Aminiya:
2025-11-06@10:10:09 GMT

Zaɓen 2027: ’Yan Najeriya za su yanke wa Tinubu hukunci — PDP

Published: 25th, April 2025 GMT

Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa zaɓen 2027 zai kasance ne kai tsaye tsakanin Shugaba Bola Tinubu da ’yan Najeriya da gwamnatinsa ta jefa su cikin mawuyacin yanayin rayuwa.

Shugaban riƙo na PDP, Umar Damagum, ya jaddada cewa zaɓen “Tsakanin Jam’iyyar APC ne da ’yan Najeriya,” yana mai nuni da wahalar da talakawa ke fuskanta a ƙarƙashin mulkin APC.

Ya yi kira ga ’yan Najeriya da su haɗa kai don magance abin da ya kira “wahalar da aka kawo mana da gangan.”

Damagum ya kuma yi tsokaci kan sauya sheƙar Gwamnan Jihar Delta, Sheriff Oborevwori, da tsohon Gwamna, Ifeanyi Okowa, tare da mambobin majalisar zartarwarsu, zuwa jam’iyyar APC mai mulki.

’Yan bindiga sun kashe ango, sun sace amarya a Nasarawa NAJERIYA A YAU: Dalilin da zazzaɓin cizon sauro ba ya jin magani

A hirarsa da tashar talabijin ta Channels, Damagum ya nuna rashin jin daɗi, yana mai cewa PDP ta kasance mai matuƙar goyon baya ga Jihar Delta kuma ba ta cancanci irin wannan siyasar ba.

Amma duk da sauya sheƙar, ya tabbatar da juriya da kuma ƙarfin PDP.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan Najeriya sauya sheka Zaɓen 2027

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

 

Ya ƙara da cewa: “Mun cika dukkan buƙatunsu. Yanzu mun koma teburin tattaunawa, yanzu haka na zo wurin shugaba Tinubu ne don zayyana masa inda muka tsaya da ASUU.”

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai 2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC November 4, 2025 Labarai Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume November 4, 2025 Manyan Labarai Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno November 4, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Najeriya ta yi watsi da sanya sunanta cikin jerin kasashen da ake tauye ’yancin addini
  • Masu Sa Ido na Tarayyar Afirka: Zaben Tanzania Ya Keta Ka’idojin Demokradiyya
  • Musulmi na farko ya lashe zaɓen magajin garin New York a Amurka
  • Tinubu na neman majalisa ta amince masa ya ciyo sabon bashin Tiriliyan 1.150
  • Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU
  • 2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC
  • NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya
  • An rantsar da Samia Suluhu Hassan a wa’adin mulki na biyu a Tanzaniya
  • An rantsar da Samia Suluhu Hassan a wa’adin mullki na biyu a Tanzaniya
  • Sabon Muƙaddashin Shugaban PDP Ya Sha Alwashin Maido Da Martabar Jam’iyyar Kafin 2027