Sashin ma’adinai da ba na karfe ba ta kashe kudin makamashi da kashi 33.7 zuwa naira biliyan 118.49, kuma masana’antar yadi, tufafi da takalmi kudin da ya kashe ya karu sau hudu, wanda ya kai naira biliyan 26.45 a shekarar 2024, idan aka kwatanta da naira biliyan 6.97 a shekarar 2023.

 

Rahoton ya ce duk da an samu karin wutar lantarki a cikin masana’antu a shekarar 2024, da adadin karin wuta na awa 13.

3 a kwace ranar da ya karu daga awa 10.6 a shekarar 2023.

 

Kazalika karin kudin wuta ya karu da kaso 200 ga wadanda suke amfani da rukunin A, don haka kudaden da masana’antun ke kashewa wajen biyan kudin wuta nan ma ya karu sosai.

 

“A daidai lokacin da aka samu karin wutar lantarki, masana’antu da dama har yanzu suna fuskantar daukewar wuta a kai a kai, da tsadar wutan duk da kasar kuma ta fuskanci lalacewar babban layin wuta har sau 12, wanann shi ne babban abun damuwa.

 

“A neman mafita ga yawan daukewar wutar da karin farashin kudin mai da gas duk sun mamaye masana’antu,” rahoton ya shaida.

 

A daidai wannan gabar, adadin mutanen da suke barin aiki a kamfanoni ya karu daga 17,364 a 2023 zuwa 17,949 a shekarar 2024. A gefe guda kuma an samu sabbin ma’aikata 16,820 a 2024.

 

Dangane da saka hannun jari a fannin da ake samu, an ce fannin ya samu raguwar zuba jarin masana’antu da kashi 35.3 a duk shekara zuwa naira biliyan 658.81 a shekarar 2024, lamarin da ke nuni da rashin tabbas na tattalin arziki da kuma rage tsare-tsaren fadada ayyukan.

 

Rahoton ya kara da cewa, jimillar jarin ya ragu da kashi 11.3 zuwa naira tiriliyan 2.85, inda a bangaren filayen da gine-gine da kayan daki da sauran kayayyaki suka samu koma-baya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: a shekarar 2024 naira biliyan

এছাড়াও পড়ুন:

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

 

Ya ce Sin tana maraba da kamfanonin dake fuskantar kalubale su tuntubi ma’aikatar ko hukumomi masu ruwa da tsaki, yana cewa, ma’aikatar za ta nazarci ainihin abubuwan dake faruwa da kuma bayar da damar fitar da kayayyaki ga wadanda suka cancanta. (Mai fassara: FMM)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya November 1, 2025 Daga Birnin Sin Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar November 1, 2025 Daga Birnin Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung  November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Pezeshkian: Bunkasa Masana’antar Makamashin Nukiliyar Iran Don Inganta Rayuwar Al’ummar Iran Ne
  • Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya
  • Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • Kofin kofi mafi tsada a duniya ya shiga kasuwa a kan Naira miliyan 1.5m
  • Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
  • Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC
  • Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede
  • Borno ta fara fitar da kayan robobi zuwa ƙasashen waje – Zulum