Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Natasha za ta sake komawa kotu kan hana ta shiga harabar majalisa

Dakatacciyar Sanatar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan, ta lashi takobin sake maka shugabancin Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio a gaban kotun daukaka kara bayan an hana ta shiga harabar majalisar a ranar Talata.

Cikin bacin rai, Natasha ta shaida wa ’yan jarida cewa za ta tattauna da lauyoyinta cikin gaggawa domin fara shigar da karar, tana mai cewa matakin ya saba da hukuncin kotun da ta bayar da umarnin a mayar da ita kan kujerarta.

Lamarin dai ya biyo bayan yadda jami’an tsaron da ke gadin majalisar suka tare hanya suka hana tawagar motocinta shiga majalisar, duk kuwa da umarnin kotu na mayar da ita.

HOTUNA: An ƙaddamar da aikin sabunta ginin Majalisar Dokokin Bauchi Majalisar Dattawa ta sahale wa Tinubu karɓo rancen $21bn a ƙetare

Ta kuma ce hatta dakatar da itan ma da farko ba ya kan ka’ida.

A cewar ta, “Yanzu zan je na tattauna da lauyoyina domin shirin daukaka kara alabasshi kotu ta fassara mana abin da ya faru. Ni mace ce mai bin dokokin kasa.”

Sanatar ta kuma yi alla-wadai da matakin da Shugaban Majalisar, Godswill Akpabio ya dauka na hana ta shigar, inda ta ce hakan tamkar raina kotu ne.

Ta kuma ce, “Akpabio bai fi karfin kundin tsarin mulkin Najeriya ba. Ina so ’yan Najeriya su sani cewa ba Ofishin Shugaban Majalisar Dattawa ne ya mayar da ni Sanata ba.

“Duk da cewa ya tafi daukaka kara, hakan ba yana nufin cewa ya soke hukuncin Mai Shari’a Binta Nyako ba ne kuma hakan ba zai dakatar da ni daga kasancewa Sanata ba.

“Mutanen Kogi ta Tsakiya ne suka zabe ni kuma su nake wakilta,” in ji Natasha.

Tun da farko dai Sanatar ta yi yunkurin shiga majalisar tare da magoya bayanta amma, amma aka hanata, dole sai da ta sauka ta tafi a kafa.

An dai girke tarin jami’an tsaron da ba a saba ganin irin su ba a majalisar, inda aka ga wasu jami’an na duba motoci tare da ma takaita yawan wadanda za su ajiya ababen hawa a wajen fakin na wajen majalisar.

Akalla an ga motocin sintiri na jami’an ’yan sanda guda biyar da aka girke a muhimman wuraren shiga majalisar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Sule Ya Ƙara Musanta Zargin Kare Ƴan Ta’adda A Nasarawa
  • Makarantun Kano Za Su Fara Hutun Ƙarshen Zango A Ranar Juma’a – Gwamnati
  • Shugaban Amurka Trump Ya Bukaci Gurfanar Da Tsohon Shugaban Amurka Barack Obama A gaban Kuliya
  • Natasha za ta sake komawa kotu kan hana ta shiga harabar majalisa
  • Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu
  • Sin Ta Samar Da Karin Guraben Aikin Yi Miliyan 6.95 A Rabin Farko Na Bana
  • Jami’an tsaro sun dakile yunkurin Sanata Natasha na shiga harabar Majalisa
  • Asibitin ATBUTH za ta fara gwajin rigakafin zazzaɓin Lassa
  • Kotu Ta Dage Shari’ar Zargin Cin Hanci Da Ake Yi Wa Shugaban KANSIEC Na Kano Zuwa Nuwamba
  • Jami’in Shari’ar Kasa Da Kasa Ya Bayyana Cewa: Harin Da Aka kai Kan Iran Babban Laifi Ne