Hare-haren Isra’ila sun yi sanadin shahadar falasdinawa kusan 1,000 a cikin sa’o’I 48
Published: 19th, March 2025 GMT
Rahotanni daga Gaza na cewa hare haren Isra’ila a baya bayan nan sun yi sanadin shahadar mutane kusan 1,000 a baya bayan nan wanda ke nuna irin girman barnar da gwamnatin sahayoniyan ke aikatawa a zirin.
Ma’aikatar lafiya ta Gaza ta ce sabon danyen aikin da Isra’ila ta yi ya kai ga kashe akalla mutane 970 cikin sa’o’i 48.
Wata sanarwa da ma’aikatar lafiya ta kasar ta fitar ta bayyana cewa, hare-haren wuce gona da iri da Isra’ila ta kaddamar a ranar Talata, sun yi sanadiyar mutuwar mutane akalla 970.
Wasu rahotanni na daban ce mutane 356 ne suka mutu a harin da aka kai ta sama, a cikin sa’a huda sannan akalla Falasdinawa 1,000 ne suka samu raunuka.
Wani babban jami’in Hamas ya shaidawa kamfanin dillancin labaran reuters cewa hare-haren na Isra’ila na nufin cewa Isra’ila ta kawo karshen tsagaita bude wuta a Gaza da aka fara a ranar 19 ga watan Janairu.
Mohammed Zaqout, babban darektan asibitocin Gaza, ya yi kira ga kasashen duniya da su shiga tsakani tare da tilastawa Isra’ila ba da damar samar da magunguna a cikin yankin.
Mata da yara da dama na daga cikin wadanda aka kashe
Ma’aikatar lafiya ta Gaza ta ce akalla Falasdinawa 61,700 ne aka tabbatar da mutuwarsu tare da jikkata 112,041 a yakin da Isra’ila ke yi a Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Bata Taba yin Watsi Da Diplomasiya Ba Amurka Ce Ke Kai Mutane Bango
Ministan harkokin wajen kasar iran Abbas Araqchi ya fadi cewa iran tana ci gaba da aiki da diplomasiya duk da cikas da Amurka take kawo wa a tattaunawar da ba ta kai tsaye ba, ganin cewa Amurka tana amfani da karfi wajen gudanar da harkokin duniya .
Yace idan bangaren Amurka ta nuna shirinta na yin tattaunawa bisa mutunta jina da kare munufofin kowa, to iran za ta iya duba lamarin, saboda bamu taba barin teburin tattaunawa ba , saboda it ace ingantacciyar hanya ta fuskantar alumma.
Dangane da Ziyarar da ya kai a bayan bayan nan a garin muscat da kuma tarurrukan da yayi, babban jami’in diplomasiyar iran yace babban abin takaici shi ne inda dokokin kasa da kasa da tsarin duniya suke kara yin tasiri ga yanayin Amurka na amfani da karfi a dangantakar kasa da kasa.
Daga karshe yace akwai bukatar gina tsaro a iyakokin kasashen yankin ba tare da tsoma bakin kasashen waje ma’abota girman kai ba, wanda wannan ne zai kara samar da yarda da zai sa akulla yarjejeniyar tsaro a yankin tekun fasha.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugaban Kungiyar ECOWAS Ya Gana Da Shugaban Mulki Soji Na Kasar Guinea Bissau December 2, 2025 An Bude Taron Bikin Cika Shakaru 41 Da Kafa Kungiyar Tattalin Arziki Ta ECO A nan Tehran December 2, 2025 Araghchi: Halayyar Amurka ce yin matsin lamba maimakon diflomasiyya a dangantaka ta kasa da kasa December 2, 2025 Aljeriya: Taron Kasashen Afirka Don Amincewa Da Mulkin Mallaka A Matsayin Laifi December 2, 2025 Lebanon: An Gudanar Da Taron Musulunci da Kiristanci a Beirut tare da halartar Paparoma December 2, 2025 Chuck Schumer: Trump Ba Shi da Ikon Kaddamar da Yaki Kan Venezuela December 2, 2025 Najeriya: Matatar Dangote Za Ta Mika Tataccen Mai Lita Biliyan 1.5 A Watan Disamba December 2, 2025 Ramaphosa ya yi watsi da barazanar Trump na ware Afirka ta Kudu daga G20 December 2, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 165 December 1, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan 164 December 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci