Ƙungiyoyin ƙwadago sun buƙaci Tinubu ya mayar da Fubara kan kujerarsa
Published: 19th, March 2025 GMT
Ƙungiyoyin Ƙwadagon Najeriya, NLC da TUC, sun yi Allah-wadai da matakin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya ɗauka na sanya dokar ta-ɓaci a Jihar Ribas.
Ƙungiyoyin sun soki dakatar da Gwamna Siminilayi Fubara, mataimakiyarsa, da ’yan majalisar dokokin jihar.
Goman Ƙarshe: Dama ta ƙarshe ga mai neman rahamar Allah Matatar Dangote ta dakatar da sayar da fetur a NairaA wata sanarwa da suka fitar ranar Laraba, ƙungiyoyin bitu sun bayyana cewa wannan mataki ya saɓa wa kundin tsarin mulkin Najeriya, musamman sashe na 2 da 305 na dokar 1999 da aka yi wa kwaskwarima.
Sun ce wannan mataki ne da ka iya tauye ikon zartarwa, tare da zama barazana ga dimokuraɗiyya a Najeriya.
A ranar Talata ne, Shugaba Tinubu ya sanar da sanya dokar ta-ɓaci a Jihar Ribas, inda ya bayyana cewa rikicin siyasar jihar yana barazana ga zaman lafiya da tsaron al’umma.
Wannan mataki ya janyo ce-ce-ku-ce a faɗin Najeriya, inda mutane da dama ke ganin hakan bai dace da kundin tsarin mulki ba.
Ƙungiyoyin NLC da TUC sun buƙaci Shugaba Tinubu da ya gaggauta janye wannan mataki, don kada ya jefa Najeriya yanayin saɓa wa doka a nan gaba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Dokar Ta Ɓaci Fubara Ƙungiyoyin Ƙwadago
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Kano ta dawo da shugaban ƙaramar hukumar Rano kan kujerarsa
Majalisar Dokokin Jihar Kano, ta wanke Shugaban Ƙaramar Hukumar Rano da aka dakatar, Alhaji Naziru Yau, daga dukkanin zarge-zargen da aka masa.
Wannan ya ba shi damar komawa bakin aikinsa da shugabancin Ƙaramar Hukumar Rano.
An kama Faston da ake zargi da yi wa mambobin cocinsa 3 fyade ’Yan bindigar da suka sace masu ibada a cocin Kwara sun nemi a ba su N3bn kafin sakin suAn dakatar da Yauyayin da ake bincike a kansa.
Bayan sanar da dawo da shi kan kujerunsa, dubban magoya bayansa ne suka tarbe shi da murna a kan iyakar Rano da Bunkure.
Daga nan ya wuce zuwa fadar Sarkin Rano, Muhammad Isa Umaru, wanda ya yi masa addu’a kafin ya sake komawa ofis ɗinsa da ke sakateriyar Ƙaramar Hukumar Rano.
Da yake yi wa ma’aikata da magoya bayansa jawabi, Yau, ya gode wa Allah da Ya tsare masa mutuncinsa.
Sannan ya gode wa Majalisar Dokokin jihar da ta wanke shi.
Ya yi godiya ga Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, Gwamna Abba Kabir Yusuf, shugabannin NNPP da sauran masu ruwa da tsaki da suka taimaka wajen dawo da shi kan kujerarsa.
Tun farko an dakatar da shi ne bayan kwamitin karɓar ƙorafe-ƙorafe na majalisar ya miƙa rahoton wucin-gadi.
Rahoton ya zarge shi da aikata ba daidai ba, cin zarafin ofishinsa, karkatar da dukiyar jama’a da kuma aikata rashin gaskiya wajen sarrafa kuɗaɗen gwamnati.
Sauran zarge-zargen sun haɗa da haifar da rikici tsakanin shugabannin siyasa, sayar da taki sama da farashin da gwamnati ta ƙayyade, da kuma rashin bayyana gaskiya wajen karɓar kuɗaɗen haraji na kasuwanni.
Haka kuma an zarge shi da sayar da rumfunan kasuwa ba bisa ƙa’ida ba.
Yanzu da an wanke shi daga dukkanin zarge-zargen, ya koma bakin aikinsa a matsayin Shugaban Ƙaramar Hukumar Rano.