An ayyana zaman makoki na kwana uku bayan kashe mutum 44 a Nijar
Published: 22nd, March 2025 GMT
Gwamnatin Nijar ta ayyana zaman makoki na kwana uku bayan an kashe fararen hula 44 a kudu maso yammacin ƙasar a wani hari da “yan ta’adda” da ke da alaƙa da ƙungiyar ta’addanci ta Daesh suka kai.
Ma’aikatar harkokin cikin gida ta ƙasar ce ta bayyana hakan a wata sanarwa da ta fitar a gidan talabijin na ƙasar a ranar Juma’a.
Sanarwar ta ce ‘yan ta’addan sun kashe fararen hular ne a lokacin da suka afka cikin wani masallaci a ƙauyen Fombita da ke Kokorou inda suka far wa masallata.
Ma’aikatar ta yi Allah-wadai da harin inda ta kira shi da hari na “rashin imani” tare da shan alwashin ƙara matsa ƙaimi domin yaƙi da ta’addanci a yankin.
Zaman makokin da gwamnatin ta Nijar ta sanar na awa 72 zai fara aiki ne daga ranar Asabar domin girmama waɗanda suka rasu.
Za a ɗaga tutocin Nijar rabi a faɗin ƙasar, haka kuma za a dakatar da taruka a daidai lokacin da ƙasar ke cikin makoki.
Yankin kudu maso yammacin Jamhuriyar Nijar, musamman yankunan da ke kusa da kan iyaka da Mali da Burkina Faso, na fuskantar tashe-tashen hankula a ‘yan shekarun nan, inda ƙungiyoyi irin su Daesh ke amfani da rashin zaman lafiya wajen kai munanan hare-hare kan ƙauyuka da jami’an tsaro.
Harin dai ya nuna ƙalubalen tsaro da ƙasar da ke yankin Sahel ke fuskanta, duk kuwa da ƙoƙarin da gwamnati da ƙawayenta na ƙasa da ƙasa suke yi na daƙile ayyukan tada ƙayar baya.
Kawo yanzu dai babu wata kungiya da ta ɗauki alhakin kai harin, ko da yake ma’aikatar harkokin cikin gidan ƙasar ta danganta shi da Daesh saboda kasancewar ƙungiyar a yankin.
Hukumomin ƙasar dai sun yi alƙawarin gudanar da cikakken bincike tare da ɗaukar ƙwararan matakai domin gurfanar da waɗanda suka aikata laifin a gaban kuliya.
Kashe-kashen na baya-bayan nan na ƙara yawan asarar rayukan fararen hula a Nijar, inda al’ummomi ke ci gaba da fuskantar barazanar tashe-tashen hankula.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: fararen hula Nijar
এছাড়াও পড়ুন:
Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka
Wani sojan Ƙasar Amurka ɗan asalin Jihar Kano, Suleiman Isah, wanda yake aiki a rundunar sojin Amurka, ya ce ba zai yaƙi da ƙasarsa ta haihuwa ba saboda yaɗa labaran ƙarya game da yi wa Kiristoci kisan gilla a Najeriya.
Isah, wanda ya shiga rundunar sojin Amurka shekaru biyu da suka gabata, yana aiki ne da rundunar California Army National Guard, mai dakaru sama da 18,000.
Kisan Kiristoci: Lauyoyi sun nemi Gwamnatin Tarayya ta tattauna da Amurka Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin AmurkaA wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook wanda Aminiya ta tabbatar, Isah ya mayar da martani kan jita-jitar cewa Amurka za ta ɗauki matakin yaƙi a kan Najeriya saboda zargin yi wa Kiristoci kisan gilla.
Ya bayyana cewa ba zai taɓa amfani da makami a kan mutanensa ba.
“Ba zan shiga Najeriya na kashe iyayena ba saboda ƙaryar cewa ana kashe Kiristoci,” in ji shi.
Ya ce duk da yake yana Allah-wadai da kashe-kashe da tashin hankali, bai kamata matsalar tsaro a Najeriya a danganta da wani addini ba.
“Ba zan ƙaryata batun kisan Kiristoci da Musulmai ba,” in ji shi.
“Shekau, Bello Turji, Dogo Gide da sauransu ba suna kai wa wani addini ɗaya hari ba ne kaɗai.”
Maganganun Isah na zuwa ne daidai lokacin Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi barazanar ɗaukar matakin yaƙi a kan Najeriya.
Sai dai Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa matsalar tsaro a Najeriya ba ta addini ba ce, inda ta ce matsalar na shafar Musulmai da Kiristoci baki ɗaya.