su a gaban kotu, domin daƙile laifi.

NiDCOM ta miƙa waɗanda aka ceto ga hukumar NAPTIP domin tantance su da kuma ci gaba da ba su kulawa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sharhin Bayan Labarai: Iran Zata Ci Gaba Da Tashe Uranium Tare Da Yarjeniya Ko Babu Ita
  • Babban Muftin Oman Ya Yi Suka Kan Taron Kungiyar Larabawa Saboda Rashin Saboda Rashin Ba Wa Gaza Muhimmanci
  • Jihar Jigawa Za Ta Sayi Motoci 36 Ga Mambobin Kungiyar NURTW
  • NiDCOM Ta Ceto ‘Yan Nijeriya 13 Da Aka Yi Safarar Zuwa Ghana Da Mali
  • Shugaban Kasar Colombia: Ayyukan Kasar Sin Sun Nuna Wani Sabon Salo Na Ci Gaban Zamantakewar Al’ummar Bil’adama
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Wani Kasurgumin Barowon Shanu Da Garkuwa Da Mutane A Kasuwar Shinge
  • Sin Ta Cimma Nasarar Gwajin Jirgin Sama Samfurin AG600
  • Fahimtar Hakikanin kasar Sin
  • Mutane 7 Sun Mutu 11Sun Jikkata A Hadarin Mota A Niger.
  • Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Nuna Wasu Manyan Fina-Finai 22