Fadin Yankin Da Ke Fama Da Zaizayar Kasa Na Kasar Sin Ya Ragu A 2024
Published: 22nd, March 2025 GMT
Ma’aikatar kula da albarkatun ruwa ta kasar Sin ta bayyana a jiya Juma’a cewa, fadin yankin kasar dake fama da zaizayar kasa ya ragu zuwa murabba’in kilomita miliyan 2.6019 a shekarar 2024, wanda ya samu raguwar murabba’in kilomita 25,700, idan aka kwatanta da na shekarar 2023.
Wadanann alkaluman wani bangare ne na sakamakon aikin sa ido kan zaizayar kasa a kasar Sin a shekarar 2024, wanda aka kammala a kwanan nan.
Wani jami’in ma’aikatar ya bayyana cewa, sakamakon da aka samu ya nuna cewa, ana samun ci gaba bisa daidaito wajen magance zaizayar kasa a kasar Sin, inda aka samu raguwar fadin yankin da ke fuskantar matsalar da ma karfin zaizayar kasa, gami da raguwar zaizayar kasa bisa dalilan ruwa da iska.
Manyan kogunan da suka hada da kogin Yangtze, Rawayen Kogi, da kogin Huaihe, sun kai kashi 73.19 cikin 100 na yankin da aka samu raguwar zaizayar kasa a fadin kasar baki daya. (Mohammed Yahaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: zaizayar kasa a kasar Sin
এছাড়াও পড়ুন:
Sojojin Kasar Iran Sun Ce Bazasu Dakatar Da Yaki ba Har Zuwa Samun Nasara A kan HKI
Babban kwamandan dokarun khatamul Ambiya (s) a nan birnin Tehran ya bayyana cewa sojojinsa zasu ci gaba da fafatawa da HKI har zuwa lokacinda zata dakatar da kawowa Iran yaki, ko kuma ta sami nasara a kansu,
Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto Janar Ali Shudmoni, yana fadar haka a yau Lahadi bayan da suke cilla makamai masu linzami da kuma jiragen yaki wadanda ake sarrafasu da nesa kan HKI a karon farko na rana, a cikin kwanaki uku da fara yakin.
Janar Shodmani ya kara da cewa zasu ci gaba da kaiwa yahudawan hare-hare har zuwa lokacinda zasu yi nadama sun daina yakin.
Kwamnatin ya bayyana cewa ya zuwa yanzu sun saminar kasar lalata cibiyoyin da jiragen yakin HKI suke shan makamashi wanda yake basu damar isa kasar Iran don kai hare-hare. Banda haka akwai nasarori da dama da suka samu a hare-haren wadanda nan gaba zasu bayyana.