Leadership News Hausa:
2025-12-04@09:19:19 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [12]

Published: 20th, March 2025 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [12]

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [10] Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [9]

Fashin Baƙi:

Ibn Juzai, ya bayyana nau’ikan rai uku da suka shafi halayyar ɗan’adam, bisa koyarwar addinin Islama. Waɗannan nau’ikan rai suna da nasaba da matsayin mutum a cikin halayensa da alaƙarsa da Allah.

Ga cikakken bayani kan kowanne daga cikinsu:

1. Rai Mai Umarni da Mummuna (النَّفْسُ الأَمَّارَةُ بِالسُّوءِ): Wannan ita ce zuciyar da take yawan umartar mai ita da aikata sharri da mugunta, da saɓo. Allah Ya ambaci irin wannan rai a cikin Alƙur’ani inda Ya ce:” Ba kuma ina wanke kaina ba ne. Shakka babu ɗabi’ar rai ce ta umurci mutum da yin mummunan abu, sai fa wanda Ubangiji Ya yi wa jin ƙai. Lalle Ubangiji Mai gafara ne Mai jin ƙai” Suratu Yusuf aya ta 53.

Irin wannan rai tana da alaƙa da sha’awa, da son zuciya, da rinjayen Shaiɗan a kanta. Duk wanda yake a wannan matsayi, yana yawan aikata laifi ba tare da jin kunya ba. Sai dai idan Allah Ya yi masa rahama, zai farka daga halinsa ya nemi gafara ya tuba.

Alamomin Rai Mummuna: Yawan aikata zunubi ba tare da nadama ba.
Jin daɗi da mugunta da zalunci.
Rashin kulawa da umarnin Allah da hani.
Bin son zuciya da jin daɗin duniya fiye da lahira.

Hanyoyin Gyara Irin Wannan Rai:

● Neman gafarar Allah akai-akai.
● Yawan ambaton Allah (zikiri) don rage rinjayen sha’awa.

●Yin hijira daga munanan abokai ko yanayi.
● Cusa wa rai ƙaunar ibada da karatun Alƙur’ani.

2. Rai Mai Yawan Zargin Kanta (النَّفْسُ اللَّوَّامَةُ):
Wannan ita ce zuciyar da take tsawatar da mai ita a lokacin da ya aikata kuskure,ko zai aikata shi. Wannan nau’in rai yana matakin tsaka-tsaki tsakanin mugunta da kyautatawa. Allah Ya ambaci wannan rai a cikin Alƙur’ani, inda Ya ce:” Ina rantsuwa da rai mai yawan zargin kanta.” Suratul Ƙiyama aya ta 2.

Mutumin da yake da wannan rai yana aikata laifi amma daga baya zuciyarsa tana yi masa tir, tana sa shi jin nadama. Wannan nadama ita ce take jawo tuba da gyara hali.

Alamomin Rai Mai Yawan Zargin Kanta:

● Yawan jin laifi da nadama bayan aikata kuskure.
● Farkawa daga barci na gafala idan aka yi laifi.
●Rashin kwanciyar hankali yayin aikata haram.
● Son gyara hali da tuba.

Hanyoyin Ƙarfafa Rai Mai Yawan Zargin Kanta:

● Cusa wa zuciya son Allah da Manzonsa.
● Taimaka wa rai da kyakkyawan abokai.
● Rayuwa a cikin yanayi mai tsafta da ibada.
● Yawan karanta tarihin mutanen kirki don yin koyi da su.

3. Rai Mai Nutsuwa (النَّفْسُ الْمُطْمَئِنَّةُ): Wannan ita ce zuciyar da ta samu cikakken natsuwa da yarda da hukuncin Allah. Wannan mataki ne mafi girma a cikin halayyar rai. Allah Ya ambaci irin wannan rai a Alƙur’ani inda Ya ce:” Ya kai wannan rai mai nutsuwa. Ka koma zuwa ga Ubangijinka kana mai yarda da sakamako abin yarda. Don haka, ka shiga cikin bayina. Ka kuma shiga Aljannata.” Suratul Fajri aya ta 27-30.

Wannan matakin na rai yana ga mutanen da suka sami cikakkiyar ɗa’a da biyayya ga Allah da Manzonsa (S.A.W). Sun tsarkake zukatansu daga son zuciya, da hassada, da riya, da zalunci. Duk wata fitina da ta zo masu, sun yarda da cewa ƙaddarar Allah ce, don haka ba sa firgita ko damuwa.

Alamomin Rai Mai Nutsuwa:

● Tsananin ƙaunar Allah da Manzonsa fiye da komai.
● Cikakkiyar yarda da ƙaddara, mai daɗi ko akasin haka.
● Jin daɗin ibada da guje wa sharri.
● Kyautatawa ga mutane ba tare da neman lada a duniya ba.
● Jin daɗin rayuwa ko da an sami wahala.

Hanyoyin Samun Rai Mai Nutsuwa:

● Yawaita karatun Al-Qur’ani da nazarin ma’anoninsa.
● Yin addu’a don tsarkake zuciya daga cututtukan rai.
● Yawaita tunani a kan lahira da rayuwar gaskiya.
● Gujewa duniya da halayenta marasa amfani.

Waɗannan nau’ikan rai suna nuni da matakin da mutum yake a cikin bautar Allah. Duk wani mai imani yana ƙoƙarin tashi daga rai mai umurni da mummuna zuwa rai mai yawan zargin kanta, sa’an nan zuwa rai mai nutsuwa. Wannan tafiya tana buƙatar dagewa da ibada, sabo da zuciya na da ƙarfi wajen rinjayar hali.

Ibn Juzai Allah Ya yi masa rahama ya bayyana waɗannan matsayin domin su zama ginshiƙin gyara hali da kyautata rayuwa ta ibada. Duk wanda yake aiki da wannan koyarwar, zai iya cimma babban matsayi na kusanci da Allah, wanda a ƙarshe zai kai shi ga samun dacewa da rahama a duniya da lahira.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Abu Razina Nuhu Ubale Paki Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

Ramaphosa ya yi watsi da barazanar Trump na ware Afirka ta Kudu daga G20

Shugaban Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa  ya yi watsi da barazanar Shugaban Amurka Donald Trump na cire Pretoria daga taron G20 na shekara mai zuwa, yana mai sake tabbatar da matsayin Afirka ta Kudu na memba da aka kafa wannan dandali na kasa da kasa tare da ita.

Trump ya sanar a ranar Laraba da ta gabata cewa ba za a gayyaci Afirka ta Kudu zuwa taron G20 na 2026 a Florida ba, yana mai ambaton zargin da ake yi wa kasar na kin mika shugabancin G20 ga wakilin ofishin jakadancin Amurka a bikin rufe taron da aka yi a kasar  a baya. Duk da haka, Pretoria ta dage cewa shugabancin da ake yi nak aba-karba  an mika shi ga wani jami’in Amurka.

Bayan kauracewa taron shugabannin G20 da aka gudanar a Johannesburg a ranar 22-23 ga Nuwamba a karkashin shugabancin Afirka ta Kudu, Trump ya maimaita ikirarinsa na cewa gwamnatin kasar mai rinjayen bakaken fata tana nuna wariya ga tsirarun fararen fata.

A jawabinsa, Ramaphosa ya kira zarge-zargen Trump na kisan kare dangi da kwace filaye daga fararen fata da cewa ba gaskiya ba ne, zargui ne maras hujja balantana makama, yana mai sake jaddada cewa “Afirka ta Kudu cikakkiyar memba ce da aka kafa G20 tare da ita.”

Rikicin da ke tsakanin Washington da Pretoria ya fara kamari ne a farkon 2025. A ranar 14 ga Maris, Amurka ta kori jakadan Afirka ta Kudu, Ebrahim Rasool, bayan ya zargi Shugaban Amurka Donald Trump da abokansa da haɓaka ajandar duniya ta masu ra’ayin wariyar launin fata

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 165 December 1, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan 164 December 1, 2025 Baqaei: Amurka Ce Babbar Barazana Ga Zaman Lafiya Da Tsaro A Duniya December 1, 2025 Paparoma Leo Na 14 Yana Ziyarar Aiki Na Kwanaki 3  A Kasar Lebanon December 1, 2025 Kamaru: Madugun Adawa Ya Rasu A Gidan Kaso December 1, 2025 Tawagar ECOWAS Ta Bar Guinea – Bissau bayan da shugaban kasar yayi barazanar korarsu Da Karfi December 1, 2025 Yawan Yahudawan Da Suke Ficewa Daga HKI Sun Nininka Har Sau 100% December 1, 2025 Gaza: Fiye da Falasdinawa 350 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila tun bayan tsagaita wuta December 1, 2025 Hamas : Isra’ila na jinkirta aiwatar da mataki na biyu na yarjejeniyar tsagaita wuta December 1, 2025 Nijar : zamu sayar da uranium dinmu ga wanda muka ga dama_ Janar Tiani December 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Abun Da Masu Ruwa Da Tsaki Ke Yi Na Dakile Laifuka A Wurin Matasa
  • Gobara ta kashe mata da miji da ’ya’yansu 3 a Katsina
  • DAGA LARABA: Kalubalen Dake Gaban Janar Christopher Musa A Matsayin Ministan Tsaro
  • An aiwatar da sauye-sauye a wasu muhimman kwamitocin Majalisar Dattawa
  • Shugaba Tinubu Ya Nada Janar Christopher Musa Sabon Ministan Tsaro
  • Tinubu ya naɗa Janar CG Musa sabon Ministan Tsaron Nijeriya
  • NAJERIYA A YAU: Matsalar Kansar Mama Da Hanyoyin Magance Shi
  • Ramaphosa ya yi watsi da barazanar Trump na ware Afirka ta Kudu daga G20
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 165
  • Yawan Yahudawan Da Suke Ficewa Daga HKI Sun Nininka Har Sau 100%