MDD : ba tabbas kan ko za’a kawar da zazzabin malaria nan da shekarar 2030
Published: 25th, April 2025 GMT
Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewa ba tabbas ko za’a iya kawar da cutar zazzabin cizon sauro nan da shekarar 2030, musamman a nahiyar Afrika.
Fiye da mutane miliyan 263 ne suka kamu da cutar a cikin 2023, kuma kusan 600,000 ne suka mutu sanadin cutar a cewar alkalumman na MDD.
Musamman a wannan lokacin da shugaban Amurka Donald Trump ya rage kashe kudaden tallafi na kasa da kasa, inji rahoton.
A cikin shekaru 25, zuba jari a yakin da ake yi da zazzabin cizon sauro ya hana kamuwa da cutar ga mutane biliyan 2 da kuma mutuwar mutane miliyan 13, musamman a Afirka.
“Akwai babbar barazana, da kuma bukatar jajircewa wajen samar da magunguna in ji Philippe Duneton, darektan Unitaid, kungiyar da ke da fafatuklar samar da magunguna na HIV, tarin fuka ko TB da kuma zazzabin cizon sauro.
Bayyanin ya fito ne gabanin zagayowar ranar duniya ta yaki da cutar zazzabin sauro yau 25 ga watan Afrilu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane
Haka kuma, ya zargi Matawalle da karɓar Naira miliyan 300 daga tsohon gwamnan Katsina, Aminu Bello Masari, don a sako ɗaliban, amma ya bai wa ‘yan bindiga miliyan 30 kacal.
APC ta ƙaryata wannan zargi.
Ta kuma bayyana cewa zargin Kaura yana shafar wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar kamar tsohon Gwamna Abdulaziz Yari, wanda yanzu ke wakiltar Zamfara ta Yamma a Majalisar Dattawa.
Jam’iyyar APC ta ƙalubalanci Kaura da ya kawo hujjoji kan wannan zargi da kuma wasu mutane da aka sace a jihar, kamar satar ɗalibai mata 270 daga makarantar Government Girls Secondary School da ke Jangebe a ranar 26 ga watan Fabrairun 2021, da kuma satar ɗaliban Kwalejin Noma da Kiwo da ke Bakura.
APC ta jaddada cewa gwamnatin Matawalle ta yi ƙoƙari wajen yaƙi da ‘yan bindiga da ceto al’ummomi da dama.
Ta bayyana yankuna kamar Gwaram, Kanoma, Kaya, Faru, Janbako, Lilo da Anka, a matsayin wuraren da aka gudanar da ayyukan tsaro da taimako.
Jam’iyyar ta kuma ce tana duba yiwuwar ɗaukar matakin shari’a kan gidan talabijin na Maibiredi TV da ya watsa hirar da ake ganin an shirya don ɓata sunan ministan.
Ta zargi PDP da ƙoƙarin karkatar da hankalin jama’a daga gazawarta ta hanyar yaɗa ƙarya da tayar da fitina don samun moriyar siyasa.
A ƙarshe, APC ta yi kira ga mambobinta da su zauna lafiya da bin doka, inda ta bayar da tabbacin cewa gaskiya za ta fito fili, kuma za a yi adalci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp