Aminiya:
2025-12-03@21:39:37 GMT

Zaɓen 2027: ’Yan Najeriya za su yanke wa Tinubu hukunci — PDP

Published: 25th, April 2025 GMT

Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa zaɓen 2027 zai kasance ne kai tsaye tsakanin Shugaba Bola Tinubu da ’yan Najeriya da gwamnatinsa ta jefa su cikin mawuyacin yanayin rayuwa.

Shugaban riƙo na PDP, Umar Damagum, ya jaddada cewa zaɓen “Tsakanin Jam’iyyar APC ne da ’yan Najeriya,” yana mai nuni da wahalar da talakawa ke fuskanta a ƙarƙashin mulkin APC.

Ya yi kira ga ’yan Najeriya da su haɗa kai don magance abin da ya kira “wahalar da aka kawo mana da gangan.”

Damagum ya kuma yi tsokaci kan sauya sheƙar Gwamnan Jihar Delta, Sheriff Oborevwori, da tsohon Gwamna, Ifeanyi Okowa, tare da mambobin majalisar zartarwarsu, zuwa jam’iyyar APC mai mulki.

’Yan bindiga sun kashe ango, sun sace amarya a Nasarawa NAJERIYA A YAU: Dalilin da zazzaɓin cizon sauro ba ya jin magani

A hirarsa da tashar talabijin ta Channels, Damagum ya nuna rashin jin daɗi, yana mai cewa PDP ta kasance mai matuƙar goyon baya ga Jihar Delta kuma ba ta cancanci irin wannan siyasar ba.

Amma duk da sauya sheƙar, ya tabbatar da juriya da kuma ƙarfin PDP.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan Najeriya sauya sheka Zaɓen 2027

এছাড়াও পড়ুন:

Wani ya yi shigar mahaifiyarsa da ta mutu ya je karvar kuxin fanshonta

Wani ya yi shigar mahaifiyarsa da ta mutu ya je karvar kuxin fanshonta

Ana binciken wani tsohon ma’aikacin jinya a qasar Italiya bisa zargin ya yi shigar mahaifiyarsa da ta mutu kuma ya je ma’aikatar fansho a matsayin mahaifiyarsa don neman fanshonta. Haka kuma an gano ya voye gawarta a cikin gidansa har tsawon shekaru uku bayan mutuwarta.

Mutumin xan Italiya ya saka tufafin mahaifiyarsa da ta mutu sannan ya yi kwalliya da gazar da jan-baki kamar yada take yi, ya je bankin da take ajiya yana neman a biya shi kuxi fanshonta, bayan ya voye gawarta a gida.

Mutumin mai shekaru 56, ma’aikacin jinya da ya rasa aikinsa a garin Mantua, ya sami damar karvar dubban kuxi na Yuro kafin asirinsa ya tonu, kamar yadda Jaridar Corriere della Sera ta Italiya ta ruwaito.

An kuma yi zargin cewa, ya naxe gawar mahaifiyarsa, Graziella Dall’Oglio, sannan ya voye ta a cikin firji a gidansu har tsawon shekara uku ba tare da ya sanar da ma’aikatar fansho ba, inda ya riqa zuwa yana cire kuxin fanshon da ake tura mata yana bidirin gabansa.

Mis Dall’Oglio ta rasu kimanin shekara uku da suka gabata, tana da shekara 82. Amma xanta bai bayar da rahoton mutuwarta a hukumance ba, maimakon haka ya naxe gawarta a cikin zane, ya saka ta a cikin wata jakar ajiye kaya sannan ya voye ta a gidan.

Rahotanni sun ce, ya yi shigar mahaifiyarsa, sanye da jan-baki da hoda da gazar da kuma sarqa, sannan ya tafi sabunta katin shaidarta da ya qare a ofishin gwamnati da ke wajen Borgo Virgilio.

Bayanai sun nuna cewa, ya yi wa kansa aski sannan ya sanya gashin mata a kansa kamar irin na mahaifiyarsa da ta rasu, kuma ya sanya kayan ado kamar yadda ta saba.

Jaridar ta bayyana cewa, wannan wani sabon salon damfara ce kamar irin na fim xin ‘Mrs Doubtfire’, wanda aka yi a shekarar 1993 da Robin WilliaMis da ya fito a ciki. Mutumin ya bayyana a ofishin gwamnati da ke wajen Mantua a farkon wannan watan, inda aka yi zargin ya bayyana kansa a matsayin Mis Dall’Oglio.

Wani ma’aikacin ma’aikatar fansho ne ya harvo jirginsa, inda ya lura da cewa, akwai alamar tambaya game da ‘matar’ da take neman a canza mata katin. Musamman da yake ya san wacce take da ainihin katin ba ta da kaurin wuya, sannan kuma muryarta ba ta maza ba ce. Wannan ce ta sanya ma’aikacin bai wata-wata ba cikin sauri ya kai rahoto ga ‘yan sanda nan da nan kuma ya sanar da magajin garin Mantua.

’Yan sanda sun ce, da isarsu sai suka kwatanta hotunan Mis Dall’Oglio na gaske da na xanta da ya yi shigar burtu kuma sun fahimci cewa, akwai lauje a cikin naxi.

Bincike ya nuna xan ya karvi kuxin fanshonta na shekaru uku da suka kai kusan Fam 47,000 kuma da mallakar gidaje uku, a cewar rahotanni.

Bayan an kama shi, ‘yan sanda sun je gidansa, inda suka gano gawar Mis Dall’Oglio da aka voye a xakin wanki.

“Ya shigo ofishin ma’aikatar fansho yana sanye da dogon siket, ya yi ado da jan baki da jan-farce da sarqa da ‘yan kunne irin na tsofaffi,” Francesco Aporti, magajin garin Borgo Virgilio ya shaida wa Jaridar Corriere della Sera.

“Amma sai dai yana da kaurin wuya, sannan kuma fatar hannunsa ba ta yi kama da na tsohuwa ‘yar shekara 85 ba.

“Muryarsa kuma ta maza ce duk da yake ya yi shigar mata. Amma da a ce ba a lura da waxannan abubuwa ba da ya ci lalai.”

Da yake magana game da mahaifiyar wanda ake zargin, magajin garin ya ce, “Wataqila ta mutu ne saboda dalilai na rashin lafiya, amma za a tabbatar da hakan ne kawai ta hanyar binciken gawar.” Wannan labari ne mai ban mamaki kuma abin baqin ciki ne qwarai.”

‘Yan sandan Italiya sun ce, gawar mahaifiyar an naxe ta da zanin gado sannan aka saka ta a wata jakar kaya, aka sanya ta cikin firji.

Daga baya ’yan sanda sun xauki gawar zuwa wajen ajiye gawarwaki a asibitin da ke yankin don yin gwajin qwaqwaf da nufin gano musabbabin rasuwarta. Yanzu haka ana binciken mutumin a kan laifukan zamba da voye gawar da ya yi ba bisa qa’ida ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya san dalilin da ya sa na yi murabus daga muƙamin ministan — Badaru
  • Wani ya yi shigar mahaifiyarsa da ta mutu ya je karvar kuxin fanshonta
  • Yau Majalisar Dattawa za ta tantance sabon Ministan Tsaro
  • Ministan Tsaron Najeriya  Ya Mika Takardar Ajiye Aiki Ga Shugaban Kasa Ahmad Tinubu.
  • NAJERIYA A YAU: Matsalar Kansar Mama Da Hanyoyin Magance Shi
  • Tinubu ya gana da Janar Christopher Musa bayan Ministan Tsaro ya yi murabus
  • Tinubu ya gana da Janar Christopher CG Musa bayan Ministan Tsaro ya yi murabus
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan 164
  • Najeriya Ta Kara Ƙaimi Wajen Kawar da Cutar HIV Nan da 2030
  • NAJERIYA A YAU: Halayen Da Ambasadoji Ya Kamata Su Mallaka Kafin Tura Su Wasu Kasashe