Aminiya:
2025-06-15@13:20:16 GMT

An yi wa wata karya tiyatar ceton rai

Published: 22nd, March 2025 GMT

Wata karya ta hadiyi safa 24 da sauran kayan sawa, inda suka makale masa a mukamuki – lamarin da ya haifar da yi masa tiyatar ceton rai a Jihar California a Amurka, kamar yadda cibiyar kula da dabbobi ta bayyana.

Wata karya mai suna Luna, jinsin Bernese Mountain da ta shafe wata 7 tana fama da rashin lafiya, sakamakon hadiye wasu kayayyaki na mamallakinta a ranar 16 ga Fabrairu bayan kamar yadda Cibiyar Ba da Agajin Dabbobi ta Corona ta ce a cikin wani sakon da ta wallafa a Instagaram.

Za a hukunta ma’auratan da suka ci zarafin yarinya a kan mangwaro — Zulum Majalisar Wakilai ta musanta karɓar kuɗi kan dokar ta-ɓaci a Ribas

Lokacin da ta fara amai, an garzaya da ita zuwa asibitin dabbobi, inda wani likitan dabbobi ya bude cikinta, ya cire tufafin da ya haifar da toshewar hanjinta.

“Lokacin da ‘yan uwan masu karyar suka lura tana amai kuma tana cikin rashin lafiya mai tsauri, sai suka garzayo da ita wurinmu,” in ji cibiyar.

“Ba tare da bata lokaci ba, yanzu Luna yanzu ta fara kada wutsiyarta!” Ta kara da cewa “karyar tana da tsananin son safa “.

Cibiyar kula da lafiyar dabbobi ta saka hoton safa da aka cire daga hanjin karyar tare da hotunan D-ray na toshewar hanjinta, a cewar kafar Storyful, wanda ya fara gano labarin ceton karyar.

Safa 24 da sauran kayan da karyar ta hadiya bayan tiyatar ceton rai

Wasu hotuna sun nuna Luna – tana wasa – cikin farin ciki da kwanciyar hankali a kan gadon asibiti, bayan an yi mata tiyata.

Cibiyar ta yi gargadin cewa, wadanda suka mallaki karnuka idan suka “lura suna amai, ko alamar rashin lafiya” sai su yi sauri su tuntubi likitan dabbobi.”

“Ita wannan karyar ta musamman ce, kuma muna farin cikin samun labarin murmurewarta,” in ji wani sakon da wani ya wallafa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: karya Tiyata

এছাড়াও পড়ুন:

Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8

Kwanaki takwas bayan wata mummunar ambaliyar ruwa da ta mamaye garin Mokwa, hedikwatar Ƙaramar hukumar Mokwa a Jihar Neja, an gano gawar mutum ɗaya daga cikin waɗanda lamarin ya rutsa da su.

Mazauna garin sun shaida wa Daily Trust cewa, an tsinci gawar ne a ranar Alhamis a wata gona da ke kan hanyar wucewa kusa da wani wuri da aka fi sani da ‘dam’.

Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi

A cewar shaidun gani da ido, an kasa tantance wanda abin ya shafa saboda gawar ta lalace. An binne shi ne a inda aka gano gawarsa.

Wata mazauniyar yankin mai suna Tswata Mai Rubutu da ta zanta da Aminiya ta wayar tarho, ta ce an tsinci gawar a kan hanyar da ruwa ke wucewa.

“Gawar wani babban mutum ne, amma ba za mu iya gane shi ba saboda tuni ya fara lalacewa. An binne shi a wurin tun da ba a iya motsa gawar,” in ji shi.

An yi ƙoƙarin jin ta bakin Darakta Janar na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja, Abdullahi Baba Arah, domin ƙarin bayani lamarin ya ci tura.

Tun da farko hukumar ta tabbatar da mutuwar mutane 161, yayin da wasu da dama suka ɓace bayan iftila’in ambaliyar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda wani ɗan sanda ya rasu a hanyar zuwa ɗaurin aurensa
  • An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe
  • Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba
  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8
  • Gwamnatin Tarayya Ta Dukufa Wajen Karya Farashin Kayan Abinci – Minista
  • NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya
  • Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje
  • Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Afirka Sun Yi Alkawarin Karfafa Alaka
  • Mutum ɗaya ya tsira da ransa cikin 242 a hatsarin jirgin India