Hare-haren Isra’ila sun yi sanadin shahadar falasdinawa kusan 1,000 a cikin sa’o’I 48
Published: 19th, March 2025 GMT
Rahotanni daga Gaza na cewa hare haren Isra’ila a baya bayan nan sun yi sanadin shahadar mutane kusan 1,000 a baya bayan nan wanda ke nuna irin girman barnar da gwamnatin sahayoniyan ke aikatawa a zirin.
Ma’aikatar lafiya ta Gaza ta ce sabon danyen aikin da Isra’ila ta yi ya kai ga kashe akalla mutane 970 cikin sa’o’i 48.
Wata sanarwa da ma’aikatar lafiya ta kasar ta fitar ta bayyana cewa, hare-haren wuce gona da iri da Isra’ila ta kaddamar a ranar Talata, sun yi sanadiyar mutuwar mutane akalla 970.
Wasu rahotanni na daban ce mutane 356 ne suka mutu a harin da aka kai ta sama, a cikin sa’a huda sannan akalla Falasdinawa 1,000 ne suka samu raunuka.
Wani babban jami’in Hamas ya shaidawa kamfanin dillancin labaran reuters cewa hare-haren na Isra’ila na nufin cewa Isra’ila ta kawo karshen tsagaita bude wuta a Gaza da aka fara a ranar 19 ga watan Janairu.
Mohammed Zaqout, babban darektan asibitocin Gaza, ya yi kira ga kasashen duniya da su shiga tsakani tare da tilastawa Isra’ila ba da damar samar da magunguna a cikin yankin.
Mata da yara da dama na daga cikin wadanda aka kashe
Ma’aikatar lafiya ta Gaza ta ce akalla Falasdinawa 61,700 ne aka tabbatar da mutuwarsu tare da jikkata 112,041 a yakin da Isra’ila ke yi a Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Barin jama’a su kare kansu ne ke rura rashin tsaro — Sojoji
Rundunar Sojin Najeriya, ta ce barin jama’a da aka yi don su kare kansu ne ke rura wutar rikici a Jihar Filato.
Birgediya Janar MA Etsy-Ndagi, Shugaban Hulɗar Sojoji Da Fararen Hula ne, ya bayyana haka a lokacin da yake hira da ’yan jarida a Jos.
An rufe duk makarantu a Kebbi Ma’aikatan lantarki na shirin shiga yajin aiki a faɗin NajeriyaYa ce barin al’umma domin su kare kansu bai haifar da ɗai mai ido ba, illa ƙara tsananta rikice-rikice.
Jihar Filato na fama da rikice-rikice tun daga shekarar 2001, inda mutane da dama suka rasu, wasu kuma suka jikkata.
Wasu ƙungiyoyi a jihar sun yi kiran da a bar jama’a su kare kansu saboda yawan hare-hare da suke fuskanta.
Sai dai Janar Etsy-Ndagi ya ce rikici tsakanin manoma da makiyaya ya koma wani yanayi na ɗaukar fansa, inda kowane ɓangare ke kai wa juna hari.
Ya ce dole ne sojoji su ƙwace dukkanin makaman da ke hannun jama’ar gari domin kawo ƙarshen hare-haren ramuwar gayya.
A cewarsa: “Domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi, dole mu tabbatar an ƙwace makamai daga hannun kowa, kuma babu wanda yake ƙera makami. Hakan ne zai ba da damar samun zaman lafiya.”
Ya ƙara da cewa: “Rikicin ya ɗauki wani sabon salo. Manoma suna zargin makiyaya da lalata musu amfanin gona, makiyaya kuma suna zargin manoma da satar musu shanu.
“Rikici na tsananta. Ba ma goyon bayan al’umma su kare kansu, muna kare jama’ar da ke fuskantar tashin hankali kuma muna ba su goyon baya.”
Ya kuma buƙaci mutanen jihar su zauna lafiya da juna tare da haɗa kai da jami’an tsaro domin tabbatar da zaman lafiya da ci gaban yankunansu.
Ya jaddada cewar Rundunar Sojin Najeriya za ta ci gaba da yaƙar matsalar tsaro a sassan ƙasar nan.