HausaTv:
2025-07-30@18:40:24 GMT

MDD : ba tabbas kan ko za’a kawar da zazzabin malaria nan da shekarar 2030

Published: 25th, April 2025 GMT

Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewa ba tabbas ko za’a iya kawar da cutar zazzabin cizon sauro nan da shekarar 2030, musamman a nahiyar Afrika.

Fiye da mutane miliyan 263 ne suka kamu da cutar a cikin 2023, kuma kusan 600,000 ne suka mutu sanadin cutar a cewar alkalumman na MDD.

Musamman a wannan lokacin da shugaban Amurka Donald Trump ya rage kashe kudaden tallafi na kasa da kasa, inji rahoton.

A cikin shekaru 25, zuba jari a yakin da ake yi da zazzabin cizon sauro ya hana kamuwa da cutar ga mutane biliyan 2 da kuma mutuwar mutane miliyan 13, musamman a Afirka.

“Akwai babbar barazana, da kuma bukatar jajircewa wajen samar da magunguna in ji Philippe Duneton, darektan Unitaid, kungiyar da ke da fafatuklar samar da magunguna na HIV, tarin fuka ko TB da kuma zazzabin cizon sauro.

Bayyanin ya fito ne gabanin zagayowar ranar duniya ta yaki da cutar zazzabin sauro yau 25 ga watan Afrilu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Remi Tinubu ta bai wa waɗanda harin Benuwe ya shafa tallafin Naira biliyan ɗaya

Uwargidan Shugaban Nijeriya, Sanata Remi Tinubu ta bayar da tallafin naira biliyan daya ga wadanda harin nan ya rutsa da su a yankin Yelwata na Ƙaramar Hukumar Guma a Jihar Benuwe.

Sanata Tinubu wadda ta miƙa cakin kuɗin ga Gwamna Hyacinth Alia ta sanar da bayar da tallafin ne a jawabinta na jaje wanda ta kai Fadar Gwamnatin Benuwe da ke Makurdi.

Gwamnatin Zamfara ta amince da naɗin sabon Sarkin Katsinan Gusau Ambaliya ta yi ajalin mutum 30 a China

Uwargidan shugaban ƙasar ta buƙaci a yi amfani da wannan tallafin a matsayin gudunmawar farfaɗo da yankin da waɗanda suka tsallake rijiya da baya a yayin harin musamman yaran da yanzu ke buƙatar komawa makarantu.

Ana iya tuna cewa, tun a daren ranar 13 ga watan Yuni zuwa wayewar gari 14 ga watan ne aka kashe fiye da mutum 100 a ƙauyen Yelwata, lamarin da ya janyo Allah wadai daga sassa daban-daban a faɗin ƙasar.

Jihar Benuwe dai na daga cikin jihohin da ke fuskantar matsalar tsaro a Nijeriya, musamman rikicin manoma da makiyaya da kuma na ƙabilanci, wanda ke sanadiyyar salwantar rayuka da dama.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • An Kaddamar da Makon MNCH na 2025, Ya Rarraba Fakitin Bayarwa 6,000, Kayan C/S 500
  • Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace
  • Remi Tinubu ta bai wa waɗanda harin Benuwe ya shafa tallafin Naira biliyan ɗaya
  • Ambaliya ta yi ajalin mutum 30 a China
  • Gwamnatin Katsina Ta Fara Bayar Da Maganin Zazzabi Kyauta A Asibitoci
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a sabon hari a Alkaleri
  • Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021
  • Mutum miliyan 1.2 na fama da ciwon hanta a Kano
  • Harin Ta’addanci A Wani Coci Ya Lashe Rayukan Mutane Fiye Da 21 A Gabashin Kongo