Aminiya:
2025-12-14@18:15:16 GMT

Zaɓen 2027: ’Yan Najeriya za su yanke wa Tinubu hukunci — PDP

Published: 25th, April 2025 GMT

Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa zaɓen 2027 zai kasance ne kai tsaye tsakanin Shugaba Bola Tinubu da ’yan Najeriya da gwamnatinsa ta jefa su cikin mawuyacin yanayin rayuwa.

Shugaban riƙo na PDP, Umar Damagum, ya jaddada cewa zaɓen “Tsakanin Jam’iyyar APC ne da ’yan Najeriya,” yana mai nuni da wahalar da talakawa ke fuskanta a ƙarƙashin mulkin APC.

Ya yi kira ga ’yan Najeriya da su haɗa kai don magance abin da ya kira “wahalar da aka kawo mana da gangan.”

Damagum ya kuma yi tsokaci kan sauya sheƙar Gwamnan Jihar Delta, Sheriff Oborevwori, da tsohon Gwamna, Ifeanyi Okowa, tare da mambobin majalisar zartarwarsu, zuwa jam’iyyar APC mai mulki.

’Yan bindiga sun kashe ango, sun sace amarya a Nasarawa NAJERIYA A YAU: Dalilin da zazzaɓin cizon sauro ba ya jin magani

A hirarsa da tashar talabijin ta Channels, Damagum ya nuna rashin jin daɗi, yana mai cewa PDP ta kasance mai matuƙar goyon baya ga Jihar Delta kuma ba ta cancanci irin wannan siyasar ba.

Amma duk da sauya sheƙar, ya tabbatar da juriya da kuma ƙarfin PDP.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan Najeriya sauya sheka Zaɓen 2027

এছাড়াও পড়ুন:

Jam’iyyar PDP ta tabbatar da mutuwar mataimakin Gwamnan Bayelsa

Jam’iyyar PDP a ranar Alhamis ta tabbatar da mutuwar mataimakin gwamnan jihar Bayelsa, Sanata Lawrence Ewhrudjakpo.

Jam’iyyar ta tabbatar da rasuwar ce a cikin wata sanarwa da sakatarenta yada labaranta na kasa, Kwamared Ini Ememobong, ya fitar.

Rahotanni sun ce Ewhrudjakpo ya yanke jiki ya faɗi a ofishinsa da ke gidan gwamnati, Yenagoa, a ranar Alhamis, inda aka garzaya da shi zuwa Cibiyar Lafiya ta Ƙasa (FMC) da ke Yenagoa.

Lamarin ya faru ne a ranar Alhamis.

An haifi Ewhrudjakpo ranar ranar biyar ga watan Satumban 1965, a ƙauyen Ofoni da ke Ƙaramar Hukumar Sagbama, Jihar Bayelsa. Ya rasu yana da shekaru 60.

Kodayake ba a san ainihin dalilin faɗuwarsa ba, majiyoyi sun ce ya faɗi ne ba zato ba tsammani yayin da yake gudanar da ayyukan ofis, lamarin da ya sa dogarai da ma’aikatansa suka yi gaggawar taimaka masa.

Wasu majiyoyi da ke kusa da marigayin sun nuna cewa mutuwarsa na iya zama sakamakon bugun zuciya.

Lamarin ya haifar da ɗan tashin hankali a gidan gwamnati da kuma fadin Yenagoa, inda mazauna garin suka nuna damuwa game da mutumin da suke kira da “Mataimakin Gwamna Mai Aikin Dare.”

Sun ce sau da yawa yana yin aiki har dare ba tare da hutu ba.

A lokacin da ake rubuta wannan rahoto da yammacin jiya, gwamnatin Jihar Bayelsa ba ta fitar da wata sanarwa ba a hukumance a kan lamarin.

Kazalika, da mai taimaka wa mataimakin gwamnan kan yaɗa labarai, Doubra Atazi, da kuma Kwamishinan Yaɗa Labarai na jihar, Ebiuwou Koku-Obiyai, sun ƙi yin bayani lokacin da aka tuntube su.

Sai dai a cikin sanarwarta, PDP ta bayyana kaduwa da alhini kan rasuwar mataimakin gwamnan, tana bayyana shi a matsayin “amintaccen ɗan jam’iyya kuma mai gaskiya.”

Sanarwar ta ce: “Jam’iyyar PDP ta kadu matuƙa da labarin rasuwar Mataimakin Gwamnan Jihar Bayelsa kuma ɗan jam’iyya mai aminci, Mai Girma Sanata Lawrence Oborawharievwo Ewhrudjakpo, wanda rahotanni suka ce ya faɗi ya rasu a yau.

“Wannan labari mai tayar da hankali ya jefa Kwamitin Zartarwa na Ƙasa ƙarƙashin jagorancin Kabiru Tanimu Turaki, SAN, da kuma dukkan mambobin jam’iyyarmu mai girma, musamman mambobinmu masu aminci a Jihar Bayelsa, cikin baƙin ciki mai yawa.

“Tun yana raye, Sanata Ewhrudjakpo ya kasance ɗan siyasa mai gaskiya da daidaito wanda ya yi siyasa bisa ƙa’ida. Mutum ne da ya yi tsayin daka, jagora ne wanda rayuwarsa ta ta’allaka da imani, gaskiya da ƙarfin hali. Ya tsaya tsayin daka kan waɗannan dabi’u har zuwa ƙarshe.

“Muna cikin baƙin ciki matuƙa da rasuwar wannan jarumin siyasa mai gaskiya, kuma muna roƙon Allah ya ba shi hutu na har abada. Muna mika ta’aziyyarmu ga gwamnati da al’ummar jihar Bayelsa kan wannan babban rashin da ba za a iya maye gurbinsa ba.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin da ya sa muka ziyarci Obasanjo — Turaki
  • ’Yan sanda sun ba da tabbacin isasshen tsaro a zaɓen ƙananan hukumomin Borno
  • Amurka ta kama jirgin ruwan dakon man Najeriya
  • Kotu ta sa ranar yanke hukunci a Shari’ar Abba Kyari da NDLEA
  • 2027: Jam’iyyar NNPP ta rantsar da sabbin shugabanni a Gombe
  • Zaɓen 2027 ya hana ni korar wasu ma’aikata – Bago
  • Kotun Koli ta soke afuwar da Tinubu ya yi wa Maryam Sanda
  • Yadda APC Da ADC Ke Amfana Da Rikicin Jam’iyyar PDP
  • ‘Sojojin Najeriya da na Ivory Coast 200 sun shiga domin tsaftace Jamhuriyar Benin’
  • Jam’iyyar PDP ta tabbatar da mutuwar mataimakin Gwamnan Bayelsa