Ƙungiyoyin ƙwadago sun buƙaci Tinubu ya mayar da Fubara kan kujerarsa
Published: 19th, March 2025 GMT
Ƙungiyoyin Ƙwadagon Najeriya, NLC da TUC, sun yi Allah-wadai da matakin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya ɗauka na sanya dokar ta-ɓaci a Jihar Ribas.
Ƙungiyoyin sun soki dakatar da Gwamna Siminilayi Fubara, mataimakiyarsa, da ’yan majalisar dokokin jihar.
Goman Ƙarshe: Dama ta ƙarshe ga mai neman rahamar Allah Matatar Dangote ta dakatar da sayar da fetur a NairaA wata sanarwa da suka fitar ranar Laraba, ƙungiyoyin bitu sun bayyana cewa wannan mataki ya saɓa wa kundin tsarin mulkin Najeriya, musamman sashe na 2 da 305 na dokar 1999 da aka yi wa kwaskwarima.
Sun ce wannan mataki ne da ka iya tauye ikon zartarwa, tare da zama barazana ga dimokuraɗiyya a Najeriya.
A ranar Talata ne, Shugaba Tinubu ya sanar da sanya dokar ta-ɓaci a Jihar Ribas, inda ya bayyana cewa rikicin siyasar jihar yana barazana ga zaman lafiya da tsaron al’umma.
Wannan mataki ya janyo ce-ce-ku-ce a faɗin Najeriya, inda mutane da dama ke ganin hakan bai dace da kundin tsarin mulki ba.
Ƙungiyoyin NLC da TUC sun buƙaci Shugaba Tinubu da ya gaggauta janye wannan mataki, don kada ya jefa Najeriya yanayin saɓa wa doka a nan gaba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Dokar Ta Ɓaci Fubara Ƙungiyoyin Ƙwadago
এছাড়াও পড়ুন:
EU ta bukaci Isra’ila ta dauki mataki don kawo karshen tashin hankali a Yammacin Kogin Jordan
Tarayyar Turai ta yi kira ga Isra’ila da ta dauki mataki nan take don kawo karshen tashin hankali a Yammacin Kogin Jordan.
Mai magana da yawun Hukumar Kula da Harkokin Waje ta Tarayyar Turai, na mayar da martani ne kan karuwar tashin hankalin dake da nasaba da yahudawa ‘yan kama wuri zamna da ke yi wa Falasdinawa a Yammacin Kogin Jordan da aka mamaye.
Jami’in ya yi kira ga hukumomin Isra’ila su dauki matakin gaggawa don hana kara tabarbarewar lamarin da kuma gurfanar da wadanda ke da alhakin wannan tashin hankalin.
Anwar Al-Aouni, mai magana da yawun Tarayyar Turai, da ke magana a taron manema labarai ranar Juma’a, ya nuna karuwar hare-haren da ‘yan kama wuri zamna na Isra’ila ke kai wa a duk fadin Yammacin Kogin Jordan, yana mai cewa wadannan ayyuka “dole ne a dakatar da su nan take.”
Ya kara da cewa: “Fadada matsugunan, tashin hankalin, lalatawa, kwace gidaje, korar Falasdinawa ya saba wa alkawarin Isra’ila kuma dole ne a dakatar da su.”
Kakakin Hukumar Kula da Harkokin Waje ta Tarayyar Turai ya sake nanata cewa Majalisar Turai ta sha nanata bukatar hukumomin Isra’ila su dauki matakai na musamman don hana tashin hankalin da kuma gurfanar da wadanda suka aikata laifin, wanda ke daidai da manufar Tarayyar Turai kan yankunan da aka mamaye.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Amurka Ta Sanar Da Fara Kai Farmakin Soja Mai Sunan ” Mashin Kudu” Akan Yankin Latin November 14, 2025 Ana Samun Kwararar ‘Yan Hijira Daga Mali Zuwa Kasar Cote De Voire November 14, 2025 Unrwa: Fiye Da Gidaje 282,000 “Isra’ila” Ta Rusa A Gaza November 14, 2025 Limamin Juma’a Ya Bukaci Ganin An Kai Karar Donald Trump A Kotunan Duniya November 14, 2025 Iran ce ta farko wajen fitar da dabino a duniya November 14, 2025 Wasu kasashen duniya sun nuna damuwa game da tsarin mulkin bayan yakin Gaza November 14, 2025 Kwamitin Tsaro ya tsawaita wa’adin aikin tawagar MDD a Afrika ta Tsakiya November 14, 2025 Tehran da Ankara sun jaddada muhimmancin zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin November 14, 2025 Iran ta yi tir da G7 kan goyon bayan takunkuman Amurka November 14, 2025 Iran da China na bunkasa alakoki da hadin gwiwa a tsakaninsu November 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci