Hare-haren Isra’ila sun yi sanadin shahadar falasdinawa kusan 1,000 a cikin sa’o’I 48
Published: 19th, March 2025 GMT
Rahotanni daga Gaza na cewa hare haren Isra’ila a baya bayan nan sun yi sanadin shahadar mutane kusan 1,000 a baya bayan nan wanda ke nuna irin girman barnar da gwamnatin sahayoniyan ke aikatawa a zirin.
Ma’aikatar lafiya ta Gaza ta ce sabon danyen aikin da Isra’ila ta yi ya kai ga kashe akalla mutane 970 cikin sa’o’i 48.
Wata sanarwa da ma’aikatar lafiya ta kasar ta fitar ta bayyana cewa, hare-haren wuce gona da iri da Isra’ila ta kaddamar a ranar Talata, sun yi sanadiyar mutuwar mutane akalla 970.
Wasu rahotanni na daban ce mutane 356 ne suka mutu a harin da aka kai ta sama, a cikin sa’a huda sannan akalla Falasdinawa 1,000 ne suka samu raunuka.
Wani babban jami’in Hamas ya shaidawa kamfanin dillancin labaran reuters cewa hare-haren na Isra’ila na nufin cewa Isra’ila ta kawo karshen tsagaita bude wuta a Gaza da aka fara a ranar 19 ga watan Janairu.
Mohammed Zaqout, babban darektan asibitocin Gaza, ya yi kira ga kasashen duniya da su shiga tsakani tare da tilastawa Isra’ila ba da damar samar da magunguna a cikin yankin.
Mata da yara da dama na daga cikin wadanda aka kashe
Ma’aikatar lafiya ta Gaza ta ce akalla Falasdinawa 61,700 ne aka tabbatar da mutuwarsu tare da jikkata 112,041 a yakin da Isra’ila ke yi a Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran ta bayyana halin da Falasdinawa ke ciki da rauni mufi da aka wa dan adam a doron kasa
Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta bayyana halin da Falasdinu ke ciki da rauni mafi muni da aka aikata kan bil adama a doron kasa.
A yayin bikin Ranar Falasdinu ta Duniya, Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta sake nanata goyon bayan Jamhuriyar Musulunci ta Iran ke bai wa Falasdinawa, tana mai bayyana halin da suke ciki a matsayin “mafi munin rauni ga lamirin dan adam, Kamar yadda mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran, Esmail Baghai, ya bayyana.
Kisan kare dangi, wanda ya fara a watan Oktoba na 2023, ya kashe Falasdinawa sama da 70,000, galibi mata da yara, kuma ya mayar da yankin kufai.
Yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma a farkon watan Oktoba tare da kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas a Gaza, ba ta tabaka komai ba, hasali ma baiwa Isra’ila damar ci gaba da aiwatar da kisan kare dangi da take yi a Gaza.
Mista Baghai ya yi Allah wadai da ci gaba da tashin hankali da zaluncin da ake yi wa Falasdinawa, sannan ya yi Allah wadai da rawar da Amurka da kawayenta ke takawa wajen rashin hukunta wadanda suka aikata wadannan ta’asa.
Ya yi kira ga kasashen duniya da su cika wajibcinsu na shari’a ta hanyar goyon bayan “jajircewar al’ummar Falasdinawa na halal don kawo karshen mamayar da kuma tabbatar da ‘yancinsu na cin gashin kansu.”
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka An yi gangami a fadin duniya a zagayowar ranar Falasdinu November 30, 2025 Cinikin Kasashen Waje na Iran Ya Zarce Dala Biliyan 76.5 November 30, 2025 Najeriya : Sojoji sun kubutar da yan mata 12 da mayakan ISWAP November 30, 2025 An sake zabar Eto’o a matsayin Shugaban Hukumar kwallon kafa ta Kamaru November 30, 2025 Shugaban Najeriya Ya Mika Sunaye Sabbin Jakadun Kasar su 32 Ga Majalisa Domin Tantancewa November 30, 2025 Hizbullah Ta Bukaci Shugaban Cocin Katolika Na Duniya Yayi Tir Da Hare-haren Isra’ila November 30, 2025 Iran: Kalaman Da Trump Yayi Na Rufe Sararin Samaniyar Kasar Venuzuwela Ya Sabama Doka. November 30, 2025 Shugaban Pakistan Yayi Kira Da A Gudanar Da Bincike Kan Laifukan Yaki Da HKI Ke Tafkawa November 30, 2025 MDD Ta Bukaci Isra’ila Da ta Kawo Karshen Mamayar Da Tayi wa Yankunan Falasdinawa November 30, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 163 November 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci