Kudaden Da Ke Hannun Mutane Sun Ragu Zuwa Naira Tiriliyan 5 – Rahoto
Published: 25th, April 2025 GMT
Raguwar kudin a hannun mutane na iya zama wani bangare na kokarin rage matsin lamba kan hauhawar farashin kayayyaki da samun daidaiton tattalin arziki.
Baya ga raguwar kudade a hannun mutane, ajiyar a bankin CBN ya karu zuwa naira biliyan 28.52 a watan Maris na 2025, daga naira biliyan 27.57 a watan Fabrairun 2025.
A halin yanzu, ajiyar ko-ta kwana ba ta canza ba a naira miliyan 284.36 a cikin watanni uku.
Ajiyar banki yana nufin kudaden da Babban Bankin da bankunan kasuwanci ke rike da shi don tabbatar da hada-hadar kudade a cikin bangaren banki. Ci gaba da karuwar ajiyar bankuna wata alama ce ta kokarin CBN na tsare harkokin kudade da daidaita tattalin arziki.
Ya daidai wannan lokacin a bara, an bayyana cewa darajar kudin Nijeriya da ke yawo a hannun mutane ya karu zuwa naira tiriliyan 3.87 a karshen watan Maris na 2024.
Wannan ya nuna karuwa daga naira tiriliyan 3.69 a watan Fabrairu da naira tiriliyan 3.65 a watan Janairu. Bugu da kari, kudin da ke wajen bankuna kuma ya karuwa a cikin kwata na farko, ya karu daga naira tiriliyan 3.28 a watan Janairu zuwa naira tiriliyan 3.41 a watan Fabrairu, kuma ya kai naira tiriliyan 3.63 a watan Maris.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: naira tiriliyan 3
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Majalisar Abinci Mai Gina Jiki ta Jihar Jigawa
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya kaddamar da Majalisar Abinci Mai Gina Jiki ta Jihar Jigawa 774, inda ya tabbatar da kudurin gwamnatinsa na yaki da rashin abinci mai gina jiki da inganta yalwar abinci a fadin jihar.
An gudanar da kaddamarwar ne yayin ziyarar Mrs. Uju Rochas-Anwuka, mai bai wa Shugaban Kasa shawara ta musamman kan lafiya ( Karkashin Ofishin Mataimakin Shugaban Kasa), wacce ta je Jigawa domin kaddamar da shirin Nutrition 774 da ke karkashin shirin sabunta kudurori na Renewed Hope Agenda.
Gwamna Namadi ya bayyana cewa Jigawa ta kasance gaba a yaki da matsalar, tare da kafa shiri na musamman da aka yi wa lakabi da Masaki tun a 2020 domin fadakar da al’umma a matakin ƙasa, wanda ya amfanar da sama da mutum miliyan 1 da dubu 300.
Ya kara da cewa gwamnati na ware Naira Miliyan 13 da rabi a kowane wata domin tallafa wa shirin na Masaki, da kuma Naira Miliyan 250 a shekara, don sayen abinci da magani tare da UNICEF, yayin da Majalisar Dokoki ke bayar da Naira Miliyan 300 a shekara.
Haka kuma, sama da mata 600 sun samu horo a shirin abincin yara na Tom Brown don samar da abinci mai gina jiki a gida tare da hadin gwiwar hukumar NAFDAC.
Gwamnan ya ce sabuwar majalisar za ta hada kai da ma’aikatun gwamnati wajen tsara da aiwatar da manufofin abinci mai gina jiki, tare da nufin sanya Jigawa ta zama ta farko da za ta cimma burin shirin gwamnatin tarayya naNutrition 774.
A jawabinta, Mrs Uju ta ce shirin na daga cikin manyan shirye-shiryen gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, da nufin magance matsalar rashin abinci mai gina jiki a fadin kasar.
Usman Muhammad Zaria