Aminiya:
2025-12-07@13:38:35 GMT

Zaɓen 2027: ’Yan Najeriya za su yanke wa Tinubu hukunci — PDP

Published: 25th, April 2025 GMT

Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa zaɓen 2027 zai kasance ne kai tsaye tsakanin Shugaba Bola Tinubu da ’yan Najeriya da gwamnatinsa ta jefa su cikin mawuyacin yanayin rayuwa.

Shugaban riƙo na PDP, Umar Damagum, ya jaddada cewa zaɓen “Tsakanin Jam’iyyar APC ne da ’yan Najeriya,” yana mai nuni da wahalar da talakawa ke fuskanta a ƙarƙashin mulkin APC.

Ya yi kira ga ’yan Najeriya da su haɗa kai don magance abin da ya kira “wahalar da aka kawo mana da gangan.”

Damagum ya kuma yi tsokaci kan sauya sheƙar Gwamnan Jihar Delta, Sheriff Oborevwori, da tsohon Gwamna, Ifeanyi Okowa, tare da mambobin majalisar zartarwarsu, zuwa jam’iyyar APC mai mulki.

’Yan bindiga sun kashe ango, sun sace amarya a Nasarawa NAJERIYA A YAU: Dalilin da zazzaɓin cizon sauro ba ya jin magani

A hirarsa da tashar talabijin ta Channels, Damagum ya nuna rashin jin daɗi, yana mai cewa PDP ta kasance mai matuƙar goyon baya ga Jihar Delta kuma ba ta cancanci irin wannan siyasar ba.

Amma duk da sauya sheƙar, ya tabbatar da juriya da kuma ƙarfin PDP.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan Najeriya sauya sheka Zaɓen 2027

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya ta shigo da tataccen man fetur na tiriliyan 12.8 cikin watanni 15

Najeriya ta shigo da tataccen man fetur na Naira tiriliyan 12.8 daga watan Agustan 2024 zuwa Oktoba 2025, bisa ga bayanan da Hukumar Kula da Rarraba Man Fetur ta Najeriya (NMDPRA) ta fitar.

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da kasar ke ƙoƙarin ƙara samar da man fetur a cikin gida, duk kuma da aikin da matatar Dangote ke yi.

An kashe matashi yayin rikici a wajen raɗin suna a Bauchi Amurka za ta hana ’yan Najeriyar da ake zargi da yi wa Kiristoci kisan kiyashi biza

Bisa amfani da matsakaicin farashin lita ɗaya na ₦829.77, an ƙididdige jimillar lita 15,435,000,000 da aka shigo da su a wannan lokaci.

Bincike ya nuna cewa mafi yawan shigo da man fetur ya kasance ne a watan Satumban 2024 lokacin da ba a samar da man ba a cikin gida, inda aka shigo da lita biliyan 1.52, sai Agusta 2024 da lita biliyan 1.38, sannan Disamba 2024 da lita biliyan 1.31.

A Oktoba 2025, an shigo da lita biliyan 1.17, sai Nuwamba da lita biliyan 1.12. Amma a Janairu 2025, adadin ya ragu sosai zuwa lita miliyan 765.7, kafin ya ɗan ƙaru zuwa lita miliyan 770 a Fabrairu, sannan miliyan 889.7 a Maris.

A Afrilu, an samu lita miliyan 861, sai kuma Mayu da ya haura zuwa 1.19 biliyan, kafin ya ragu zuwa 978 miliyan a Yuni, sannan ya ƙaru zuwa 1.11 biliyan a Yuli, kafin ya sauka zuwa 818.4 miliyan a Agusta, 663 miliyan a Satumba, da 855.6 miliyan a Oktoba.

Samarwa da mai a cikin gida

A ɓangaren samarwa a cikin gida, jimillar lita biliyan 7.2 aka samar a wannan lokaci, dukkansu daga matatar man Dangote.

Bayanan sun nuna cewa ba a samu gudunmawar samarwa daga cikin gida ba a watan Agusta 2024, amma a Satumba 2024, Dangote ya samar da lita miliyan 102, wanda ya ƙaru zuwa miliyan 300.7 a Oktoba 2024, sannan miliyan 558 a Nuwamba 2024.

Bayanan sun nuna cewa har yanzu ƙasar na dogaro sosai da shigo da man fetur duk da ƙoƙarin kawo ƙarshen shigo da shi domin tallafa wa samarwa a cikin gida.

Dangote ya sha bayyana cewa matatar man shi karfin tace ganga 650,000 a kullum na iya wadatar da Najeriya.

Sai dai masana a fannin sun ce haramta shigo da man fetur zai iya haifar da babakere a fannin, wanda suka ce bai dace da kasuwar man fetur ba a kasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 168
  • Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 167
  • Sabuwar Dokar CBN: Nawa Za a Iya Cirewa a ATM da POS?
  • Fyaɗe ga ’yar shekara 12 ya ja wa matashi ɗaurin rai-da-rai a Yobe
  • Akwai hannun ƙasashen waje a rashin tsaron Najeriya —Sheikh Gumi
  • Limamin Tehran:  Idan Abokan Gaba Su Ka  Sake Yin Kuskure Akan Iran Za Su Sake Cin Kasa
  • Ina nan a PDP duk da sauya sheƙar ’yan majalisar Ribas — Wike
  • Najeriya: Tinubu Ya Nada Wasu Karin Jakadu 65, Sanatoci Da Tsoffin Gwamnoni Na Daga Cikinsu
  • Najeriya ta shigo da tataccen man fetur na tiriliyan 12.8 cikin watanni 15
  • Microsoft Za Ta Fuskanci Hukunci Kan Waimaka Wa Isra’ila A  Laifukan Da Take Aikatawa Kan Falasdinawa