Kungiyar Wasan Kareti Ta Iran Ta Zama Gwarzo A Asyia
Published: 21st, February 2025 GMT
Kungiyar wasan Kareti ta Iran ta zama ta daya a nahiyar Asiya, yayin da Iraki ta zo ta biyu sai kuma Tajikistan ta uku.
An yi wannan gasar ne ta Asiya a garin Calus dake Arewacin Iran wanda ya sami halartar kasashe da dama. Daga cikin kasashen da su ka shiga gasar wasannnin da akwai Iraki, Hadaddiyar Daular Larabawa, Oman sai kuma Tajikistan.
An bude wannan gasar ne dai daga ranar 19 ga watan nan na Febrairu, kuma za a rufe ta zuwa gobe 22 gare shi.
Da akwai ‘yan wasa 120 na cikin gida da waje da su ka shiga cikin gasar, da ‘yan kallo 700 a cikin dakin wasa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ba dole sai na zama shugaban Nijeriya ba — Peter Obi
Tsohon ɗan takarar shugaban Nijeriya a ƙarƙashin jam’iyyar Labour a Zaɓen 2023, Peter Obi, ya ce ba dole ba ne sai ya zama shugaban ƙasar nan ba.
Sai dai Peter Obi ya ce yana so ya ga ƙasar tana aiki yadda ya kamata a ƙarƙashin jagoranci nagari.
Rikici ya barke a taron Atiku da kungiyoyin Arewa Kwastam ta kama Tiramol ta N150m, ta miƙa wa NAFDAC a KanoGidan Talabijin na Channels ya ruwaito Obi yana bayyana haka ne lokacin bikin murnar cika shekara biyu kan mulki na Gwamnan Abia, Alex Otti.
Ya ce ya kamata a samu shugabanni waɗanda mutane za su yi alfahari da su.
Ya ƙara da cewa haƙƙin shugaba ne ya kare muradun waɗanda yake mulka.
Tsohon gwamnan na Jihar Anambra ya zo na uku a zaɓen shugaban ƙasar da ya gabata, inda ya sha kaye hannun shugaba Bola Tinubu na jam’yyar APC.