Aminiya:
2025-12-13@00:38:02 GMT

Ƙungiyoyin ƙwadago sun buƙaci Tinubu ya mayar da Fubara kan kujerarsa

Published: 19th, March 2025 GMT

Ƙungiyoyin Ƙwadagon Najeriya, NLC da TUC, sun yi Allah-wadai da matakin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya ɗauka na sanya dokar ta-ɓaci a Jihar Ribas.

Ƙungiyoyin sun soki dakatar da Gwamna Siminilayi Fubara, mataimakiyarsa, da ’yan majalisar dokokin jihar.

Goman Ƙarshe: Dama ta ƙarshe ga mai neman rahamar Allah Matatar Dangote ta dakatar da sayar da fetur a Naira

A wata sanarwa da suka fitar ranar Laraba, ƙungiyoyin bitu sun bayyana cewa wannan mataki ya saɓa wa kundin tsarin mulkin Najeriya, musamman sashe na 2 da 305 na dokar 1999 da aka yi wa kwaskwarima.

Sun ce wannan mataki ne da ka iya tauye ikon zartarwa, tare da zama barazana ga dimokuraɗiyya a Najeriya.

A ranar Talata ne, Shugaba Tinubu ya sanar da sanya dokar ta-ɓaci a Jihar Ribas, inda ya bayyana cewa rikicin siyasar jihar yana barazana ga zaman lafiya da tsaron al’umma.

Wannan mataki ya janyo ce-ce-ku-ce a faɗin Najeriya, inda mutane da dama ke ganin hakan bai dace da kundin tsarin mulki ba.

Ƙungiyoyin NLC da TUC sun buƙaci Shugaba Tinubu da ya gaggauta janye wannan mataki, don kada ya jefa Najeriya yanayin saɓa wa doka a nan gaba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dokar Ta Ɓaci Fubara Ƙungiyoyin Ƙwadago

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴan Bindigar Daji: Jihohin Arewa 7 Sun Kaddamar Da Rundunar Fatattakar Su

Da yake zantawa sa wakilinmu jim kadan bayan Kamala atisayen, mataimakin Babban Kwamandan Hukumar Tsaron Daji na kasa (NFSS) mai kula da Ayyuka, Manjo Muhammad Abubakar Abdullahi mai nurabus, ya ce hukumar na kara samun kaimi wajen amfani da sabbin dabaru da tsare-tsare don kare dazukan kasar.

DCG Mohammed, ya bayyana suna gudanar da irin wannan atisayen musamman duk karshen shekara na Arewa maso yamma bisa umarnin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na samar da ingantaccen tsaro a dazukan Nijeriya.

Ya bayyana cewa NFSS za ta ci gaba da tallafa wa hukumomin tsaro domin lalata maboyar ’yan bindiga da sauran miyagu da ke cikin dazukan kasar.

DCG Mohammed ya bayyana cewa bayan kammala atisayen, za a tura dakaru daban-daban zuwa muhimman dazuka da ake fuskantar barazana domin karfafa hadin gwiwa da sauran hukumomin tsaro wajen tabbatar da cewa Najeriya ta samu zaman lafiya mai dorewa.

Ya ce: “Mun tara wadannan jami’ai ne domin tabbatar da cewa kowannensu ya samu cikakken horo da kuma fahimtar dabarun aiki a daji, kuma samu kayan aiki na zamani da za su ba su damar cin nasara a kowanne fanni.”

Wani jami’in leken asiri na hukumar ya bayyana cewa horon ya kunshi koyon yadda ake shige da ficen dazuka da dabarun gano layukkan sadarwar ’yan ta’adda, da kuma hanyoyin katse su ta hanyar amfani da fasahar zamani.

Shugaban Sashen Leken Asiri na Arewa maso Yamma, Habibu Shehu Yakawada, ya ce jami’an hukumar sun shirya tsaf wajen amfani da gogewa da kwarewarsu a matsayin tsofaffi da masu aikin tsaro domin inganta tsaron daji.

Ya kara da cewa hukumar na da jami’ai a fadin kasar kuma za ta ci gaba da aiki tare da dukkan masu ruwa da tsaki domin samun dawwamammen sakamako.

A nasa jawabin,Wakilin Shugaban karamar Hukumar Nassarawa da ke Jihar Kano, Sani Jibrin SK Tudun Murtala wanda ya wakilci gwamnatin Jihar Kano, ya tabbatar da ci gaba da bayar da goyon baya ta fannoni daban-daban. Ya bayyana tsaro a matsayin alhakin kowa, tare da nanata kudirin Gwamnatin Jihar Kano na kare rayuka da dukiyoyi, yana kuma jinjina wa jami’an tsaro.

Kwamandan NFSS na Jihar Kano, Abdullahi Al’amin, ya ce wannan shi ne karo na 15 da ake gudanar da irin wannan horo, yana mai kara da cewa ba da jimawa ba za su fito fili su nuna shirinsu ga ’yan kasa a matsayin hanyar karfafa amincewar jama’a ga hukumar NFSS.

Ya tabbatar da cewa hukumar na da cikakken niyyar kawar da ’yan bindiga da sauran miyagun mutane daga dazuka da sauran yankunan kasar.

Shima Shugaban Sashen Fasaha da kirkire-kirkire na hukumar ta (NFSS) DCG Y. A. Abdulkareem, ya ce hukumar za ta yi amfani da sabbin hanyoyin tattara bayanan leken asiri da fasahohi sadarwa don inganta ayyuka da karfafa tsaron dazuka a fadin Nijeriya.

Haka zalika, an gudanar da atisayen kai farmaki na karshe, inda jami’an suka nuna kwarewarsu ta yadda za su kewaye daji, su toshe hanyoyin tserewa, sannan su fatattaki duk wata kungiya ta miyagu da ke cikin yankin.

Wani jami’i daga cikin mahalarta atisayen ya ce: “Mun dauki wannan horo da muhimmanci domin kare rayukan ’yan kasa. Za mu shiga dazuka ba tare da tsoro ba har sai mun kawar da barazanar ta’addanci.”

Da yawan jami’an tsaron dajin da suka zanta da wakilinmu sun tabbatar da cewa jama’ar yankunan arewa sun nuna gamsuwa da wannan mataki, suna masu fatan cewa sabon shirin zai kawo karshen matsalar rashin tsaro da ta dade tana addabar su.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Gwamnonin Arewa Sun Yi Rawar Gani A Kafa Gidauniyar Fuskantar Matsalar Tsaro December 12, 2025 Labarai ‘Yan Siyasa Ne Ke Zagon Ƙasa Ga Ci Gaban Nijeriya — Sarki Sanusi II December 11, 2025 Labarai Kotu Ta Yanke Wa Wani Mutum Hukuncin Kisa Bisa Garkuwa Da Kashe Mai Gidansa A Kano December 11, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƴan Bindigar Daji: Jihohin Arewa 7 Sun Kaddamar Da Rundunar Fatattakar Su
  • Kremlin: Putin Ya Bayyana Wa Shugaba Maduro  Na Venezuela Goyon Bayansa
  • NAJERIYA A YAU: Alfanu Da Kalubalen Sabon Jadawalin Karatun Makarantu Da Gwamnati Ta Bijiro Dashi
  • Yadda za ku cike neman aikin dan sandan Najeriya na 2025/2026
  • EFCC ta tsare tsohon ministan ƙwadago, Chris Ngige
  • Najeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar samar da tsaro
  • Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara Ta Taya Oluremi Tinubu Murnar Nadin Sarauta a Ile-Ife
  • Australia ta Fara Aiwhatar da Dokar Hana Yara Amfani da Shafukan Sada Zumunta
  • Iya sojojin da ke tsaron Seyi Tinubu sun isa su samar da tsaro a Benin – Soyinka
  • Iya sojojin da ke tsaron Seyi Tinubu sun isa su samar da tsaro a Jamhuriyar Benin – Soyinka