Leadership News Hausa:
2025-04-30@17:32:26 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [12]

Published: 20th, March 2025 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [12]

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [10] Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [9]

Fashin Baƙi:

Ibn Juzai, ya bayyana nau’ikan rai uku da suka shafi halayyar ɗan’adam, bisa koyarwar addinin Islama. Waɗannan nau’ikan rai suna da nasaba da matsayin mutum a cikin halayensa da alaƙarsa da Allah.

Ga cikakken bayani kan kowanne daga cikinsu:

1. Rai Mai Umarni da Mummuna (النَّفْسُ الأَمَّارَةُ بِالسُّوءِ): Wannan ita ce zuciyar da take yawan umartar mai ita da aikata sharri da mugunta, da saɓo. Allah Ya ambaci irin wannan rai a cikin Alƙur’ani inda Ya ce:” Ba kuma ina wanke kaina ba ne. Shakka babu ɗabi’ar rai ce ta umurci mutum da yin mummunan abu, sai fa wanda Ubangiji Ya yi wa jin ƙai. Lalle Ubangiji Mai gafara ne Mai jin ƙai” Suratu Yusuf aya ta 53.

Irin wannan rai tana da alaƙa da sha’awa, da son zuciya, da rinjayen Shaiɗan a kanta. Duk wanda yake a wannan matsayi, yana yawan aikata laifi ba tare da jin kunya ba. Sai dai idan Allah Ya yi masa rahama, zai farka daga halinsa ya nemi gafara ya tuba.

Alamomin Rai Mummuna: Yawan aikata zunubi ba tare da nadama ba.
Jin daɗi da mugunta da zalunci.
Rashin kulawa da umarnin Allah da hani.
Bin son zuciya da jin daɗin duniya fiye da lahira.

Hanyoyin Gyara Irin Wannan Rai:

● Neman gafarar Allah akai-akai.
● Yawan ambaton Allah (zikiri) don rage rinjayen sha’awa.

●Yin hijira daga munanan abokai ko yanayi.
● Cusa wa rai ƙaunar ibada da karatun Alƙur’ani.

2. Rai Mai Yawan Zargin Kanta (النَّفْسُ اللَّوَّامَةُ):
Wannan ita ce zuciyar da take tsawatar da mai ita a lokacin da ya aikata kuskure,ko zai aikata shi. Wannan nau’in rai yana matakin tsaka-tsaki tsakanin mugunta da kyautatawa. Allah Ya ambaci wannan rai a cikin Alƙur’ani, inda Ya ce:” Ina rantsuwa da rai mai yawan zargin kanta.” Suratul Ƙiyama aya ta 2.

Mutumin da yake da wannan rai yana aikata laifi amma daga baya zuciyarsa tana yi masa tir, tana sa shi jin nadama. Wannan nadama ita ce take jawo tuba da gyara hali.

Alamomin Rai Mai Yawan Zargin Kanta:

● Yawan jin laifi da nadama bayan aikata kuskure.
● Farkawa daga barci na gafala idan aka yi laifi.
●Rashin kwanciyar hankali yayin aikata haram.
● Son gyara hali da tuba.

Hanyoyin Ƙarfafa Rai Mai Yawan Zargin Kanta:

● Cusa wa zuciya son Allah da Manzonsa.
● Taimaka wa rai da kyakkyawan abokai.
● Rayuwa a cikin yanayi mai tsafta da ibada.
● Yawan karanta tarihin mutanen kirki don yin koyi da su.

3. Rai Mai Nutsuwa (النَّفْسُ الْمُطْمَئِنَّةُ): Wannan ita ce zuciyar da ta samu cikakken natsuwa da yarda da hukuncin Allah. Wannan mataki ne mafi girma a cikin halayyar rai. Allah Ya ambaci irin wannan rai a Alƙur’ani inda Ya ce:” Ya kai wannan rai mai nutsuwa. Ka koma zuwa ga Ubangijinka kana mai yarda da sakamako abin yarda. Don haka, ka shiga cikin bayina. Ka kuma shiga Aljannata.” Suratul Fajri aya ta 27-30.

Wannan matakin na rai yana ga mutanen da suka sami cikakkiyar ɗa’a da biyayya ga Allah da Manzonsa (S.A.W). Sun tsarkake zukatansu daga son zuciya, da hassada, da riya, da zalunci. Duk wata fitina da ta zo masu, sun yarda da cewa ƙaddarar Allah ce, don haka ba sa firgita ko damuwa.

Alamomin Rai Mai Nutsuwa:

● Tsananin ƙaunar Allah da Manzonsa fiye da komai.
● Cikakkiyar yarda da ƙaddara, mai daɗi ko akasin haka.
● Jin daɗin ibada da guje wa sharri.
● Kyautatawa ga mutane ba tare da neman lada a duniya ba.
● Jin daɗin rayuwa ko da an sami wahala.

Hanyoyin Samun Rai Mai Nutsuwa:

● Yawaita karatun Al-Qur’ani da nazarin ma’anoninsa.
● Yin addu’a don tsarkake zuciya daga cututtukan rai.
● Yawaita tunani a kan lahira da rayuwar gaskiya.
● Gujewa duniya da halayenta marasa amfani.

Waɗannan nau’ikan rai suna nuni da matakin da mutum yake a cikin bautar Allah. Duk wani mai imani yana ƙoƙarin tashi daga rai mai umurni da mummuna zuwa rai mai yawan zargin kanta, sa’an nan zuwa rai mai nutsuwa. Wannan tafiya tana buƙatar dagewa da ibada, sabo da zuciya na da ƙarfi wajen rinjayar hali.

Ibn Juzai Allah Ya yi masa rahama ya bayyana waɗannan matsayin domin su zama ginshiƙin gyara hali da kyautata rayuwa ta ibada. Duk wanda yake aiki da wannan koyarwar, zai iya cimma babban matsayi na kusanci da Allah, wanda a ƙarshe zai kai shi ga samun dacewa da rahama a duniya da lahira.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Abu Razina Nuhu Ubale Paki Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

Kissoshin Rayuwa: Imam Hassan (a) 115

115-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissiso da suka zo cikin alkur’ani mai girma ko kuma cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin dastane rastan, ko kum littafin mathnawi na maulana Jalaluddeen rumi. Ko kuma cikin wasu littafan da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu a cikin shirimmu na yau.

///… Masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata, a kuma cikin sirar Imam Al-hassan limami na biyu daga cikin limamai masu tsarki daga iyalan gidan manzon All..(s), kuma da na farko ga Fatimah(s) diyar manzon All..(s), sannan jikansa na farko.

A cikin shirimmu da ya gabata, mun ji yadda wasu malaman tarihi suka kawo wasu hadisai wadanda basu inganta ba suka jinginawa Imam Alhassan Almujtaba (a) dangane da son da yakewa khalifa na ukku wasu Uthman bin Affan, mun gudanar da bincike cikin daya daga cikin hadisan a sanadi da kuma mataninsa inda muka tabbatar da cewa , Mada’ini wanda aka ruwaito wannan hadisin, nasibi ne, wato wata jama’a wacce ta ke addini da kiyayya ga iyalan gidan manzon All..(s), har’ila yau yana kirkiro hadisan na kariya ya jinganawa manzon All..(s) na muzantasu da kuma kirkiro wasu hadisan daga manzon All..(s) na yabon banu umayya.

Sannan a matanin hadisin mun bayyana kariyar zance mai cewa Imam Hassan yana zargin babansa Imam Ali (a) da hannu a kashe Uthman dan Affan, sannan yana tare da mahaifinsa, manya-manyan yake-yake guda biyu da yayi a lokacin khalifancinsa, da wadanda  suke tuhumarsa da zubar da jinin Khalifa Uthman.

Wato yake-yaken Jamal da Siffin. Imam Hassan (a) ya yaki wadannan makiyan mahaifinsa wadanda suke zarginsa da hannu a kissan Uthman. Kuma bamu taba sanin akwai sabani tsakanin Imam Ali (a) da yayansa Alhassan da Alhussain (a).

Daga karshen mun kawo maku yadda manyamanayn sahabban manzon All..(s) da suka rage a Madina suka rubuta wasi ku zuwa sauran sahabbansa a sauran yankuna na daular musulunci suna neman taimakonsu don kauda Khalifa uthman daga khalifanci, saboda ya sabawa littafin All..da sunnar manzon All..da kuma siran khalifofin da suka gabata. Sun koka kan yadda ya mika al-amuran daular musulunci ga danginsa banu Umayya suna satar dukiyar al-umma sannan sun barsu da talauci.

Mun bayyana cewa akwai abubun lura a cikin wannan wasikar kamar haka,

1-Sunan zarginsa na kin amfani da littafin All..

02-Sauya sunnan manzon All..(s) da kuma, yayi watsi da ita,

03-yayi watsi ga hanyar khalifofin biyu da suka gabace shi wato Abubakar da Umar

04- Ya kauda ma’anar khalifancin manzon All..(s) daga yadda yakamata ta kasance,

5-Kwace dukkan duniyar Al-ammu da kuka sarrafata a wasu wurare kebantattu, wato kashe ta kan dangin khalifa wato Banu Umayya.

Malaman tarihi sun bayyana cewa, wadannan al-amura sun girgiza daular musulunci, kuma sun kusan su rusata.

Sannan mun bayyana cewa wadanda suke sukan shugabancin Khalifa Uthman sun rubuta wata wasika ga murabiduna, wato wadanda suke kula da kan iyakokin daular musulunci daga cikin sahabbai, sun bukacesu su dawo madina don tsada khalifancin manzon All..(a), don tabbatar da khaifancin ya dawo kan yadda yakamata ya kasanci.

Ga kuma matanin wasikar kamar haka.

{Lalle ku, kun fita ne don ku yi jihadi a kan tafarkin All..mai girma da daukaka, kuna neman kare addinin Muhammad (s) to lalle khalifanku ya lalata addnin Muhammadu, ku dawo ku tsaida shi,…}.

Banda haka a lokacinda wasikun nan suka isa yankuna da dama na daular musulunci sun yi ta aika tawaga don ganin abinda yake faruwa a Madina, sannan tawagogi da suka isa Madina don ganewa idanunsu abubuwan da suke faruwa, da kuma tattauna matsalolin da kuma yadda za’a magance su, sun hada da.

Tawaga daga kasar Masar, kafin haka akwai mutane 700 da suka tura tun farko bayan da suka kama wani bawan Khalifa Uthman wanda ake kira warsh dauke da wasikar Khalifa zuwa dan uwansa gwamnan Masar Abdullahi ibn Abisharkh, na ya kashe sui dan sun isa da sabon kwamna Muhammad dan Abubakar.

A wannan karon mutanen masar sun aiki mutane 400. Tare da jagorancin Muhammad dan Abubakar wanda dama yana manina, da Abdrrahman dan Udais Al-balawi.

2-sai tawagar Kufa wanda ya hada da Malik dan Ashtar, Zaidu dan Sauhan Al-Abdi, da Ziyad dan Annadhir Al-harithy. Da abdullahi dan Asam Al-Amuri da shugabansu gaba daya, Amru dan Ah-tham .

03-sai tawagar Basra wacce ta hada da Hakin dan Jibilah, tere da wasu mutane 100. Bayan haka wasu khamsin sun bisu. A cikinsu akwai Zarih dan Abidi Al-Abdi, da bishru dan shuraih Alkaisi, da dan Mahrash, da wasunsu daga cikin fitattun mutane kuma sanannu na Basra.

A lokacinda wadannan tawagogi suka isa Madina an yi maraba da su, kuma nag ode masu da karban kiran da aka yi masu, sannan sun tattauna da sauran sahabbai da kuma musulmai dan al-amuran da suka faru, da kuma irin mummunan halin da musulmi suka shiga ciki saboda yadda Khalifa Uthman ya sauya al-amura da dama, daga cikin ya hanasu dukiyoyinsu, wadanda suka saba samu a zamanin khalifofin da suka gabata. Ko kuma ya fita daga tsarin da manzon All..(s) yake raba dukiya a cikin al-umma.

Bayan yan kwanaki sai mutanen kasar masar sun ga cewa kafin ko me da farko a rubutawa khalifa Usman  wasika, a yi masa nisiha kan ya dawo kan tafarkin da ya dace ga kuma kadan daga cikin abinda wasikar ta kunsa.

Bayan Basmala da salati ga manzon All..(s) da kuma godiya ga All..sai suka ce

(bayan haka, ka sani kan cewa, {Lalle All..baya sauya halin da mutane suke ciki sai sai sun sauya halinsu, muna hadaka da All..kuma muna sake hadaka da All..Lalle kai kana cikin duniya mai gucewa, … .. kuma kada ka manta da rabon a lahira, kada duniya ta rudeka, kuma ka san cewa mu don All..muke yi, kuma don All…muke fushi. Kuma muna neman yardarm All.. ne, kuma lalle ba zamu dauke takubbammu daga wuyoyimmu ba saika tuba daga abubuwan da ka aikata mana, tuba mai tsanani kuma a fili, wannan shi ne maganarmu da kai, sannan bukatarmu a gareka, All..ne mai karban uzurimmu dangane da kai..wassalam…}.

A lokacinda Khalifa Uthman ya karanta sai ya ji tsoro. Sai Mughira ya nemi izininsa yayi Magana da mutane, sai ya bashi izini, a lokacinda suka ganshi sai suka daga murya suna cewa: Ya makaho  koma ya Fajiri koma ya fasiki koma.ya koma ya kasa Magana da su.

Sai Uthman ya kira Amru dan Asi, ya bukaci yayi Magana da su, ya amince, amma a lokacinda suka ganshi, sai yayi masu, sallama ba wanda ya amsa daga cikinsu,  suka daga murya suna cewa: Ko koma ya makiyin All.. ka kuma ya dan Nabigha. Kai ba amintecce ne a wajemmu ba kuma mai aminci ba.

A nan sai Khalifa Uthman ya fahinci cewa babu wanda zai taimaka masa sai Amirulminina Aliyu dan Abitalib (a), sai ya nemi taimakonsa, ya fada masa cewa, yayi kira ga mutane zuwa ga Alkur’ani mai girma da sunnar annabinsa.

Sai Imam ya amince, amma da sharudda kan cewa, ya yi masa alkawali tsakaninsa da All..zai yi aiki da abinda ya fada. Sai ya yi alkawali zai zai cika alkawalinsa, za iyi aiki da abinda ya fada.

Sai Imam (a) ya je wajen mutane, shima a lokacinda suka ganshi suka ce, koma , sai yace a’a na zo maku da cewa, za’a yi aiki da littafin All.., kuma za’a sauya duk abinda kuka yi fushi dominsa. Sai ya fada masu abinda khlifa ya bada.  Sai suka ce: Ka lamunce mana haka zai faru? Sai yace :ee. Sai suka ce mun yarda.   

Sai ya shigar da manya manya daga fitattun mutane  wajen Uthman, sai suka yi ta sukansa, sannan suka ce, ya Sanya abinda ya yi alkawali na aiki da littafin All..da kuma sunnar manzon All..(s) da kuma bawa musulmi hakkinsu da ake basu.

Sai ya amince ya rubuta ya basu sannan suka karbi takardan suka kama hanyar masar.

Wannan shi ne nassin abinda ya rubuta ya basu’

{Wannan rubutun daga bawan All..Uthman Amirulmuminina zuwa ga wadanda suke sukansa daga cikin muminai da musulmai, kan cewa hakkinsu ne in yi aiki da littafin All..da sunnar annabinsa a cikinu, za’a bawa talaka hakkinsa, wanda yake cikin tsoro a amintar da shi, wanda aka kora adawo da shi …kuma za’a samar da kudade ga musulmi. Sannan Aliyu dan Abitalib (a) shi ne mai lamuncewa muminai, kuma wajibi ne ga Uthman ya cika alkawalin da ya dauka cikin wannan rubutun}.

Banda haka Zubair dan Awwam, Talha dan Ubaidullahi,Sa’du dan Abi wallas, Abdullahi dan Umar, Zaidu dan Thabit, Sahal dan Hunaif,, Abu ayyuba Khalid dan zaid, kuma anyi wannan rubutun a cikin watan Zulkida shekara ta shekara 35.

Masu sauraro a nan zamu dasa aya a cikin shirimmu nay au sai kuma wata fitowa idan All..ya kaimu. Wassalau alaikum warahamatullahi wa barakathu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • DAGA LARABA: Asarar Da Hausawa Ke Tafkawa Sakamakon Bacewar Tatsuniya
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Na Iran Ya Ce: Maganar ‘Yan Sahayoniyya Rudu Ne Maras Amfani
  • Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
  • Arsenal Da PSG: Wa Zai Yi Nasara A Gasar Zakarun Turai A Yau?
  • NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya
  • Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku
  • Jagora Ya Bada Umurnin A Gudanar Bincike Mai Zurfi A Fashewar Tashar Jiragen Ruwa Na Shaheed Rajae
  • Kissoshin Rayuwa: Imam Hassan (a) 115
  • Kissoshin Rayuwa: Imam Al-Hassan 114
  • Yadda matsalar ƙwacen waya da faɗan daba ke addabar Kano