Zaɓen 2027: ’Yan Najeriya za su yanke wa Tinubu hukunci — PDP
Published: 25th, April 2025 GMT
Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa zaɓen 2027 zai kasance ne kai tsaye tsakanin Shugaba Bola Tinubu da ’yan Najeriya da gwamnatinsa ta jefa su cikin mawuyacin yanayin rayuwa.
Shugaban riƙo na PDP, Umar Damagum, ya jaddada cewa zaɓen “Tsakanin Jam’iyyar APC ne da ’yan Najeriya,” yana mai nuni da wahalar da talakawa ke fuskanta a ƙarƙashin mulkin APC.
Ya yi kira ga ’yan Najeriya da su haɗa kai don magance abin da ya kira “wahalar da aka kawo mana da gangan.”
Damagum ya kuma yi tsokaci kan sauya sheƙar Gwamnan Jihar Delta, Sheriff Oborevwori, da tsohon Gwamna, Ifeanyi Okowa, tare da mambobin majalisar zartarwarsu, zuwa jam’iyyar APC mai mulki.
’Yan bindiga sun kashe ango, sun sace amarya a Nasarawa NAJERIYA A YAU: Dalilin da zazzaɓin cizon sauro ba ya jin maganiA hirarsa da tashar talabijin ta Channels, Damagum ya nuna rashin jin daɗi, yana mai cewa PDP ta kasance mai matuƙar goyon baya ga Jihar Delta kuma ba ta cancanci irin wannan siyasar ba.
Amma duk da sauya sheƙar, ya tabbatar da juriya da kuma ƙarfin PDP.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan Najeriya sauya sheka Zaɓen 2027
এছাড়াও পড়ুন:
Mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya ɗaya ba ya cikin manufofinmu — Tinubu
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi watsi da zargin cewa gwamnatinsa na ƙoƙarin mayar da Nijeriya kan tsarin ƙasa da ke kan tafarkin jam’iyya ɗaya a ƙarƙashin mulkinsa.
Shugaban ya kore wannan zargin ne a yayin jawabin da ya yi na zagayowar Ranar Dimokuraɗiyya a zauren majalisar dokokin ƙasar da ke Abuja, yau Alhamis.
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwaman Zulum ya yi wa fursunoni 66 afuwa 12 ga Yuni: Najeriya na bikin ranar dimokuraɗiyyaTinubu ya ce masu tunanin cewa APC na son mayar da Nijeriya ƙasa mai jam’iyya ɗaya, to tunanin nasu kuskure ne, kuma suna yin sa cikin ruɗani ne.
Ya ce: “Tsarin jam’iyya ɗaya ba ya cikin manufofinmu. Kuma ba zai taɓa zama cikin manufofinmu ba.”
Sai dai shugaban ya ce wannan ba zai hana jam’iyyar APC yin maraba da duk wanda ke son shiga cikinta ba.
“Zai kasance mun yi maguɗin siyasa idan muka hana mutane daga wasu jam’iyyun siyasa shigowa jam’iyyar APC,” in ji Tinubu.
Sai dai Tinubun ya ce suna farin cikin da rikicin ci gida da ke addabar jam’iyyun adawa kuma ba zai shawarar yadda za su warware matsalolinsu ba.
“Ina jin daɗin ganin jam’iyyun adawa a cikin ruɗani, saboda hakan nasara ce bangarenmu.
“Najeriya ba za ta zama ƙasa mai jam’iyya ɗaya ba, batun jam’iyya ɗaya bai ta taso ba, amma siyasar za ta taɓarɓare idan muka rufe ƙofa ga masu son shiga APC,” in ji shi.