Chelle Ya Fara Da Ƙafar Dama A Super Eagles
Published: 22nd, March 2025 GMT
Sabon Kocin tawagar Super Eagles ta Nijeriya Eric Chelle, ya fara jagorantar tawagar da ƙafar dama, bayan samun nasara a wasan farko da ya jagorance ta.
Chelle wanda ya zo Super Eagles watanni biyu da su ka gabata, ya jagoranci Super Eagles a wasan da su ka doke ƙasar Rwanda da ci biyu da nema a Amahoro.
Wasan shi ne zagaye na biyar a wasannin neman gurbi a gasar cin kofin Duniya da za a buga a shekarar 2026, Nijeriya na matsayi na 4 a rukunin C na gasar da maki 6 a wasanni 5, sai Afrika Ta Kudu dake jan ragamar rukunin, ƙasar Benin ta biyu sai Rwanda dake matsayi na uku.
Eric Chelle Ya Sake Bai Wa Ahmed Musa Damar Taka Leda A Super Eagles Ministan Harkokin Wajen Benin Ya Yi Wa Sinawa Gaisuwar Sabuwar ShekaraTsohon gwarzon ɗan wasan Afrika Victor Osimhen ne ya jefa wa Nijeriya duka kwallayenta biyu a wasan, Ademola Lookman da Samuel Chukwueze ne su ka taimakawa Osimhen wajen zura kwallayen a ragar masu masaukin bakin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Martanin Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Kan Ta’addancin ‘Yan Sahayoniyya ya Shiga Rana Ta Biyu
Martanin Iran game da ta’addancin haramtacciyar kasar Isra’ila na ci gaba a rana ta biyu
Ana ci gaba da mayar da martani mai girma na Iran game da harin da haramtacciyar kasar Isra’ila take kaiwa da makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuka ciki.
‘Yan mintoci da suka gabata a zaman wani bangare na biyu na “Alkawarin Gaskiya Na 3”, Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta harba daruruwan makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuka kan haramtacciyar kasar Isra’ila.
An harba wadannan makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuka ciki da kuma jiragen sama masu saukar ungulu daga Tehran da sauran garuruwan kasar Iran a matsayin wani mataki na murkushe laifuffukan da yahudawan sahayoniyya suka aikata a kan yankunan Jamhuriyar Musulunci ta Iran, kuma a zaman wani bangare na biyu na “Alkawarin Gaskiya na 3”.
Kafofin yada labaran yahudawan sahayoniyya sun watsa rahoton tashin gobara da hayaki a birnin Haifa da ke arewacin Falasdinu da aka mamaye.
An ga wuta da hayaki na tashi bayan da makamai masu linzami na Iran sun afkawa matatar mai ta Haifa da ke arewacin Falasdinu da aka mamaye. Sannan a cewar bayanan farko, an kashe fiye da mutane 10 a Haifa.