Zaɓen 2027: ’Yan Najeriya za su yanke wa Tinubu hukunci — PDP
Published: 25th, April 2025 GMT
Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa zaɓen 2027 zai kasance ne kai tsaye tsakanin Shugaba Bola Tinubu da ’yan Najeriya da gwamnatinsa ta jefa su cikin mawuyacin yanayin rayuwa.
Shugaban riƙo na PDP, Umar Damagum, ya jaddada cewa zaɓen “Tsakanin Jam’iyyar APC ne da ’yan Najeriya,” yana mai nuni da wahalar da talakawa ke fuskanta a ƙarƙashin mulkin APC.
Ya yi kira ga ’yan Najeriya da su haɗa kai don magance abin da ya kira “wahalar da aka kawo mana da gangan.”
Damagum ya kuma yi tsokaci kan sauya sheƙar Gwamnan Jihar Delta, Sheriff Oborevwori, da tsohon Gwamna, Ifeanyi Okowa, tare da mambobin majalisar zartarwarsu, zuwa jam’iyyar APC mai mulki.
’Yan bindiga sun kashe ango, sun sace amarya a Nasarawa NAJERIYA A YAU: Dalilin da zazzaɓin cizon sauro ba ya jin maganiA hirarsa da tashar talabijin ta Channels, Damagum ya nuna rashin jin daɗi, yana mai cewa PDP ta kasance mai matuƙar goyon baya ga Jihar Delta kuma ba ta cancanci irin wannan siyasar ba.
Amma duk da sauya sheƙar, ya tabbatar da juriya da kuma ƙarfin PDP.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan Najeriya sauya sheka Zaɓen 2027
এছাড়াও পড়ুন:
Mai taɓin hankali ya kashe soja a Legas
Wani mutum da ake zargin yana fama da matsalar tabin hankali ya kai hari tare da kashe wani soja a yankin Imota da ke Ikorodu a jihar Legas.
Lamarin, wanda ya faru a fili da rana tsaka a ranar Lahadi, ya sa makwabtan wurin da dama guduwa don neman tsira.
Gobara ta laƙume kasuwar Katako a Gombe Amurka za ta binciki zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya ranar AlhamisShaidu sun bayyana cewa wanda ya kai harin, wanda ba shi da makami sai sanda ta itace, ya kusanci sojan ya dinga dukan shi da sandar.
Sojan da ya rasu, wanda aka ce yana aiki a karkashin Operation AWASE, rundunar haɗin gwiwa ta musamman da ke yaki da laifuka a jihar, ya mutu sakamakon raunukan da ya samu.
Lamarin ya faru ne a ranar Lahadi, 16 ga Nuwamba, 2025, da misalin ƙarfe 4:00 na yamma, lokacin da aka tura sojan don aikin tsaro na cikin gida.
Rundunar Sojojin Najeriya ta 81 ta tabbatar da faruwar lamarin, tare da yin ta’aziyya ga iyalan sojan da ya rasu.
Mai rikon mukamin Daraktan Hulɗa da Jama’a na shiyyar, Musa Yahaya, ya bayyana a ranar Talata cewa sojan yana ƙoƙarin kwantar da tarzoma ne lokacin da mai harin ya bugi kansa da sanda mai nauyi, wanda ya jawo masa mummunan rauni.
Ya kuma ce sauran sojoji sun hanzarta shawo kan lamarin, suka kashe mutumin tare da dawo da makamin sojan.
Yahaya ya ƙara da cewa an garzaya da sojan da ya ji rauni zuwa Asibitin Gwamnati da ke Ikorodu, inda aka tabbatar da mutuwarsa.
Ya ce tuni aka fara gudanar da bincike kan lamarin, kuma rundunar sojoji ta yi kira ga jama’a da su kasance masu lura da kuma bayar da rahoton duk wani abun da ba su yarda da shi ba.