Aminiya:
2025-07-04@01:08:14 GMT

Zaɓen 2027: ’Yan Najeriya za su yanke wa Tinubu hukunci — PDP

Published: 25th, April 2025 GMT

Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa zaɓen 2027 zai kasance ne kai tsaye tsakanin Shugaba Bola Tinubu da ’yan Najeriya da gwamnatinsa ta jefa su cikin mawuyacin yanayin rayuwa.

Shugaban riƙo na PDP, Umar Damagum, ya jaddada cewa zaɓen “Tsakanin Jam’iyyar APC ne da ’yan Najeriya,” yana mai nuni da wahalar da talakawa ke fuskanta a ƙarƙashin mulkin APC.

Ya yi kira ga ’yan Najeriya da su haɗa kai don magance abin da ya kira “wahalar da aka kawo mana da gangan.”

Damagum ya kuma yi tsokaci kan sauya sheƙar Gwamnan Jihar Delta, Sheriff Oborevwori, da tsohon Gwamna, Ifeanyi Okowa, tare da mambobin majalisar zartarwarsu, zuwa jam’iyyar APC mai mulki.

’Yan bindiga sun kashe ango, sun sace amarya a Nasarawa NAJERIYA A YAU: Dalilin da zazzaɓin cizon sauro ba ya jin magani

A hirarsa da tashar talabijin ta Channels, Damagum ya nuna rashin jin daɗi, yana mai cewa PDP ta kasance mai matuƙar goyon baya ga Jihar Delta kuma ba ta cancanci irin wannan siyasar ba.

Amma duk da sauya sheƙar, ya tabbatar da juriya da kuma ƙarfin PDP.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan Najeriya sauya sheka Zaɓen 2027

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Halin da al’ummar Mokwa ke ciki wata 2 bayan ambaliya

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Tun bayan da ambaliyar ruwa ya ci wasu sassan garin Mokwa al’ummar yankin suka faɗa halin neman taimako.

Duk da cewa Gwamnatin Tarayya da wasu ɗaiɗakun mutane sun tallafa wa waɗanda abin ya shafa da kuɗi da ma wasu abubuwa, amma mazauna yankin suna bayyana rashin jin daɗinsu bisa yadda al’amura ke gudana a garin.

Najeriya A Yau: Yadda Za A Kawo Karshen Daukar Doka A Hannu A Najeriya DAGA LARABA: Ko Najeriya Na Da Kudin Renon Sabbin Jihohi?

Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan halin da al’ummar Mokwa ke ciki watanni biyu bayan ibtila’in ambaliyar.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci
  • ’Yan Najeriya sun fara begen Buhari saboda azabar Tinubu – Amaechi
  • ’Yan Najeriya sun fara begen Buhari saboda azabar TIinubu – Amaechi
  • 2027: David Mark zai kai mu ga nasara — ADC
  • David Mark ya fice daga PDP, ya shiga haɗaka don ƙalubalantar Tinubu
  • Kotu ta yanke hukuncin rataya ga dalibin da ya kashe malaminsa a Jos
  • Ko ɗaya Buhari bai yi wa takarar Tinubu zagon ƙasa ba – Garba Shehu
  • Kotu A Kasar Iraki Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wadanda Suka Kashe Ayatullahi Baqir Sadr
  • Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen VC Na Jami’ar Bayero Ta Kano 
  • NAJERIYA A YAU: Halin da al’ummar Mokwa ke ciki wata 2 bayan ambaliya