Hare-haren Isra’ila sun yi sanadin shahadar falasdinawa kusan 1,000 a cikin sa’o’I 48
Published: 19th, March 2025 GMT
Rahotanni daga Gaza na cewa hare haren Isra’ila a baya bayan nan sun yi sanadin shahadar mutane kusan 1,000 a baya bayan nan wanda ke nuna irin girman barnar da gwamnatin sahayoniyan ke aikatawa a zirin.
Ma’aikatar lafiya ta Gaza ta ce sabon danyen aikin da Isra’ila ta yi ya kai ga kashe akalla mutane 970 cikin sa’o’i 48.
Wata sanarwa da ma’aikatar lafiya ta kasar ta fitar ta bayyana cewa, hare-haren wuce gona da iri da Isra’ila ta kaddamar a ranar Talata, sun yi sanadiyar mutuwar mutane akalla 970.
Wasu rahotanni na daban ce mutane 356 ne suka mutu a harin da aka kai ta sama, a cikin sa’a huda sannan akalla Falasdinawa 1,000 ne suka samu raunuka.
Wani babban jami’in Hamas ya shaidawa kamfanin dillancin labaran reuters cewa hare-haren na Isra’ila na nufin cewa Isra’ila ta kawo karshen tsagaita bude wuta a Gaza da aka fara a ranar 19 ga watan Janairu.
Mohammed Zaqout, babban darektan asibitocin Gaza, ya yi kira ga kasashen duniya da su shiga tsakani tare da tilastawa Isra’ila ba da damar samar da magunguna a cikin yankin.
Mata da yara da dama na daga cikin wadanda aka kashe
Ma’aikatar lafiya ta Gaza ta ce akalla Falasdinawa 61,700 ne aka tabbatar da mutuwarsu tare da jikkata 112,041 a yakin da Isra’ila ke yi a Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Jami’ar MDD Ta Musamman A Falasdinu Ta Soki Shirin Trump Kan Tsagaita Bude Wuta A Gaza
Jami’ar Majalisar Dinkin Duniya ta musamman kan kare hakkin bil’adama a yankin Falasdinu ta soki shirin Trump kan Gaza tana mai jaddada cewa: “Yana daga mafi munin cin mutuncin da ta taɓa gani a rayuwarta
Jami’ar Majalisar Dinkin Duniya ta Musamman kan Kare Haƙƙin Dan Adam a Yankin Falasɗinu, Francesca Albanese, ta bayyana shirin zaman lafiya na Shugaban Amurka Donald Trump a Gaza a matsayin “mafi munin cin mutunci da na taɓa gani a rayuwarta,” tana mai tabbatar da cewa Shirin ba shi da haƙƙi na shari’a da na ɗabi’a.
Albanese ta bayyana cewa: Ba ta da imani da tsarin siyasa na yanzu da ake Shirin aiwatarwa a Gaza ba, tana mai ƙarawa da cewa, “Ba za a iya gina yarjejeniyar zaman lafiya bisa karya dokokin ƙasa da ƙasa ba, kuma ba ta amince da mutanen da ke da alhakin gudanar da wannan tsari ba.” Tana mai nuni da cewa: Gwamnatin mamayar Isra’ila ba ta son ci gaba da zaman Falasɗinawa a Gaza, tana mai bayyana cewa wannan matsayi ya kasance bayyananne tsawon shekaru, a cewarta a wata hira da jaridar iPaper ta Birtaniya.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Sojojin Isra’ila Na Kai Hare-Hare Kan Gaza A Matsayin Keta Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta October 29, 2025 Larijani: Dangantakar Iran da Pakistan na iya komawa babban hadin gwiwa a tsakaninsu October 29, 2025 Iraki: Al-Sudani ya kirayi Irakawa da suka kare kundin tsarin Mulki ta hanyar fitowa zabe October 29, 2025 Abiy Ahmed: Habasha na bukatar sulhu kan rikicin teku tsakaninta da Eritrea October 29, 2025 Hare-haren Isra’ila Sun Kashe Mutane fiye da 60 a Gaza October 29, 2025 Senegal ta sake gano wasu shaidu kan kisan gillar da aka yi a lokacin mulkin mallaka October 29, 2025 An bude taron ministocin cikin gida na kungiyar ECO October 28, 2025 Sojojin Isra’ila sun kashe Falasdinawa uku a Yammacin Kogin Jordan October 28, 2025 Hamas : Netanyahu Yana kokarin wargaza yarjejeniyar tsagaita wuta October 28, 2025 China za ta dauki mataki idan takunkuman Iran sun shafi muradunta October 28, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci