Aminiya:
2025-12-06@13:11:35 GMT

Zaɓen 2027: ’Yan Najeriya za su yanke wa Tinubu hukunci — PDP

Published: 25th, April 2025 GMT

Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa zaɓen 2027 zai kasance ne kai tsaye tsakanin Shugaba Bola Tinubu da ’yan Najeriya da gwamnatinsa ta jefa su cikin mawuyacin yanayin rayuwa.

Shugaban riƙo na PDP, Umar Damagum, ya jaddada cewa zaɓen “Tsakanin Jam’iyyar APC ne da ’yan Najeriya,” yana mai nuni da wahalar da talakawa ke fuskanta a ƙarƙashin mulkin APC.

Ya yi kira ga ’yan Najeriya da su haɗa kai don magance abin da ya kira “wahalar da aka kawo mana da gangan.”

Damagum ya kuma yi tsokaci kan sauya sheƙar Gwamnan Jihar Delta, Sheriff Oborevwori, da tsohon Gwamna, Ifeanyi Okowa, tare da mambobin majalisar zartarwarsu, zuwa jam’iyyar APC mai mulki.

’Yan bindiga sun kashe ango, sun sace amarya a Nasarawa NAJERIYA A YAU: Dalilin da zazzaɓin cizon sauro ba ya jin magani

A hirarsa da tashar talabijin ta Channels, Damagum ya nuna rashin jin daɗi, yana mai cewa PDP ta kasance mai matuƙar goyon baya ga Jihar Delta kuma ba ta cancanci irin wannan siyasar ba.

Amma duk da sauya sheƙar, ya tabbatar da juriya da kuma ƙarfin PDP.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan Najeriya sauya sheka Zaɓen 2027

এছাড়াও পড়ুন:

Sabuwar Dokar CBN: Nawa Za a Iya Cirewa a ATM da POS?

Yanzu ƴan Najeriya za su iya cire naira 100,000 ta na’urar cire kuɗi ta ATM a rana, haka ma abin yake a ɓangaren cire kuɗi ta na’urar POS.

A ɓangaren ma’aikatu kuma, za su iya cire kuɗi har naira miliyan biyar ne a duk mako.

Wannan na ƙunshe ne a cikin sabbin tsare-tsaren da Babban Bankin Najeriya CBN ya fitar bayan garambawul da ya yi kan dokokin cire kuɗi ta na’urar ATM da POS a Najeriya.

Bankin ya ce wannan sabuwar dokar za ta fara aiki ne daga ranar 1 ga watan Janairun shekarar 2026.

A cikin wata sanarwa da daraktan tsare-tsare na bankin, Dr Rita Sike ta fitar a ranar Talata 2 ga watan Disamba, ta ce babban bankin ya yi gyara ne a kan dokokin kuɗin da za a iya cirewa.

Amma idan mutum ya cire kuɗi sama da ƙa’idar da aka ƙayyade a mako, mutum zai biya wani adadi na kuɗin.

Ya kamata ƴan Najeriya su fahimci cewa ida suka shiga cikin banki suka cire naira 100,000, shi ma yana cikin kuɗin da suka cire a rana.

Hakan na nufin za a ƙirga shi a cikin kuɗin da mutum ya cire a makon, kamar ya cire ta ATM ko POS.

Me ya sa aka yi canjin?

Kamar yadda sanarwar ta nuna, an tsara tsohuwar dokar ce domin rage ta’ammali da tsabar kuɗi da magance matsalolin tsaro da ma daƙile sama da faɗi da kuɗaɗe da sauran abubuwan da ake tunanin ba su da sauƙi sai da tsabar kuɗi.

Sauran dokokin sun haɗa da:

Cire kuɗi mai yawa – Idan ka cire kuɗi sama da adadin da ƙayyade, za ka biya kashi uku, idan kuma ma’aikata ce za ta biya kashi biyar na kuɗin.

Amfani da takardar karɓar kuɗi a banki – Idan ka tura wani da takardar karɓar kuɗi wato ‘check’, shi ma za a ƙirga a cikin adadin kuɗin da ka cire a mako.

Yadda aka fara dokar

A watan Disamban 2022 ne babban bankin Najeriya ya sanar da cewa daga ranar 9 ga wata Janairun 2023, ɗaiɗaikun mutane ba za su cire kuɗi sama da naira 100,000 ba, ma’aikatu kuma naira 500,000.

Sannan a lokacin bankin ya ce adadin kuɗin da za a iya cirewa ta na’urar POS shi ne naira 20,000.

Haka kuma a lokacin bankin ya ƙayyade cewa ƙananan takardun kuɗi irin su naira 200 zuwa ƙasa ne za a riƙa sakawa a ATM.

Bankin ya fitar da tsare-tsaren ne bayan fitar da sababbin takardun kuɗi a Najeriya.

Idan mutum zai cire sama da adadin, zai biya kashi biyar, ma’aikatu kuma za su biya kashi 10.

A baya, kuɗin da mutum zai iya cirewa ta na’urar ATM naira 100,00 ne a mako, amma mutum naira 20,000 kawai zai iya cira a kullum, amma a POS kuma, naira 20,000 kawai za a iya cirewa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sabuwar Dokar CBN: Nawa Za a Iya Cirewa a ATM da POS?
  • Fyaɗe ga ’yar shekara 12 ya ja wa matashi ɗaurin rai-da-rai a Yobe
  • Akwai hannun ƙasashen waje a rashin tsaron Najeriya —Sheikh Gumi
  • Ina nan a PDP duk da sauya sheƙar ’yan majalisar Ribas — Wike
  • Najeriya: Tinubu Ya Nada Wasu Karin Jakadu 65, Sanatoci Da Tsoffin Gwamnoni Na Daga Cikinsu
  • Microsoft Za Ta Fuskanci Hukunci Kan Waimaka Wa Isra’ila A  Laifukan Da Take Aikatawa Kan Falasdinawa
  • Tinubu ya naɗa tsohon kantoman Ribas da Dambazau a matsayin Jakadun Najeriya
  • Na gana da Tinubu kan Kanu ba batun sauya sheƙa ba — Gwamnan Abia
  • ’Yan Najeriya suna da ƙwarin guiwa a kaina, ba zan ba su kunya ba — Ministan Tsaro
  • Tinubu ya san dalilin da ya sa na yi murabus daga muƙamin ministan — Badaru