Aminiya:
2025-12-12@11:56:47 GMT

Ƙungiyoyin ƙwadago sun buƙaci Tinubu ya mayar da Fubara kan kujerarsa

Published: 19th, March 2025 GMT

Ƙungiyoyin Ƙwadagon Najeriya, NLC da TUC, sun yi Allah-wadai da matakin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya ɗauka na sanya dokar ta-ɓaci a Jihar Ribas.

Ƙungiyoyin sun soki dakatar da Gwamna Siminilayi Fubara, mataimakiyarsa, da ’yan majalisar dokokin jihar.

Goman Ƙarshe: Dama ta ƙarshe ga mai neman rahamar Allah Matatar Dangote ta dakatar da sayar da fetur a Naira

A wata sanarwa da suka fitar ranar Laraba, ƙungiyoyin bitu sun bayyana cewa wannan mataki ya saɓa wa kundin tsarin mulkin Najeriya, musamman sashe na 2 da 305 na dokar 1999 da aka yi wa kwaskwarima.

Sun ce wannan mataki ne da ka iya tauye ikon zartarwa, tare da zama barazana ga dimokuraɗiyya a Najeriya.

A ranar Talata ne, Shugaba Tinubu ya sanar da sanya dokar ta-ɓaci a Jihar Ribas, inda ya bayyana cewa rikicin siyasar jihar yana barazana ga zaman lafiya da tsaron al’umma.

Wannan mataki ya janyo ce-ce-ku-ce a faɗin Najeriya, inda mutane da dama ke ganin hakan bai dace da kundin tsarin mulki ba.

Ƙungiyoyin NLC da TUC sun buƙaci Shugaba Tinubu da ya gaggauta janye wannan mataki, don kada ya jefa Najeriya yanayin saɓa wa doka a nan gaba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dokar Ta Ɓaci Fubara Ƙungiyoyin Ƙwadago

এছাড়াও পড়ুন:

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara Ta Taya Oluremi Tinubu Murnar Nadin Sarauta a Ile-Ife

Daga Aminu Dalhatu

Uwargidar Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta taya Uwargidar Shugaban Kasa, Sanata Oluremi Tinubu, murna bisa nadin ta a matsayin Yeye Asiwaju Gbogbo Ile Oodua a Ile-Ife na  Jihar Osun.

Nadin ya kasance wani bangare na bukukuwan cikar shekaru 10 na Mai Martaba Ooni Adeyeye Enitan Ogunwusi Ojaja II akan karagar mulki na Ooni Ife, wanda ya jawo sarakunan gargajiya, manyan jami’an gwamnati da fitattun mutane daga sassan kasar nan.

A wata sanarwa da sakatariyar yada Labarai ta Uwargidar Gwamnan, Rabi Yusuf, ta fitar, ta bayyana karramawar da aka yi wa Sanata Oluremi a matsayin abin yabawa, inda ta ce karramawar ta yi daidai da jajircewarta wajen ci gaban kasa, tallafawa mata, da kuma gudummawarta wajen karfafa iyalai da al’umma ta hanyar aikace-aikacen jin kai da manufofin raya al’umma.

Ta kuma yaba wa Ooni na Ife bisa zabar Sanata Oluremi Tinubu domin wannan girmamawa, tana mai cewa wannan zabe ya nuna irin jagoranci, tasiri da dogon lokacin da ta shafe tana hidima ga kasa.

A cewar Hajiya Huriyya, wannan zabe ya nuna rawar da masarautu ke takawa wajen gane karrama wadanda suka yi wa al’umma  hidima.

Bikin ya nuna al’adun Yarbawa da kuma muhimmancin gudunmawar da masarautu ke bayarwa wajen gina hadin kan kasa.

Manyan shugabannin gargajiya da suka halarci bikin sun hada da Sarkin Musulmi, Olu na Warri, da Soun na Ogbomoso, da sauransu, wadanda suka hadu domin bikin cikar Ooni shekaru 10 a kan karaga da kuma nadin Sanata Oluremi Tinubu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kremlin: Putin Ya Bayyana Wa Shugaba Maduro  Na Venezuela Goyon Bayansa
  • NAJERIYA A YAU: Alfanu Da Kalubalen Sabon Jadawalin Karatun Makarantu Da Gwamnati Ta Bijiro Dashi
  • Yadda za ku cike neman aikin dan sandan Najeriya na 2025/2026
  • EFCC ta tsare tsohon ministan ƙwadago, Chris Ngige
  • Najeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar samar da tsaro
  • Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara Ta Taya Oluremi Tinubu Murnar Nadin Sarauta a Ile-Ife
  • Australia ta Fara Aiwhatar da Dokar Hana Yara Amfani da Shafukan Sada Zumunta
  • Iya sojojin da ke tsaron Seyi Tinubu sun isa su samar da tsaro a Benin – Soyinka
  • Iya sojojin da ke tsaron Seyi Tinubu sun isa su samar da tsaro a Jamhuriyar Benin – Soyinka
  • Juyin Mulki: ECOWAS ta ayyana dokar ta-baci a kasashenta